< Genèse 7 >
1 Or le Seigneur dit à Noé: Entre, toi et toute ta maison, dans l’arche; car je t’ai trouvé juste devant moi au milieu de cette génération.
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Nuhu. “Shiga jirgin, kai da dukan iyalinka, gama na ga kai mai adalci ne a wannan zamani.
2 De tous les animaux purs prends sept couples, mâles et femelles; mais des animaux impurs, deux couples, mâles et femelles.
Ka ɗauki bakwai na kowace iri tsabtaccen dabba tare da kai, namiji da ta mace, da kuma biyu na kowace dabba marar tsabta, namiji da ta mace,
3 Et des volatiles du ciel pareillement sept couples, mâles et femelles, afin qu’en soit conservée la race sur la face de toute la terre.
da kuma bakwai na kowane iri tsuntsu, namiji da ta mace, domin a bar kowane irinsu da rai a dukan duniya.
4 Car encore sept jours, et après je ferai pleuvoir sur la terre durant quarante jours et quarante nuits, et j’exterminerai toutes les créatures que j’ai faites, de la surface de la terre.
Kwana bakwai daga yanzu zan aiko da ruwa a duniya yini arba’in da dare arba’in, zan kuma kawar da kowace halitta mai rai da na yi daga doron ƙasa.”
5 Noé fit donc tout ce que lui avait ordonné le Seigneur.
Nuhu ya aikata duk abin da Ubangiji ya umarce shi.
6 Or, il avait six cents ans, lorsque les eaux du déluge inondèrent la terre.
Nuhu yana da shekaru 106 ne sa’ad da aka yi ambaliya ruwa a duniya.
7 Ainsi Noé et ses fils, sa femme et les femmes de ses fils entrèrent avec lui dans l’arche, à cause des eaux du déluge.
Nuhu da matarsa da’ya’yansa da matansu, suka shiga jirgi domin su tsira daga ruwa ambaliya.
8 Les animaux aussi, purs et impurs, les oiseaux et tout ce qui se meut sur la terre,
Biyu-biyu daga dabbobi masu tsabta da marasa tsabta, da tsuntsaye da kuma dukan halittu masu rarrafe a ƙasa,
9 Entrèrent deux à deux auprès de Noé dans l’arche, mâle et femelle, comme avait ordonné le Seigneur à Noé.
namiji da ta mace, suka zo wurin Nuhu, suka shiga jirgi, kamar yadda Allah ya umarce Nuhu.
10 Et lorsque les sept jours furent passés, les eaux du déluge inondèrent la terre.
Bayan kwana bakwai kuwa ambaliya ruwa ta sauko a bisa duniya.
11 L’an six cent de la vie de Noé, au second mois, le dix-septième jour du mois, toutes les sources du grand abîme furent rompues, et les cataractes du ciel furent ouvertes;
A ranar sha bakwai ga wata na biyu, na shekara ta ɗari shida na rayuwar Nuhu, a ran nan sai dukan maɓuɓɓugai na manyan zurfafa suka fashe, tagogin sammai suka buɗe.
12 Et la pluie tomba sur la terre durant quarante jours et quarante nuits.
Ruwa yana ta kwararowa bisa duniya, yini arba’in da dare arba’in.
13 Ce jour-là même, Noé, Sem, Cham et Japhet, ses fils, sa femme et les trois femmes de ses fils entrèrent dans l’arche;
A wannan rana Nuhu tare da matarsa da’ya’yansa maza, Shem, Ham da Yafet da matansu uku suka shiga jirgi.
14 Ainsi, eux et tout animal selon son espèce, tous les animaux domestiques selon leur espèce, et tout ce qui se meut sur la terre dans son genre et tout volatile selon son genre, tous les oiseaux et tout ce qui s’élève dans l’air,
Tare da su kuwa, akwai kowane naman jeji bisa ga irinsa, da dukan dabbobin gida bisa ga irinsu, da kowace halitta mai rarrafe a ƙasa bisa ga irinta, da kowane tsuntsun gida da na jeji bisa ga irinsa, da dukan abu mai fiffike.
15 Entrèrent auprès de Noé dans l’arche, deux à deux, de toute chair en laquelle est l’esprit de vie.
Biyu-biyu na dukan halittu masu numfashi suka zo wurin Nuhu, suka shiga jirgi.
16 Et ceux qui y entrèrent, entrèrent mâles et femelles de toute chair, comme Dieu lui avait ordonné: et le Seigneur l’enferma par dehors.
Dabbobi da kowane abu mai rai da suka shiga ciki, namiji ne da ta mace, yadda Allah ya umarci Nuhu. Sa’an nan Ubangiji ya kulle jirgin daga baya.
17 Et il y eut un déluge durant quarante jours sur la terre: et les eaux s’accrurent et élevèrent l’arche de la terre dans les airs.
Kwana arba’in ambaliya ta yi ta saukowa a duniya, sa’ad da ruwa ya yi ta ƙaruwa sai ya yi ta ɗaga jirgin sama, ya kuwa tashi can bisa duniya.
18 Car elles se répandirent impétueusement, et remplirent tout sur la surface de la terre: mais l’arche était portée sur les eaux.
Ruwa ya taso, ya ƙaru ƙwarai a duniya, jirgin kuma ya yi ta yawo a bisa ruwa.
19 Et les eaux crûrent prodigieusement sur la terre, et toutes les hautes montagnes furent couvertes sous le ciel entier.
Ruwa ya ƙaru ƙwarai a duniya, ya kuma rufe dukan duwatsu masu tsawo a ƙarƙashin sammai.
20 L’eau s’éleva de quinze coudées au-dessus des montagnes qu’elle avait couvertes.
Ruwan ya taso ya rufe duwatsu, zurfin ruwa daga duwatsun zuwa inda jirgin yake ya fi ƙafa ashirin.
21 Ainsi périt entièrement toute chair qui se mouvait sur la terre, d’oiseaux, d’animaux domestiques, de bêtes sauvages, et de tout reptile qui rampe sur la terre: tous les hommes,
Kowane abu mai rai da yake tafiya a duniya ya hallaka, tsuntsaye, dabbobin gida, namun jeji, da dukan masu rarrafe waɗanda suke rarrafe a duniya, da kuma dukan mutane.
22 Et tout ce qui a un souffle de vie sur la terre, moururent.
Kome a busasshiyar ƙasa da yake numfashi a hancinsa ya mutu.
23 C’est ainsi que Dieu détruisit toute créature qui était sur la terre, depuis l’homme jusqu’à la bête, tant le reptile que les oiseaux du ciel: tout disparut de la terre; il ne resta que Noé et ceux qui étaient avec lui dans l’arche.
Aka kawar da kowane abu mai rai, mutane da dabbobi da halittu masu rarrafe a ƙasa, da tsuntsayen sama a doron ƙasa, duka aka kawar da su daga duniya. Nuhu kaɗai aka bari da waɗanda suke tare da shi a cikin jirgi.
24 Et les eaux couvrirent la terre durant cent cinquante jours.
Ruwa ya mamaye duniya har kwana ɗari da hamsin.