< Isaïe 29 >

1 Malheur à Ariel, Ariel, cité qu’a prise d’assaut David; une année s’est jointe à une année; des solennités se sont écoulées.
Kaitonki, Ariyel, Ariyel birnin da Dawuda ya zauna! Ƙara shekara ga shekara a kuma bar shagulgulanki su yi ta kewayewa.
2 Et j’environnerai Ariel de tranchées; et elle sera triste, affligée, et elle sera pour moi comme Ariel.
Duk da haka zan yi wa Ariyel kwanto za tă kuma yi kuka da makoki, za tă zama mini kamar bagaden jini.
3 Et je ferai comme un cercle tout autour de toi, et je poserai un rempart contre toi; et je placerai des fortifications pour ton siège.
Zan kafa sansani kewaye da ke duka; zan kewaye ki da hasumiyoyi in tasar miki da ayyukan kwantona na yaƙi.
4 Tu seras humiliée, c’est du sein de la terre que tu parleras, et de la poussière que sera entendue ta parole; et sortant de la terre, ta voix sera comme celle d’un python, et de la poussière ta parole ne rendra qu’un faible son.
Za a ƙasƙantar da ke, za ki ƙi yin magana daga ƙasa; maganarki za tă yi ƙasa-ƙasa daga ƙura. Muryarki za tă zama kamar fatalwa daga ƙasa; daga ƙura maganarki zai fito ƙasa-ƙasa.
5 Et sera comme la poudre menue la multitude de ceux qui t’ont agitée, et comme la cendre brûlante qui se dissipe, la multitude de ceux qui contre toi ont prévalu;
Amma abokan gābanki masu yawa za su zama kamar ƙura mai laushi, sojojinsu masu firgitarwa za su yi ta tashi kamar yayin da iska ta hura. Farat ɗaya, cikin ɗan lokaci,
6 Et ce sera soudain, sur-le-champ. Et par le Seigneur des armées elle sera visitée au milieu d’un tonnerre, et d’un tremblement de terre, et de la grande voix d’un tourbillon, et d’une tempête, et de la flamme d’un feu dévorant.
Ubangiji Maɗaukaki zai zo da tsawa da rawar ƙasa da ƙara mai girma, da hadarin iska da guguwa da harshe na wuta mai ci.
7 Et sera comme le songe d’une vision nocturne la multitude de toutes les nations qui ont combattu contre Ariel, et il en sera ainsi de tous ceux qui lui ont fait la guerre, et l’ont assiégée, et ont prévalu contre elle.
Sa’an nan sojojin dukan al’umman da suka yi yaƙi da Ariyel, da suka fāɗa mata da kagararta suka kuma yi mata kwanto, za su zama kamar yadda yake da mafarki, wahayi da dare,
8 Et comme celui qui a faim songe qu’il mange, mais lorsqu’il est réveillé, son âme se trouve vide; et comme celui qui a soif songe qu’il boit, mais après qu’il est réveillé, il est las et a encore soif, et son âme est vide; ainsi sera la multitude de toutes ces nations qui ont combattu contre la montagne de Sion.
kamar sa’ad da mai yunwa yana mafarki cewa yana cin abinci, amma sai ya farka, yunwan tana nan; kamar sa’ad da mai ƙishirwa yana mafarki cewa yana shan ruwa, amma sai ya farka yana suma, da ƙishinsa. Haka zai zama da sojoji na dukan al’ummai da suka yi yaƙi da Dutsen Sihiyona.
9 Soyez frappés de stupeur et admirez, soyez flottants et vacillants; enivrez-vous, mais non de vin; chancelez, mais non par l’ivresse.
Ku firgita ku kuma yi mamaki, ku makance kanku ku kuma zama a makance; ku bugu, amma ba da ruwan inabi ba, ku yi tangaɗi, amma ba daga barasa ba.
10 Parce que le Seigneur a répandu sur vous un esprit d’assoupissement, il fermera vos yeux; vos prophètes et vos princes qui voient des visions, il mettra sur eux un voile.
Ubangiji ya kawo muku barci mai nauyi, Ya rufe idanunku (annabawa); ya rufe kawunanku (masu duba).
11 Et la vision d’eux tous sera pour vous comme le livre scellé; lorsqu’on le donnera à un homme qui sait lire, on dit: Lis ce livre; et il répondra: Je ne puis, car il est scellé.
Gare ku duk wannan wahayi ba kome ba ne sai dai maganganun da aka rufe a cikin littafi. In kuma kun ba da littafin ga wani wanda zai iya karanta, kuka kuma ce masa, “Karanta wannan, muna roƙonka,” zai amsa ya ce, “Ba zan iya ba; an rufe shi.”
