< Isaïe 13 >

1 Malheur accablant de Babylone qu’a vu Isaïe, fils d’Amos.
Abubuwan da Allah ya yi magana a kai game da Babilon da Ishaya ɗan Amoz ya gani.
2 Sur une montagne couverte de nuages, levez un étendard, haussez la voix, levez la main, et que dans ses portes entrent les chefs.
A tā da tuta a kan tudun da yake mai fili, ka tā da murya gare su; ka ɗaga hannu ka ba su alama don su shiga ƙofofi masu alfarma.
3 Moi, j’ai donné mes ordres à mes sanctifiés, et j’ai dans ma colère appelé mes forts qui exultent dans ma gloire.
Na umarci tsarkakana; na umarci jarumawan yaƙina su gamsar da fushina, waɗanda suke farin ciki a nasarata.
4 La voix d’une multitude sur les montagnes est comme celle de peuples nombreux; voix retentissante de rois, de nations réunies; le Seigneur des armées a commandé à la milice de guerre,
Ka saurara, akwai surutu a kan duwatsu, sai ka ce na babban taron jama’a! Ka saurara, akwai hayaniya a cikin mulkoki, sai ka ce al’ummai ne suna ta tattaruwa! Ubangiji Maɗaukaki yana shirya mayaƙa don yaƙi.
5 À ceux qui venaient d’une terre lointaine, de l’extrémité du ciel; le Seigneur et les instruments de sa fureur s’avancent pour perdre entièrement toute la terre.
Suna zuwa daga ƙasashe masu nesa, daga iyakokin duniya, Ubangiji da kuma fushinsa, zai hallaka dukan ƙasar.
6 Poussez des hurlements, parce qu’est proche le jour du Seigneur; il viendra du Seigneur comme une dévastation.
Ku yi ihu, gama ranar Ubangiji ta yi kusa za tă zo kamar hallaka daga Maɗaukaki.
7 À cause de cela toutes les mains seront affaiblies, et tout cœur d’homme se desséchera,
Saboda wannan, hannun kowane mutum zai yi rauni, ƙarfin halin kowane mutum zai kāsa.
8 Et sera brisé. Des tourments et des douleurs les tiendront; ils souffriront comme une femme en travail; chacun regardera son voisin avec stupeur; leurs visages seront comme des faces brûlées par le feu.
Tsoro zai kama su, zafi da azaba za su ci ƙarfinsu; za su yi ta murɗewa kamar mace mai naƙuda. Za su dubi juna a tsorace, fuskokinsu a ɓace.
9 Voici que le jour du Seigneur viendra cruel et plein d’indignation, et de colère et de fureur, pour réduire la terre en solitude, et en exterminer ses pécheurs.
Duba, ranar Ubangiji tana zuwa, muguwar rana, mai hasala da zafin fushi, don ta mai da ƙasar kango ta kuma hallakar da masu zunubi da suke cikinta.
10 Parce que les étoiles du ciel et leur splendeur ne répandront pas leur lumière; le soleil s’est couvert de ténèbres à son lever; et la lune ne luira pas dans sa lumière;
Taurarin sama da ƙungiyoyinsu ba za su ba da haskensu ba. Rana za tă yi duhu wata kuma ba zai ba da haskensa ba.
11 Et je visiterai les crimes de l’univers, ainsi que l’iniquité des impies, et je ferai cesser l’orgueil des infidèles, et l’arrogance des forts, je l’humilierai.
Zan hukunta duniya saboda muguntarta, mugaye saboda zunubansu. Zan kawo ƙarshe ga girman kan masu taƙama in kuma ƙasƙantar da ɗaga kan marasa tausayi.
12 L’homme de haute condition sera plus précieux que l’or, et l’homme de basse condition plus précieux que l’or le plus pur.
Zan sa mutum yă fi zinariya zalla wuyar samuwa, fiye da zinariyar Ofir wuyan gani.
13 De plus, j’ébranlerai le ciel, et la terre sortira de son lieu, et la terre sortira de son lieu, à cause de l’indignation du Seigneur des armées, et à cause du jour de la colère de sa fureur.
Saboda haka zan sa sammai su yi rawar jiki; duniya kuma za tă girgiza daga inda take a fushin Ubangiji Maɗaukaki, a ranar fushinsa mai ƙuna.
14 Et elle sera comme une daine fuyant, et comme une brebis, et il n’y aura personne qui la réunisse; chacun retournera vers son peuple, et les uns après les autres dans leur pays s’enfuiront.
Kamar barewar da ake farautarta kamar tumaki marasa makiyayi, haka nan kowane mutum zai koma ga mutanensa, kowane mutum zai gudu zuwa ƙasarsa.
15 Quiconque sera trouvé sera tué, et quiconque se présentera, tombera sous le glaive.
Duk wanda aka kama za a soke shi yă mutu; dukan waɗanda aka kama za su mutu ta takobi.
16 Leurs enfants seront écrases sous leurs yeux, leurs maisons seront pillées, et leurs femmes seront violées.
Za a fyaɗa’ya’yansu a ƙasa su yi kucu-kucu a idanunsu; za a washe gidajensu, a kuma kwana da matansu.
17 Et voilà que moi je susciterai contre eux les Mèdes, qui ne chercheront pas d’argent et qui ne voudront pas d’or.
Duba, zan zuga mutanen Medes su yi gāba da su, su da ba su kula da azurfa ba kuma ba sa damuwa da zinariya.
18 Mais de leurs flèches ils tueront les petits enfants, et ils n’auront pas pitié des seins qui allaitent, et les fils, leur œil ne les épargnera pas.
Bakkunansu za su kashe samari; ba za su ji tausayin jarirai ba ba za su kuwa nuna jinƙai ga’yan yara ba.
19 Et cette Babylone, glorieuse parmi les royaumes, illustre orgueil des Chaldéens, sera renversée, comme le Seigneur renversa Sodome et Gomorrhe.
Babilon, kayan daraja na mulkoki, abin fariyar Babiloniyawa, Allah zai kaɓantar da ita kamar yadda ya yi da Sodom da Gomorra.
20 Elle ne sera jamais habitée; et elle ne sera pas rétablie dans la suite des générations, et l’Arabe n’y dressera pas ses tentes, et les pasteurs n’y reposeront point.
Ba za ƙara kasance da mazauna kuma ba ko a yi zama a cikinta dukan zamanai; Ba wani mutumin Arab da zai kafa tentinsa a can, ba makiyayin da zai taɓa kiwon garkensa a can.
21 Mais les bêtes sauvages s’y reposeront; et ses maisons seront remplies de dragons; et les autruches y habiteront, les boucs y bondiront.
Amma halittun hamada za su kwanta a can, diloli za su cika gidajenta; a can mujiyoyi za su zauna, a can kuma awakin jeji za su yi ta tsalle.
22 Et les hibous y répondront dans ses édifices, et les sirènes dans ses palais voluptueux.
Kuraye za su yi ta kuka a kagarorinta, diloli kuma a cikin fadodinta masu alfarma. Lokacinta ya yi kusa, kwanakinta kuma ba za su yi tsawo ba.

< Isaïe 13 >