< Isaïe 53 >

1 Qui a cru à ce qu’il a entendu de nous? et à qui le bras du Seigneur a-t-il été révélé?
Wa ya gaskata saƙonmu kuma ga wa hannun Ubangiji ya bayyana?
2 Et il montera comme une branche menue devant lui, et comme un rejeton d’une terre altérée; il n’a ni éclat ni beauté; et nous l’avons vu, et il n’avait pas un aspect agréable, et nous l’avons désiré;
Ya yi girma kamar dashe marar ƙarfi, kamar saiwa kuma daga ƙeƙasasshiyar ƙasa. Ba shi da kyan gani ko wani makamin da zai ja hankalinmu, babu wani abin da yake da shi da zai sa mu yi sha’awarsa.
3 Méprisé, et le dernier des hommes, homme de douleur, et connaissant l’infirmité; son visage était comme caché, et méprisé, et nous l’avons compté pour rien.
Mutane suka rena shi suka ƙi shi, mutum ne cike da baƙin ciki, ya kuma saba da wahala. Kamar wanda mutane suna ɓuya fuskokinsu daga gare shi aka rena shi aka yi banza da shi.
4 Il a vraiment lui-même pris nos langueurs sur lui, et il a lui-même porté nos douleurs; et nous l’avons considéré comme un lépreux, frappé de Dieu et humilié.
Tabbatacce ya ɗauki cututtukanmu ya kuma daure da baƙin cikinmu duk da haka muka ɗauka Allah ya hukunta shi ne, ya buge shi ya kuma sa ya sha azaba.
5 Mais lui-même il a été blessé à cause de nos iniquités, il a été brisé à cause de nos crimes; le châtiment, prix de notre paix, est tombé sur lui; et par ses meurtrissures nous avons été guéris.
Amma aka yi masa rauni saboda laifofinmu, aka ƙuje shi saboda kurakuranmu; hukuncin da ya kawo mana salama ya kasance a kansa, kuma ta wurin mikinsa ya sa muka warke.
6 Nous tous, comme des brebis, nous avons erré; chacun s’est détourné vers sa voie; et le Seigneur a mis sur lui l’iniquité de nous tous.
Dukanmu, muna kama da tumakin da suka ɓata, kowannenmu ya kama hanyarsa; Ubangiji kuwa ya sa hukunci ya auko a kansa hukuncin da ya wajaba a kanmu.
7 Il a été offert parce que lui-même l’a voulu, et il n’a pas ouvert sa bouche; comme une brebis, il sera conduit à la tuerie, et comme un agneau devant celui qui le tond, il sera muet, et il n’ouvrira pas sa bouche.
Aka wulaƙanta shi aka kuma yi masa azaba, duk da haka bai buɗe bakinsa ba; aka kai shi kamar ɗan rago zuwa wurin yanka, kuma kamar tunkiya a gaban masu askinta tana shiru, haka bai buɗe bakinsa ba.
8 À la suite des angoisses et d’un jugement il a été enlevé; qui racontera sa génération? car il a été retranché de la terre des vivants; à cause du crime de mon peuple, je l’ai frappé.
Da wulaƙanci da kuma hukunci aka ɗauke shi aka tafi. Wa kuwa zai yi maganar zuriyarsa? Gama an kawar da shi daga ƙasar masu rai; saboda laifin mutanena aka kashe shi.
9 Et il donnera des impies pour sa sépulture, et un riche pour sa mort, parce qu’il n’a pas commis d’iniquité, et que la tromperie n’a pas été dans sa bouche.
Aka yi jana’izarsa tare da mugaye, aka binne shi tare da masu arziki, ko da yake bai taɓa yin wani tashin hankali ba, ko a sami ƙarya a bakinsa.
10 Mais le Seigneur a voulu le briser dans son infirmité; s’il donne, pour le péché, son âme, il verra une race de longue durée, et la volonté du Seigneur, par sa main, sera dirigée.
Duk da haka nufin Ubangiji ne a ƙuje shi yă kuma sa yă sha wahala, kuma ko da yake Ubangiji ya sa ransa ya zama hadaya don zunubi, zai ga zuriyarsa zai kuma kawo masa tsawon rai, nufin Ubangiji kuma zai yi nasara a hannunsa.
11 De ce que son âme a souffert, il verra le fruit, et il sera rassasié; par sa science mon serviteur justifiera lui-même un grand nombre d’hommes, et leurs iniquités, lui-même les portera.
Bayan wahalar ransa, zai ga hasken rai, ya kuma gamsu; ta wurin saninsa bawana mai adalci zai’yantar da mutane masu yawa, zai kuma ɗauki laifofinsu.
12 C’est pour cela que je lui départirai un très grand nombre d’hommes, et il distribuera les dépouilles des forts, parce qu’il a livré à la mort son âme, et qu’il a été compté parmi les scélérats; parce qu’il a porté les péchés d’un grand nombre, et qu’il a prié pour les transgresseurs.
Saboda haka zan ba shi rabo tare da manya, zai kuma raba ganima tare da masu ƙarfi, domin ya ba da ransa har mutuwa, aka kuma lissafta shi tare da masu laifofi. Gama ya ɗauki zunubin mutane masu yawa, ya kuma yi roƙo saboda laifofinsu.

< Isaïe 53 >