< Isaïe 24 >
1 Voici que le Seigneur dévastera la terre, et il la mettra à nu, et il affligera sa face, et il dispersera ses habitants.
Duba, Ubangiji zai wofinta duniya ya kuma yi kaca-kaca da ita; zai ɓata fuskarta ya watsar da mazaunanta,
2 Et comme sera le peuple, ainsi sera le prêtre; et comme l’esclave, ainsi son maître; comme la servante, ainsi sa maîtresse; comme l’achetant, ainsi celui qui vend; comme le prêteur, ainsi celui qui emprunte; comme celui qui redemande, ainsi celui qui doit.
zai zama abu ɗaya ga firist kamar yadda yake ga mutane, ga maigida kamar yadda yake ga bawa, ga uwargijiya kamar yadda yake ga baiwa, ga mai sayarwa kamar yadda yake ga mai saya, ga mai karɓan rance kamar yadda yake ga mai ba da rance, ga mai karɓan bashi kamar yadda yake ga mai ba da bashi.
3 Par la dévastation sera dévastée la terre, et par le pillage elle sera pillée; car le Seigneur a prononcé cette parole.
Za a wofinta duniya ƙaƙaf a kuma washe ta sarai. Ubangiji ne ya faɗa haka.
4 La terre a pleuré, et elle s’est dissoute, et elle s’est affaiblie; l’univers s’est dissous et la hauteur du peuple de la terre a été abaissée.
Duniya ta bushe ta kuma yanƙwane, duniya tana shan azaba ta kuma raunana, masu daraja na duniya suna shan azaba.
5 Et la terre a été infectée par ses habitants, parce qu’ils ont transgressé les lois, changé le droit, rompu l’alliance éternelle.
Duniya ta ƙazantu ta wurin mutanenta sun ƙi yin biyayya da dokoki, sun keta farillai suka kuma karya madawwamin alkawari.
6 À cause de cela, la malédiction dévorera la terre, et ses habitants pécheront; et à cause de cela ceux qui la cultivent deviendront insensés, et peu d’hommes seront laissés.
Saboda haka la’ana za tă auko wa duniya; dole mutanenta su ɗauki hakkin laifinsu. Saboda haka aka ƙone mazaunan duniya, kuma kaɗan ne kurum suka rage.
7 La vendange a pleuré, la vigne a langui, tous ceux qui se réjouissaient de cœur ont gémi.
Sabon ruwan inabi ya bushe kuringar inabi kuma sun yanƙwane; dukan masu farin ciki suna nishi.
8 La joie des tambours a cessé, le bruit de ceux qui se livraient à l’allégresse s’est calmé, le doux son de la harpe est devenu muet.
Kaɗe-kaɗen garayu sun yi shiru, surutun masu murna ya daina, garayan farin ciki ya yi shiru.
9 On ne boira pas le vin au milieu des chants; amère sera toute liqueur pour ceux qui la boiront.
Babu sauran shan ruwan inabi suna rera waƙa; barasa ya zama da ɗaci ga masu shanta.
10 Elle a été brisée, la cité de vanité; toute maison a été fermée, personne n’y entrant.
Birnin da aka birkice ta zama kango; an kulle ƙofar shiga kowane gida.
11 Il y aura une clameur sur les places publiques, au sujet du vin. Toute allégresse a été abandonnée; la joie de la terre a été transférée.
A tituna suna kukan neman ruwan inabi; dukan farin ciki ya dawo baƙin ciki, an hana dukan kaɗe-kaɗe a duniya.
12 Il n’est resté dans la ville qu’une solitude, et la calamité pèsera sur les portes.
An bar birnin kango, aka yi kaca-kaca da ƙofofinta.
13 Car ce qui restera au milieu de la terre, au milieu des peuples, sera comme quelques olives, qu’on abat de l’olivier, quand elles y sont demeurées, et comme des grappes de raisin, lorsque la vendange est finie.
Haka zai zama a duniya da kuma a cikin al’ummai, kamar sa’ad da akan karkaɗe itacen zaitun, ko kuma kamar sa’ad da ake barin kala bayan an girbe inabi.
14 Ceux-ci élèveront leur voix, et entonneront des louanges; lorsque le Seigneur aura été glorifié, ils feront; entendre des cris de la mer.
Sun daga muryoyinsu, sun yi sowa ta farin ciki; daga yamma sun furta darajar Ubangiji.
15 À cause de cela glorifiez le Seigneur par de bonnes doctrines; dans les îles de la mer, glorifiez le nom du Seigneur Dieu d’Israël.
Saboda haka a gabas sun ɗaukaka Ubangiji, a ɗaukaka sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila, a cikin tsibiran teku.
16 Des extrémités de la terre nous avons entendu des louanges, la gloire du juste. Et j’ai dit: Mon secret est pour moi, mon secret est pour moi, malheur à moi; prévariquant ils ont prévariqué, et de la prévarication des transgresseurs ils ont prévariqué.
Daga iyakokin duniya mun ji waƙoƙi, “Ɗaukaka ga Mai Adalcin nan.” Amma na ce, “Na lalace, na lalace! Kaitona! Munafukai sun ci amana! Da munafunci munafukai sun ci amana!”
17 L’effroi et la fosse et le lacs pour toi, qui es habitant de la terre.
Razana da rami da tarko suna jiranku, Ya mutanen duniya.
18 Et il arrivera que celui qui aura fui à la voix de l’effroi tombera dans la fosse; et que celui qui sera dégagé de la fosse sera retenu par le lacs; parce que les cataractes des cieux se sont ouvertes, et que les fondements de la terre seront ébranlés.
Duk wanda ya yi ƙoƙarin tserewa daga ƙarar razana zai fāɗa cikin rami; wanda kuma ya tsere daga rami za a kama shi a tarko. An buɗe ƙofofin ambaliyar ruwan sama, harsashen ginin duniya suna rawa.
19 Par le déchirement sera déchirée la terre, par le brisement sera brisée la terre, par l’ébranlement sera ébranlée la terre;
An tsage duniya, duniya ta farfashe ta wage, an girgiza duniya ƙwarai.
20 Par le chancellement chancellera la terre comme un homme ivre; et elle sera enlevée comme une tente dressée pour une seule nuit; et son iniquité l’accablera, et elle tombera, et elle ne se relèvera plus.
Duniya tana tangaɗi kamar mashayi, tana lilo kamar rumfa a cikin iska; laifin tayarwarta ya yi nauyi sosai har ta fāɗi ba kuwa za tă ƙara tashi ba.
21 Et il arrivera qu’en ce jour-là le Seigneur visitera la milice du ciel en haut, et les rois de la terre sur la terre.
A wannan rana Ubangiji zai hukunta ikokin da suke cikin sama da kuma sarakunan da suke a duniya.
22 Ils seront assemblés dans la fosse, comme un seul faisceau, et ils y seront renfermés en prison; et, après bien des jours, ils seront visités.
Za a tattara su tare kamar ɗaurarru a kurkuku; za a rufe su a kurkuku a kuma hukunta su bayan kwanaki masu yawa.
23 Et la lune rougira, et le soleil sera confondu, lorsque le Seigneur des armées régnera sur la montagne de Sion et dans Jérusalem, et qu’en présence de ses anciens il sera glorifié.
Sa’an nan wata zai ruɗe, rana ta ji kunya; gama Ubangiji Maɗaukaki zai yi mulki a kan Dutsen Sihiyona da kuma a cikin Urushalima, da kuma a gaban dattawanta, da ɗaukaka.