12 Et on donnera le livre à un homme qui ne sait pas lire, et on lui dira: Lis; et il répondra: Je ne sais pas lire.
Ko kuwa in kun ba da littafin ga wani wanda ba zai iya karantawa ba, kuka kuma ce, “Karanta wannan, muna roƙonka,” zai amsa ya ce, “Ban iya karatu ba.”
13 Et a dit le Seigneur: Parce que ce peuple s’approche de moi par sa bouche, et me glorifie par ses lèvres, mais que son cœur est loin de moi, et qu’ils m’ont craint par le commandement et les enseignements des hommes:
Ubangiji ya ce, “Waɗannan mutane sun zo kusa da ni da bakinsu suka kuma girmama ni da leɓunansu, amma zukatansu suna nesa daga gare ni. Sujadar da suke mini cike take da dokokin da mutane suka koyar.
14 C’est pour cela, voici que moi j’exciterai encore l’admiration de ce peuple par un miracle grand et étonnant; car la sagesse périra du milieu des sages, et l’intelligence des prudents sera obscurcie.
Saboda haka zan firgita waɗannan mutane sau ɗaya da abubuwan banmamaki a kan abubuwan banmamaki; hikimar masu hikima za tă lalace, azancin masu azanci zai ɓace.”
15 Malheur à vous qui êtes impénétrables de cœur, afin que vous cachiez au Seigneur un dessein; leurs œuvres sont dans les ténèbres, et ils disent: Qui nous voit, et qui nous connaît?
Kaiton waɗanda suke zuwa manyan zurfafa don su ɓoye shirye-shiryensu daga Ubangiji, waɗanda suke aikinsu cikin duhu su yi tunani, “Wa yake ganinmu? Wa zai sani?”
16 Elle est perverse, cette pensée que vous avez; comme si l’argile se révoltait contre le potier, et lui disait: Tu ne m’as pas fait; et comme si l’œuvre disait à celui qui l’ a façonnée: Tu ne comprends pas.
Kuna birkitar abubuwa, sai ka ce an mayar da mai ginin tukwane ya zama yumɓu! Abin da aka yi zai ce wa wanda ya yi shi, “Ba shi ne ya yi ni ba”? Tukunya za tă iya ce wa mai ginin tukwane, “Ba ka san kome ba”?
17 Encore un peu de temps, et le Liban ne sera-t-il pas bientôt converti en Carmel, et le Carmel ne sera-t-il pas réputé pour la forêt?
Cikin ɗan lokaci, za a mai da Lebanon gona mai taƙi kuma gona mai taƙi za tă zama kamar kurmi?
18 Et en ce jour-là, les sourds entendront les paroles d’un livre, et, affranchis des ténèbres et de l’obscurité, les yeux des aveugles verront.
A wannan rana kurame za su ji maganganun littafi, daga duruduru da duhu kuma idanun makafi za su gani.
19 Et les hommes doux ajouteront à leur joie dans le Seigneur, les hommes pauvres exulteront dans le saint d’Israël;
Masu tawali’u za su sāke yin farin ciki a cikin Ubangiji; mabukata za su yi farin ciki cikin Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
20 Parce qu’il a disparu, celui qui prévalait, et qu’il a été détruit le railleur, et qu’ils ont été retranchés, ceux qui veillaient pour l’iniquité;
Masu zalunci za su ƙare, masu ba’a za su ɓace, kuma dukan waɗanda suke da ido don mugunta za su hallaka,
21 Qui faisaient pécher les hommes par leur parole, qui à la porte tendaient des pièges à celui qui les réfutait, et sans motif s’éloignaient du juste.
waɗanda ta magana kawai sukan mai da mutum mai laifi, waɗanda suke kafa tarko wa mai ba da kāriya a ɗakin shari’a da shaidar ƙarya kuma su hana marar laifi samun shari’ar adalci.
22 À cause de cela, voici ce que dit, à la maison de Jacob, le Seigneur, qui a racheté Abraham: Jacob ne sera plus confondu, et son visage ne rougira plus;
Saboda haka ga abin da Ubangiji wanda ya fanshi Ibrahim, ya ce wa gidan Yaƙub, “Ba za a ƙara kunyata Yaƙub ba; fuskokinsu kuma ba za su ƙara yanƙwanewa ba.
23 Mais lorsqu’il verra ses fils, ouvrages de mes mains, sanctifiant au milieu de lui mon nom, ils sanctifieront ensemble le saint de Jacob, et annonceront le Dieu d’Israël,
Sa’ad da suka ga’ya’yansu a tsakiyarsu, aikin hannuwansu, za su kiyaye sunana da tsarki; za su san tsarkin Mai Tsarkin nan na Yaƙub, za su kuma ji tsoron Allah na Isra’ila.
24 Et ceux qui étaient égarés d’esprit recevront l’intelligence, et les murmurateurs apprendront la loi.
Su da suke marasa azanci a ruhu za su sami fahimtar; waɗanda suke gunaguni za su yarda da koyarwa.”

< Isaïe 29 >