< Genèse 33 >
1 Mais Jacob, levant les yeux, vit Esaü venant, et avec lui quatre cents hommes; il sépara aussitôt les enfants de Lia, de Rachel et des deux servantes;
Yaƙub ya ɗaga ido ke nan, sai ga Isuwa yana zuwa tare da mutanensa ɗari huɗu; saboda haka sai ya rarraba’ya’yan wa Liyatu, Rahila da kuma matan nan biyu masu hidima.
2 Il mit l’une et l’autre servante et leurs enfants en avant. Lia et ses enfants en second lieu, mais Rachel et Joseph les derniers.
Ya sa matan nan biyu masu hidima da’ya’yansu a gaba, Liyatu da’ya’yanta biye, sa’an nan Rahila da Yusuf a baya.
3 Et lui-même s’avançant, se prosterna, incliné vers la terre par sept fois, jusqu’à ce que son frère approchât.
Shi kansa ya sha gabansu, ya rusuna har ƙasa sau bakwai, kafin ya kai kusa da inda ɗan’uwansa Isuwa yake.
4 C’est pourquoi Esaü, courant au-devant de son frère, l’embrassa; et, serrant étroitement son cou et le baisant, il pleura.
Amma Isuwa ya ruga a guje ya sadu da Yaƙub ya rungume shi; ya faɗa a wuyansa ya sumbace shi. Suka kuma yi kuka.
5 Puis, les yeux levés, il vit les femmes et leurs petits enfants, et dit: Que signifient ceux-ci? est-ce à toi qu’ils appartiennent? Il répondit: Ce sont les petits enfants que Dieu a donnés à votre serviteur.
Sa’an nan Isuwa ya ɗaga ido ya ga mata da’ya’ya. Ya yi tambaya, “Su wane ne waɗannan tare da kai?” Yaƙub ya amsa, “Su ne’ya’yan da Allah cikin alheri ya ba bawanka.”
6 Et s’approchant, les servantes et leurs fils se prosternèrent.
Sai matan nan biyu masu hidima da’ya’yansu suka matso kusa suka durƙusa.
7 Lia aussi s’approcha avec ses enfants; et quand ils se furent pareillement prosternés, Joseph et Rachel se prosternèrent les derniers.
Biye da su, Liyatu da’ya’yanta suka zo suka rusuna. A ƙarshe duka, sai Yusuf da Rahila suka zo, su ma suka rusuna.
8 Alors Esaü dit: Quelles sont ces troupes que j’ai rencontrées? Jacob répondit: C’est pour trouver grâce devant mon seigneur.
Isuwa ya yi tambaya, “Me kake nufi da dukan abubuwan nan da na sadu da su ana korarsu?” Sai Yaƙub ya ce, “Don in sami tagomashi a idanunka ne, ranka yă daɗe.”
9 Mais Esaü reprit: J’ai beaucoup de biens, mon frère, que les tiens restent à toi.
Amma Isuwa ya ce, “Na riga na sami abin da ya ishe ni, ɗan’uwana. Riƙe abin da kake da shi don kanka.”
10 Jacob répondit: Non, je vous prie, qu’il n’en soit pas ainsi; mais si j’ai trouvé grâce à vos yeux, recevez ce petit présent de mes mains; car j’ai vu votre visage, comme si j’eusse vu la face de Dieu: soyez-moi propice.
Sai Yaƙub ya ce, “A’a, ina roƙonka, in na sami tagomashi a idanunka, sai ka karɓi wannan kyautai daga gare ni. Gama ganin fuskarka kamar ganin fuskar Allah ne, yanzu da ka karɓe ni da farin ciki.
11 Et recevez cette bénédiction que je vous ai apportée et que m’a donnée Dieu qui donne toutes choses. Esaü la recevant avec peine, son frère le pressant,
Ina roƙonka ka karɓi kyautar da aka kawo maka, gama Allah ya yi mini alheri kuma ina da kome da nake bukata.” Ganin yadda Yaƙub ya nace, sai Isuwa ya karɓa.
12 Dit: Allons ensemble, et je t’accompagnerai dans ton chemin.
Sa’an nan Isuwa ya ce, “Bari mu tafi, zan yi maka rakiya.”
13 Mais Jacob répondit: Vous savez, mon seigneur, que j’ai avec moi de petits enfants bien faibles encore, des brebis et des vaches pleines; si je les fatigue trop par la marche, tous mes troupeaux mourront en un jour.
Amma Yaƙub ya ce masa, “Ranka yă daɗe, ka san cewa’ya’yan ƙanana ne, dole in lura da tumaki da shanun da suke shayar da jariransu. In aka kore su da gaggawa a rana guda kaɗai, dukan dabbobin za su mutu.
14 Que mon seigneur précède son serviteur, et moi je le suivrai peu à peu, selon que je verrai que mes petits enfants le pourront faire, jusqu’à ce que je parvienne vers mon seigneur à Séir.
Saboda haka bari ranka yă daɗe yă sha gaban bawansa, ni kuma in tafi a hankali bisa ga saurin abin da ake kora a gabana da kuma saurin’ya’yan, sai na iso wurinka ranka yă daɗe, a Seyir.”
15 Esaü repartit: Je te prie, que des gens qui sont avec moi, quelques-uns restent pour t’accompagner. Non, dit Jacob, cela n’est pas nécessaire: la seule chose dont j’ai besoin, c’est de trouver grâce devant vous, mon seigneur.
Sai Isuwa ya ce, “To, bari in bar waɗansu mutanena tare da kai.” Yaƙub ya ce, “Amma me ya sa za ka yi haka? Bari dai in sami tagomashi a idanunka ranka yă daɗe.”
16 Esaü donc retourna ce jour-là à Séir, par le même chemin qu’il était venu.
Saboda haka a wannan rana Isuwa ya kama hanyar komawa zuwa Seyir.
17 Et Jacob vint à Sochoth, où une maison bâtie et des tentes plantées, il appela ce lieu du nom de Socoth, c’est-à-dire, tentes.
Yaƙub kuwa, ya tafi Sukkot, inda ya gina wuri domin kansa, ya kuma yi bukkoki domin dabbobinsa. Shi ya sa aka kira wurin Sukkot.
18 Ensuite il passa à Salem, ville des Sichémites, dans le pays de Chanaan, après qu’il fut revenu de la Mésopotamie de Syrie; et il habita auprès de la ville.
Bayan Yaƙub ya zo daga Faddan Aram, ya iso lafiya a birnin Shekem a Kan’ana, ya kuma kafa sansani a ƙofar birni.
19 Et il acheta pour cent agneaux, des enfants d’Hémor, père de Sichem, une portion du champ où il avait planté ses tentes.
Ya sayi fili daga’ya’yan Hamor maza, mahaifin Shekem inda ya kafa tentinsa, a bakin azurfa ɗari.
20 Puis, un autel érigé en ce lieu, il invoqua le Dieu très fort d’Israël.
A can ya kafa bagade ya kuma kira shi El Elohe Isra’ila.