< Osée 13 >

1 Ephraïm parlant, un frisson a saisi Israël, et il a péché en adorant Baal, et il est mort.
Sa’ad da Efraim ya yi magana, mutane sun yi rawan jiki; an girmama shi a cikin Isra’ila. Amma sai ya zama mai laifi na yin wa Ba’al sujada, ya kuwa mutu.
2 Et maintenant ils ont encore péché; et ils se sont fait avec leur argent une statue jetée en fonte semblable aux idoles, tout cela est un ouvrage d’artisans; à ceux-ci eux-mêmes disent: Immolez des hommes, vous qui adorez des veaux.
Yanzu sai yin zunubi a kai a kai suke; suna yin gumaka wa kansu daga azurfansu, da wayo suna sarrafa siffofi, dukansu aikin masu aikin hannu ne. Ana magana waɗannan mutane cewa, “Suna miƙa hadayar mutum su kuma sumbaci gumakan maruƙa.”
3 C’est pour cela qu’ils seront comme un nuage du matin, et comme la rosée du matin qui se dissipe, comme la poussière emportée de l’aire par un tourbillon, et comme la fumée qui s’échappe d’une cheminée.
Saboda haka za su zama kamar hazon safiya, kamar raɓar safen da yakan kakkaɓe, kamar ƙaiƙayin da ake tankaɗe daga masussuka, kamar hayaƙin da yake fita daga taga.
4 Mais moi, je suis le Seigneur ton Dieu, depuis que je t’ai retiré de la terre d’Egypte; tu ne connaîtras pas de Dieu hors moi, et il n’est de sauveur que moi.
“Amma ni ne Ubangiji Allahnku, wanda ya fitar da ku daga Masar. Ba za ku yarda da wani Allah ba sai ni, ba wani Mai Ceto in ban da ni.
5 Et je t’ai connu dans le désert, dans une terre de solitude.
Na lura da ku a hamada, cikin ƙasar mai ƙunar zafi.
6 À proportion de leurs pâturages ils se sont remplis et rassasiés; et ils ont enflé leur cœur, et ils m’ont oublié.
Sa’ad da na ciyar da su sun ƙoshi; sa’ad da suka ƙoshi, sai suka fara taƙama; sai suka manta da ni.
7 Et moi, je serai pour eux comme une lionne, comme un léopard sur la voie des Assyriens.
Saboda haka zan hau kansu kamar zaki, zan ɓuya a bakin hanya kamar damisa.
8 Je courrai à eux comme une ourse, quand on lui a ravi ses petits, je déchirerai leurs entrailles; et là je les dévorerai comme un lion; la bête des champs les mettra en pièces.
Kamar beyar da aka ƙwace mata’ya’yanta, zan fāɗa musu in ɓarke su. Kamar zaki zan cinye su; kamar naman jeji zan yayyage su.
9 Ta perte vient de toi, Israël; c’est seulement en moi qu’est ton secours.
“An hallaka ku, ya Isra’ila, domin kun tayar mini, kun tayar wa mai taimakonku.
10 Où est ton roi? que surtout maintenant il te sauve dans toutes tes villes; et qu’ils te sauvent, tes juges dont tu as dit: Donnez-moi un roi et des princes.
Ina sarkinku, da zai cece ku? Ina masu mulkinku cikin dukan garuruwanku, waɗanda kuka ce, ‘Ba mu sarki da shugabanni’?
11 Je te donnerai un roi dans ma fureur, et j’ôterai dans mon indignation.
Saboda haka cikin fushina na ba ku sarki, kuma cikin hasalata na ɗauke shi.
12 L’iniquité d’Ephraïm est liée, et son péché caché.
An yi ajiyar laifin Efraim, aka lissafta zunubansa.
13 Les douleurs d’une femme qui enfante viendront sur lui: c’est un fils qui n’est point sage; car maintenant il ne subsistera pas dans le carnage de ses fils.
Naƙuda ta zo masa kamar a mace mai haihuwa, amma shi yaro ne marar hikima; sa’ad da lokaci ya kai, ba ya zuwa inda mahaifa ta buɗe.
14 Je les délivrerai de la main de la mort, je les rachèterai de la mort; je serai ta mort, ô mort; je serai ta morsure, ô enfer; la consolation s’est cachée à mes yeux. (Sheol h7585)
“Zan fanshe su daga ikon kabari; zan cece su daga mutuwa. Ina annobanki, ya mutuwa? Ina hallakarka, ya kabari? “Ba zan ji tausayi ba, (Sheol h7585)
15 Parce qu’il divisera les frères, le Seigneur fera venir un vent brûlant qui montera du désert; et il séchera ses ruisseaux, et tarira sa source, et enlèvera le trésor de tous ses objets précieux.
ko da ma ya ci gaba cikin’yan’uwansa. Iskar gabas daga Ubangiji za tă zo, tana hurawa daga hamada; maɓulɓularsa za tă kafe rijiyarsa kuma ta bushe. Za a kwashi kaya masu daraja na ɗakin ajiyarsa ganima.
16 Périsse Samarie, puisqu’elle a poussé son Dieu à l’exaspération; qu’ils périssent par le glaive, que leurs petits enfants soient écrasés, et que ses femmes enceintes soient coupées en deux.
Dole mutanen Samariya su ɗauki laifinsu, domin sun tayar wa Allahnsu. Za a kashe su da takobi; za a fyaɗa ƙananansu da ƙasa, za a ɓarke matansu masu ciki.”

< Osée 13 >