< Isaïe 22 >
1 Malheur accablant de la vallée de Vision. Qu’as-tu donc, toi aussi, que tu es montée tout entière sur les toits?
Abin da Allah ya faɗa game da Kwarin Wahayi. Mene ne ya dame ku a yanzu, da dukanku kuka hau kan rufin gidaje.
2 Pleine de clameur, ville nombreuse, cité exultante, ceux qui t’ont été tués ne sont pas des tués par le glaive, ni des morts à la guerre.
Ya kai gari cike da hayaniya, Ya ke birnin tashin hankali da alkarya mai murna? Mutanenki ba su mutu ta wurin takobi ba, ba kuwa za su mutu a yaƙi ba.
3 Tous les princes ont fui ensemble, et ont été durement attachés; tous ceux qui ont été trouvés, ont été garrottés pareillement; cependant ils ont fui bien loin.
Dukan shugabanninki sun gudu gaba ɗaya; an kama su ba tare da an yi amfani da baka ba. Dukanku da aka kama an kwashe ku ɗaurarru gaba ɗaya, kun gudu tun abokin gāba yana da nisa.
4 À cause de cela j’ai dit: Retirez-vous de moi, je pleurerai amèrement; ne cherchez pas à me consoler sur la dévastation de la fille de mon peuple.
Saboda haka na ce, “Ƙyale ni kurum; bari in yi kuka mai zafi. Kada ka yi ƙoƙarin ta’azantar da ni a kan hallakar mutanena.”
5 Car c’est un jour de tuerie, de foulement aux pieds et de pleurs, jour venant du Seigneur Dieu des armées dans la vallée de Vision, examinant le mur, et fier sur la montagne.
Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, yana da ranar giggicewa da tattakewa da banrazana a cikin Kwarin Wahayi, ranar ragargazawar katanga da ta yin kuka ga duwatsu.
6 Et Elam a pris un carquois, le chariot du cavalier, le bouclier a laissé la muraille nue.
Elam ya ɗauki kwari da baka, tare da mahayan kekunan yaƙinta da dawakai; Kir ta buɗe garkuwoyi.
7 Et les meilleures vallées seront remplies de quadriges, et les cavaliers mettront le siège devant les portes.
Kwarurukanku mafi kyau sun cika da kekunan yaƙi, an kuma tsai da mahayan dawakai a ƙofofin birni.
8 Et ce qui couvrait Juda sera ôté, et tu verras en ce jour-là l’arsenal de la maison de la forêt.
An rurrushe kāriyar Yahuda, a ranan nan kuwa kun yi la’akari da makamai a cikin Fadan Kurmi;
9 Et vous verrez que les brèches de la cité de David ont été multipliées, et vous avez rassemblé les eaux de la piscine inférieure,
kuka ga cewa Birnin Dawuda tana da wuraren kāriya masu yawa da suka tsattsage; kuka tattara ruwa a Tafkin Ƙasa.
10 Et vous avez fait le dénombrement des maisons de Jérusalem, et vous avez détruit les maisons pour fortifier le mur.
Kuka ƙirga gine-gine a Urushalima kuka kuma rurrushe gidaje don ku ƙarfafa katanga.
11 Et vous avez fait un réservoir entre les deux murs, près de l’eau de la piscine ancienne, et vous n’avez pas levé les yeux vers celui qui l’avait faite, et vous n’avez pas vu même de loin celui qui l’a construite.
Kuka gina matarar ruwa tsakanin katanga biyu saboda ruwan Tsohon Tafki, amma ba ku yi la’akari da Wannan da ya yi su ba, ko ku kula da Wannan da ya shirya shi tuntuni.
12 Et le Seigneur Dieu des armées vous appellera en ce jour-là au pleur, au gémissement, à raser vos cheveux, et à vous ceindre d’un sac;
Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki ya kira ku a wannan rana don ku yi kuka ku yi ihu, don ku aske gashinku ku kuma sa tsummoki.
13 Et voici la joie et l’allégresse; tuer des veaux, égorger des béliers, manger des viandes, et boire du vin. Mangeons et buvons; car demain nous mourrons.
Amma duba, sai ga shi kuna farin ciki kuna kuma murna, kuna yankan shanu kuna kashe tumaki, kuna cin nama kuna kuma shan ruwan inabi! Kuna cewa, “Bari mu ci mu kuma sha, gama gobe za mu mutu!”
