< Isaïe 21 >

1 Malheur accablant du désert de la mer. Comme des tourbillons viennent de l’Africus, il vient du désert, d’une terre affreuse.
Abin da Allah ya faɗa game da Hamada da take kusa da Teku. Kamar guguwa mai share cikin ƙasar kudu, mai hari ya zo daga hamada, daga ƙasar mai banrazana.
2 Une vision pénible m’a été annoncée; celui qui est incrédule agit infidèlement; et celui qui dépeuple, dévaste. Monte, Elam; Mède, assiège; j’ai fait cesser tous ses gémissements.
An nuna mini mugun wahayi, mai bashewa ya bashe, mai washewa ya washe. Elam, ki yi yaƙi! Mediya, ki yi kwanto! Zan kawo ƙarshen dukan nishe-nishen da ta jawo.
3 À cause de cela mes reins sont remplis de douleur; l’angoisse s’est emparée de moi comme l’angoisse d’une femme en travail; je suis tombé, lorsque j’ai entendu; j’ai été tout troublé, lorsque j’ai vu.
Game da wannan jikina yana ciwo, zafi ya kama ni, kamar na mace mai naƙuda; na razana game da abin da na ji, na yi mamakin abin da na gani.
4 Mon cœur s’est flétri; des ténèbres m’ont frappé de stupeur; Babylone que je chérissais m’est devenue un sujet d’étonnement.
Gabana tana ta fāɗuwa, tsoro ya sa ina rawan jiki; hasken da nake marmari ya zo da razana gare ni.
5 Dresse la table; contemple dans une guérite ceux qui mangent et qui boivent: levez-vous, princes, saisissez le bouclier.
Sun shirya teburori, sun shimfiɗa dardumai, sun ci, sun sha! Tashi, ku hafsoshi, sa mai a garkuwoyi!
6 Car voici ce que m’a dit le Seigneur: Va, et place une sentinelle; et tout ce qu’elle aura vu, qu’elle l’annonce.
Ga abin da mai girma ya ce mini, “Tafi, ka sa mai tsaro ka kuma sa ya ba da rahoton abin da ya gani.
7 Et elle vit un chariot conduit par deux cavaliers, l’un qui montait un âne, et l’autre qui montait un chameau; et elle considéra soigneusement d’un œil très attentif.
Sa’ad da ya ga kekunan yaƙi tare da ƙungiyoyin dawakai, mahaya a kan jakuna, ko mahaya a kan raƙuma, to, fa ya zauna a faɗake, ya kintsa sosai.”
8 Et elle cria comme un lion: Je suis dans la guérite du Seigneur, m’y tenant continuellement pendant le jour, et je fais ma garde, m’y tenant les nuits entières.
Mai tsaron kuma ya yi ihu, “Kowace rana, ranka yă daɗe, nakan tsaya a hasumiyar tsaro; kowane dare nakan tsaya a wurin aikina.
9 Voici que vient cet homme qui monte le chariot aux deux montures des cavaliers; et il répondit et dit: Elle est tombée, elle est tombée, Babylone, et toutes les images de ses dieux, taillées au ciseau, ont été brisées contre terre.
Duba, ga wani mutum tafe a keken yaƙin tare da ƙungiyar dawakai. Ya kuma mayar da amsa, ‘Babilon ta fāɗi, ta fāɗi! Dukan siffofin allolinta kwance a ragargaje a ƙasa!’”
10 Mon battage, et vous, fils de mon aire, ce que j’ai ouï du Seigneur des armées. Dieu d’Israël, je vous l’ai annoncé.
Ya mutanena, an ragargaje ku a masussuka, na faɗa muku abin da na ji daga Ubangiji Maɗaukaki, daga Allah na Isra’ila.
11 Malheur accablant de Duma. Il me crie de Séir: Garde, qu’annonces-tu de la nuit? garde, qu’annonces-tu de la nuit?
Abin da Allah ya faɗa game da Duma, Wani ya kira ni daga Seyir, “Mai tsaro, me ya rage a daren? Mai tsaro, me ya rage a daren?”
12 Le garde dit: Le matin est venu, et la nuit; si vous cherchez, cherchez; convertissez-vous, venez.
Mai tsaro ya amsa, “Safiya ta gabato, haka kuma dare. In za ka yi tambaya, to, yi tambaya; sai ka sāke zuwa, ka tambaya.”
13 Malheur accablant dans l’Arabie. Dans le bois, le soir, vous dormirez, dans les sentiers de Dédanim.
Abin da Allah ya faɗa game da Arabiya. Ku ayarin Dedanawa, ku da kuka sauka a jejin Arabiya,
14 Venant au-devant de celui qui a soif, portez de l’eau, vous qui habitez la terre du midi, avec des pains venez au-devant de celui qui fuit.
ku kawo ruwa don ƙishirwa; ku da kuke zama a Tema, ku kawo abinci don masu gudun hijira.
15 Car à la face des glaives ils ont fui, à la face du glaive suspendu, à la face de l’arc bandé, à la face d’un grave combat:
Sun gudu daga takobi, daga takobin da aka janye, daga bakan da aka tanƙware da kuma daga zafin yaƙi.
16 Parce que voici ce que me dit le Seigneur: Encore une année comptée comme l’année d’un mercenaire, et toute gloire de Cédar sera enlevée.
Ga abin da mai girma ya ce mini, “Cikin shekara ɗaya, kamar yadda bawan da aka bautar da shi bisa ga yarjejjeniya zai lissafta, dukan sojojin Kedar za su zo ga ƙarshe.
17 Et le reste du nombre des forts archers de Cédar seront diminués; car le Seigneur Dieu d’Israël a parlé.
Waɗanda suka yi rai na maharba, jarumawan Kedar, za su zama kaɗan.” Ubangiji, Allah na Isra’ila, ya faɗa.

< Isaïe 21 >