< Hébreux 1 >
1 Dieu, qui a parlé autrefois à nos pères par les prophètes, bien souvent et en bien des manières, dernièrement,
A zamanin da, Allah ya yi wa kakanin kakanninmu magana ta hanyoyi ma su yawa iri iri, ta bakin annabawa.
2 En ces jours, nous a parlé par son Fils, qu’il a établi héritier en toutes choses, par qui il a fait même les siècles; (aiōn )
Amma a zamanin nan na karshe, ya yi mana magana ta wurin Dansa, wanda ya sa magajin kome, wanda ta wurinsa ya halicci duniya. (aiōn )
3 Et qui étant la splendeur de sa gloire et l’empreinte de sa substance, et soutenant toutes choses par la puissance de sa parole, après avoir opéré la purification des péchés, est assis à la droite de la Majesté, au plus haut des cieux.
Shi ne hasken daukakar Allah, ainihin kamanin zatinsa. Ya na rike da dukkan abubuwa ta ikon kalmarsa. Bayan da ya tsarkake zunubanmu, sai ya zauna a hannun dama na madaukaki a can sama.
4 Ayant été fait d’autant supérieur aux anges, que le nom qu’il a reçu en partage est bien différent du leur.
Ta haka ya ke da fifiko a kan mala'iku, kamar yadda sunansa da ya gada yake da fifiko nesa a kan nasu.
5 Car auquel des anges Dieu a-t-il jamais dit: Vous êtes mon Fils, je vous ai engendré aujourd’hui? Et encore: Moi je serai son Père, et lui sera mon Fils?
Domin kuwa wanene a cikin mala'iku Allah ya taba cewa, “Kai Da na ne, yau na zama Uba a gare ka?'' kuma, “Zan kasance Uba a gareshi, shi kuma, zai kasance Da a gare ni?''
6 Et lorsqu’il introduit de nouveau son premier-né dans le monde, il dit: Et que tous les anges de Dieu l’adorent.
Kuma, da Allah ya kawo magaji a duniya, sai ya ce, “Dukan mala'ikun Allah su yi masa sujada.”
7 À la vérité, l’Ecriture dit touchant les anges: Qui fait de ses anges des vents, et de ses ministres une flamme de feu;
A game da mala'iku kuma sai ya ce, “yakan mai da mala'ikunsa ruhohi, masu hidimarsa kuma harsunan wuta.
8 Mais au Fils: Votre trône, ô Dieu, est dans les siècles des siècles; un sceptre d’équité est le sceptre de votre empire. (aiōn )
A game da Dan, ya ce “kursiyinka, ya Allah, na har abada abadin ne. Sandar sarautarka sanda ce ta tsantsar gaskiya. (aiōn )
9 Vous avez aimé la justice et haï l’iniquité: c’est pourquoi Dieu, votre Dieu, vous a oint d’huile de joie, plus qu’il ne l’a fait à ceux qui ont été oints avec vous.
Ka kaunaci aikin adalci, ka ki aikin sabo. Saboda haka Allah, wato Allahnka, ya shafe ka da man farin ciki fiye da tsararrakinka.”
10 Puis: C’est vous. Seigneur, qui au commencement avez fondé la terre; et les cieux sont l’ouvrage de vos mains.
“Tun farko, Ubangiji, kai ne ka hallici duniya. Sammai kuma aikin hannayenka ne.
11 Ils périront, mais vous, vous demeurerez, et tous vieilliront comme un vêtement;
Za su hallaka, amma kai madawwami ne. Duk za su tsufa kamar tufafi.
12 Et vous les changerez comme un manteau, et ils seront changés; mais vous, vous êtes toujours le même, et vos années ne finiront point.
Za ka nade su kamar mayafi, za su kuma sauya, amma kai kana nan ba sakewa, Har abada shekarunka ba za su kare ba.”
13 Aussi, auquel des anges a-t-il jamais dit: Asseyez-vous à ma droite, jusqu’à ce que je fasse de vos ennemis l’escabeau de vos pieds?
Amma wanene a cikin mala'ikun Allah ya taba cewa, “Zauna a hannun dama na, sai na sa makiyanka a karkashin kafafunka?''
14 Ne sont-ils pas tous des esprits chargés d’un ministère, et envoyés pour l’exercer en faveur de ceux qui recueilleront l’héritage du salut?
Ashe, ba dukkan mala'iku bane ruhohi, wadanda Allah yakan aika, don su yi wa wadanda za su gaji ceto hidima?