14 Et s’est révélée à mes oreilles la voix du Seigneur des armées: Non, elle ne vous sera pas remise, cette iniquité, jusqu’à ce que vous mouriez, dit le Seigneur Dieu des armées.
Ubangiji Maɗaukaki ya bayyana wannan a kunnena cewa, “Har ranar mutuwarka ba za a yi kafarar wannan zunubi ba,” in ji mai girma Ubangiji Maɗaukaki.
15 Voici ce que dit le Seigneur Dieu des armées: Va, entre auprès de celui qui habite dans le tabernacle, auprès de Sobna, le préposé du temple, et tu lui diras:
Ga abin da Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, ya faɗa, “Je, ka faɗa wa wannan mai hidima, Shebna, sarkin fada.
16 Que fais-lu ici, ou à quel titre es-tu ici? que tu t’es taillé ici un sépulcre, que sur un lieu élevé tu l’es taillé dans la pierre un monument, un tabernacle.
Mene ne kake yi a nan kuma wa ya ba ka izini ka haƙa kabari wa kanka a nan, kana fafe kabarinka a bisa kana sassaƙa wurin hutunka a dutse?
17 Voici que le Seigneur te fera transporter comme est transporté un coq, et comme un manteau, ainsi il t’enlèvera.
“Ka yi hankali, Ubangiji yana shirin ya kama ka da ƙarfi ya kuma ɗauke ka, ya kai mai ƙarfi.
18 Te couronnant, il te couronnera de tribulation, il te lancera comme une balle dans une terre large et spacieuse; là tu mourras, et là sera le char de ta gloire, l’ignominie de la maison de ton Seigneur.
Zai dunƙule ka kamar ƙwallo ya jefa ka a cikin ƙasa mai girma. A can za ka mutu a can kuma kekunan yaƙinka masu daraja za su kasance, abin kunya kake ga gidan maigidanka!
19 Je te chasserai de ton rang, et de ton ministère je te déposerai.
Zan tumɓuke ka daga makaminka, za a kuma kore ka daga matsayinka.
20 Et il arrivera en ce jour-là que j’appellerai mon serviteur Eliacim, fils d’Helcias,
“A wannan rana zan kira bawana, Eliyakim ɗan Hilkiya.
21 Et je le revêtirai de ta tunique, je lui attacherai fortement ta ceinture, et ta puissance, je la mettrai en sa main; et il sera comme un père pour les habitants de Jérusalem et pour la maison de Juda.
Zan rufe shi da rigarka in kuma yi masa ɗamara in miƙa masa ikonka. Zai zama mahaifi ga waɗanda suke zama a Urushalima da kuma gidan Yahuda.
22 Et je mettrai la clef de la maison de David sur son épaule, et il ouvrira, et il n’y aura personne qui ferme; et il fermera, et il n’y aura personne qui ouvre.
Zan sa mabuɗin gidan Dawuda a kafaɗarsa; abin da ya buɗe ba mai rufewa, kuma abin da ya rufe ba mai buɗewa.
23 Et je le ficherai comme un pieu dans un lieu sûr, et il sera comme un trône de gloire pour la maison de son père.
Zan kafa shi kamar turke a tsayayyen wuri; zai zama mazaunin daraja domin gidan mahaifinsa.
24 On y suspendra toute la gloire de la maison de son père, les divers genres de vases, tout vase le plus petit, depuis les vases cratères jusqu’à tout instrument de musique.
Dukan ɗaukakar iyalinsa za tă rataya a kansa daga’ya’yansa da zuriyarsa har zuwa dukan ƙananan kayan aikinsa, wato, daga kwanoni har zuwa tuluna.
25 En ce jour-là, dit le Seigneur des armées, sera enlevé le pieu qui avait été fiché dans un lieu sûr; et sera brisé et tombera et périra tout ce qui y avait été suspendu, parce que le Seigneur a parlé.
“A ranan nan, in ji Ubangiji Maɗaukaki, turken da aka kafa a tsayayyen wuri zai sumɓule; za a sare shi ya fāɗi, za a kuma datse nauyin da yake rataya a kansa.” Ni Ubangiji na faɗa.