< Isaïe 32 >

1 Voici que dans la justice régnera un roi, et que des princes gouverneront selon le droit.
Duba, sarki zai yi mulki cikin adalci masu mulki kuma su yi mulki da adalci.
2 Et chacun sera comme celui qui est à l’abri du vent, qui se cache à la tempête, comme des ruisseaux d’eaux dans la soif, comme l’ombre d’une pierre avancée dans une terre déserte.
Kowane mutum zai zama kamar wurin fakewa daga iska mafaka kuma daga hadari, kamar rafuffukan ruwa a hamada da kuma inuwar babban dutse a ƙeƙasasshiyar ƙasa.
3 Ils ne seront pas obscurcis, les yeux de ceux qui verront; et les oreilles de ceux qui entendront écouteront attentivement.
Sa’an nan idanun waɗanda suka gani ba za su ƙara rufewa ba, kunnuwan waɗanda suka ji kuma za su saurara.
4 Et le cœur des insensés comprendra la science, et la langue des bègues parlera vite et nettement.
Zuciya marasa haƙuri za su sani su kuma fahimta, harshen masu ana’ana kuma zai sāke su yi magana sosai.
5 Il ne portera plus le nom de prince, celui qui manque de sagesse, et le frauduleux ne sera pas appelé grand;
Ba za a ƙara ce da wawa mai girma ba ko kuwa a ɗaukaka mazambaci.
6 Car l’insensé dira des paroles extravagantes, et son cœur commettra l’iniquité, afin de parfaire la simulation, et de parler à Dieu frauduleusement, et de rendre vide l’âme de celui qui a faim, et ôter le boire à celui qui a soif.
Gama wawa maganar wauta yakan yi, zuciyarsa ta cika da mugunta, yana aikata abubuwan rashin sanin Allah yana baza kurakurai game da Ubangiji; yana barin mayunwata da yunwa ya kuma hana masu ƙishirwa ruwan sha.
7 Les armes du frauduleux sont très cruelles; car c’est lui qui a combiné des pensées, pour perdre des hommes, doux par un discours menteur, lorsque le pauvre parlait justice.
Matakan mazambaci mugaye ne, yana ƙulla mugayen shirye-shirye don yă hallaka talakawa da ƙarairayi, ko sa’ad da roƙon mai bukata da gaskiya ne.
8 Mais un prince pensera des choses qui sont dignes d’un prince, et il se tiendra lui-même ferme au-dessus des chefs.
Amma mutumin kirki kan yi shirye-shirye masu kirki, kuma yakan tsaya a kan ayyukan kirki.
9 Femmes opulentes, levez-vous, et entendez ma voix; filles confiantes, prêtez l’oreille à mes paroles.
Ku matan da kuke zaman jin daɗi, ku tashi ku saurare ni; ku’yan matan da kuke tsammani kuna da kāriya, ku ji abin da zan faɗa!
10 Car après des jours et un an, vous serez troublées, vous confiantes; car la vendange est achevée; et la récolte ne viendra plus.
Cikin ɗan lokaci ƙasa da shekara guda ku da kuke tsammani kuna da kāriya za ku yi rawar jiki; girbin’ya’yan inabi zai kāsa, girbin’ya’yan itatuwa kuma ba zai zo ba.
11 Soyez dans la stupeur, femmes opulentes, soyez troublées, filles confiantes; dépouillez-vous, et soyez couvertes de confusion, et ceignez vos reins.
Ku yi rawar jiki, ku mata masu jin daɗi, ku sha wahala, ku’yan matan da kuke tsammani kuna da kāriya! Ku tuɓe rigunanku, ku ɗaura tsummoki a kwankwasonku.
12 Pleurez sur des enfants à la mamelle, sur une contrée délicieuse, sur une vigne fertile.
Ku bugi ƙirjinku don gonaki masu kyau don’ya’yan inabi
13 Sur le sol de mon peuple monteront des épines et des ronces; combien plus sur toutes les maisons joyeuses d’une cité exultante?
da kuma don ƙasar mutanena, da ƙasar da ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiya ne suka yi girma, I, ku yi kuka saboda dukan gidajen da dā ake biki da kuma domin wannan birnin da dā ake murna a ciki.
14 La maison a été abandonnée, la multitude de la ville a été délaissée; des ténèbres palpables se sont formées sur des cavernes pour jamais. La joie des onagres, ce sont les pâturages des troupeaux,
Za a ƙyale kagarar, a gudu a bar birnin da dā ake hayaniya; mafaka da hasumiyar tsaro za su zama kango har abada, jin daɗin jakuna, makiyaya don garkuna,
15 Jusqu’à ce que soit répandu sur nous l’esprit du haut du ciel, et un désert sera converti en Carmel; et le Carmel pour la forêt sera réputé;
sai an zubo Ruhu a kanmu daga sama, hamada kuma ta zama ƙasar mai taƙi, gona mai taƙi kuma ta zama kamar kurmi.
16 Et le droit habitera dans la solitude, et la justice dans le Carmel siégera;
Aikin gaskiya zai zauna a hamada adalci kuma zai zauna a ƙasa mai taƙi.
17 Et la paix sera l’ouvrage de la justice, et l’observation de la justice, le silence et la sécurité à jamais.
Aikin adalci zai zama salama; tasirin adalci zai zama natsuwa da tabbaci har abada.
18 Mon peuple se reposera dans la beauté de la paix, dans des tabernacles de confiance, et dans un repos opulent.
Mutanena za su zauna lafiya a wuraren salama, a gidaje masu kāriya, a wuraren hutun da babu fitina.
19 Mais la grêle descendra sur la forêt, et d’humiliation sera humiliée la cité.
Ko da yake ƙanƙara za tă fāɗo a jeji, a kuma rurrushe birni gaba ɗaya,
20 Bienheureux, vous qui semez sur toutes les eaux, y envoyant le pied du bœuf et de l’âne.
zai zama muku da albarka, ku da kuke shuki iri kusa da kowane rafi, kuna kuma barin lafiyayyiyar makiyaya domin shanu da jakunanku.

< Isaïe 32 >