< Osée 14 >
1 Convertis-toi, Israël, au Seigneur ton Dieu, puisque tu es tombé par ton iniquité.
Ku dawo, ya Isra’ila, ga Ubangiji Allahnku. Zunubanku ne sun zama sanadin fāɗuwarku!
2 Prenez avec vous des paroles de pénitence, et convertissez-vous au Seigneur, et dites-lui: Otez-nous toutes nos iniquités, recevez le bien que nous vous offrons, et nous vous rendrons le sacrifice de nos lèvres.
Ku ɗauki magana tare da ku ku komo wurin Ubangiji. Ku ce masa, “Ka gafarta mana dukan zunubanmu ka kuma karɓe mu da alheri, don mu iya yabe ka da leɓunanmu.
3 Assur ne nous sauvera pas, nous ne monterons pas sur des chevaux, et nous ne dirons plus: Vous êtes nos dieux, œuvres de nos mains; parce que vous aurez pitié de l’orphelin qui se repose en vous.
Assuriya ba za su iya cece mu ba; ba za mu hau dawakan yaƙi ba. Ba za mu ƙara ce, ‘Allolinmu’ wa abin da hannuwanmu suka yi ba, gama a gare ka ne maraya yakan sami jinƙai.”
4 Je guérirai leurs meurtrissures, je les aimerai de mon propre mouvement, parce que ma fureur s’est détournée d’eux.
“Zan gyara ɓatancinsu in kuma ƙaunace su a sake, gama fushina ya juya daga gare su.
5 Je serai comme la rosée, Israël germera comme le lis, et sa racine poussera avec force comme les plantes du Liban.
Zan zama kamar raɓa ga Isra’ila zai yi fure kamar lili. Kamar al’ul na Lebanon zai sa saiwarsa zuwa ƙasa;
6 Ses rameaux s’étendront, et sa gloire sera semblable à l’olivier, et son parfum comme celui du Liban.
tohonsa za su yi girma. Darajarsa za tă zama kamar itacen zaitun, ƙanshinsa kamar al’ul na Lebanon.
7 Ils retourneront, s’asseyant sous son ombre; ils vivront de blé, et ils germeront comme la vigne; son souvenir sera comme le vin du Liban.
Mutane za su sāke zauna a inuwarsa. Zai haɓaka kamar ƙwayar hatsi. Zai yi fure kamar kuringa, zai zama sananne kamar ruwan inabi daga Lebanon.
8 Ephraïm dira: Pourquoi aurais-je désormais des idoles? c’est moi qui l’exaucerai, et c’est moi qui le rendrai comme un sapin toujours vert; c’est par moi que du fruit a été trouvé sur toi.
Efraim zai ce, me kuma zai haɗa ni da gumaka? Zan amsa masa in kuma lura da shi. Ni kamar koren itacen fir ne; amincinka yana fitowa daga gare ni ne.”
9 Qui est sage, et il comprendra ces choses? qui est intelligent, et il les saura? parce que les voies du Seigneur sont droites, et les justes y marcheront; mais les prévaricateurs y tomberont.
Wane ne yake da hikima? Zai gane waɗannan abubuwa. Hanyoyin Ubangiji daidai ne; masu adalci sukan yi tafiya a kansu, amma’yan tawaye sukan yi tuntuɓe a kansu.