< Genèse 17 >
1 Or, après qu’Abram eut commencé sa quatre-vingt-dix-neuvième année, le Seigneur lui apparut, et lui dit: Je suis le Dieu tout-puissant: marche devant moi, et sois parfait.
Sa’ad da Abram ya yi shekaru 99, sai Ubangiji ya bayyana a gare shi ya ce, ni “Ni ne Allah Maɗaukaki, ka yi tafiya a gabana ka kuma zama marar abin zargi.
2 J’établirai mon alliance entre moi et toi, et je te multiplierai prodigieusement.
Zan tabbatar da alkawarina tsakanina da kai, zan kuma ƙara zuriyarka ta yi yawa.”
3 Abram tomba incliné sur sa face.
Abram ya rusuna da fuskarsa har ƙasa, Allah kuma ya ce masa,
4 Et Dieu lui dit: C’est moi, et mon alliance sera avec toi, et tu seras père de beaucoup de nations.
“Gare ni kam, wannan shi ne alkawarina da kai, za ka zama mahaifin al’ummai masu yawa.
5 Et on ne t’appellera plus du nom d’Abram, mais tu te nommeras Abraham; car je t’ai établi père de beaucoup de nations.
Ba za a ƙara kiranka Abram ba; sunanka zai zama Ibrahim, gama na mai da kai uban al’ummai masu yawa.
6 Et je te ferai croître prodigieusement, et je t’établirai chef de nations; et des rois sortiront de toi.
Zan sa ka azurta sosai, zan yi al’ummai daga cikinka, sarakuna kuma za su fito daga cikinka,
7 Ainsi j’établirai mon alliance entre moi et toi, et entre ta postérité après toi dans ses générations, par un pacte éternel; afin que je sois ton Dieu et le Dieu de ta postérité après toi.
zan kafa alkawarina kamar madawwamin alkawari tsakanina da kai da kuma zuriyarka bayanka har tsararraki masu zuwa, in zama Allahnka da kuma Allahn zuriyarka a bayanka.
8 Et je te donnerai et à ta postérité la terre de ton pèlerinage, toute la terre de Chanaan, en possession éternelle; et je serai leur Dieu.
Dukan ƙasar Kan’ana inda kake baƙo a yanzu, zan ba da ita a matsayin madawwamiyar mallaka gare ka da kuma zuriyarka a bayanka, zan kuma zama Allahnsu.”
9 Dieu dit encore à Abraham: Tu garderas mon alliance, toi et ta postérité après toi dans ses générations.
Sa’an nan Allah ya ce wa Ibrahim. “Kai fa, sai ka kiyaye alkawarina, kai da zuriyarka bayanka, har tsararraki masu zuwa.
10 Voici mon alliance que vous observerez entre moi et vous, et ta postérité après toi: Tout mâle d’entre vous sera circoncis.
Wannan shi ne alkawarina da kai da kuma zuriyarka a bayanka, alkawarin da za ka kiyaye ke nan. Kowane namiji a cikinku kuwa za a yi masa kaciya.
11 Et vous circoncirez votre chair, afin que ce soit là un signe d’alliance entre moi et vous.
Za ku yi kaciya, za tă kuma zama alamar alkawari tsakanina da kai.
12 L’enfant de huit jours sera circoncis parmi vous; tout mâle en vos générations, tant le serviteur né dans votre maison, que le serviteur acheté, sera circoncis, et même celui qui ne sera pas de votre race.
Daga yanzu duk namijin da aka haifa a cikinku za a yi masa kaciya a rana ta takwas har dukan zamananku, ko haifaffen gida ne, ko sayayye da kuɗi daga kowane baƙo wanda ba na zuriyarku ba.
13 Ainsi mon pacte en votre chair sera une alliance éternelle.
Ko haifaffe a gidanka ko an sayo da kuɗi, dole a yi musu kaciya. Alkawarina cikin jikinku zai kasance madawwamin alkawari.
14 Le mâle dont la chair n’aura pas été circoncise, cette âme sera exterminée du milieu de son peuple, parce qu’il aura rendu vaine mon alliance.
Kowane namijin da ba a yi masa kaciya a jiki ba, za a fid da shi daga cikin mutanensa; domin ya karya alkawarina.”
15 Dieu dit aussi à Abraham: Tu n’appelleras pas ta femme Saraï, mais Sara.
Allah ya kuma ce wa Ibrahim, “Game da Saira matarka kuwa, ba za ka ƙara kiranta Saira ba, sunanta zai zama Saratu.
16 Je la bénirai, et d’elle je te donnerai un fils que je dois bénir aussi; et il sera chef de nations; et des rois de peuples sortiront de lui.
Zan sa mata albarka, ban da haka ma, zan ba ka ɗa ta wurinta, zan sa mata albarka, za tă kuwa zama mahaifiyar al’ummai; sarakunan mutane za su fito daga gare ta.”
17 Abraham tomba sur sa face, et rit, disant en son cœur: Pensez-vous qu’à un centenaire naîtra un fils, et que Sara nonagénaire enfantera?
Ibrahim ya rusuna da fuskarsa har ƙasa, ya yi dariya, ya ce wa kansa, “Za a haifi ɗa wa mutum mai shekaru ɗari? Saratu za tă haifi ɗa tana da shekaru tasa’in?”
18 Et il dit à Dieu: Plaise à Dieu qu’Ismaël vive devant vous!
Ibrahim ya kuma ce wa Allah, “Me zai hana a dai bar Ishmayel kawai yă gāji alkawarin nan da ka yi mini.”
19 Et Dieu répondit à Abraham: Sara ta femme t’enfantera un fils, et tu l’appelleras du nom d’Isaac, et je ferai de mon pacte avec lui et avec sa postérité après lui une alliance éternelle.
Sai Allah ya ce, “Duk da haka dai, matarka Saratu za tă haifi maka ɗa; za ka kuma kira shi Ishaku. A kansa zan tabbatar da madawwamin alkawarina, da kuma ga zuriyarsa da za su zo bayansa.
20 Pour Ismaël, je t’ai aussi exaucé: voilà que je le bénirai, que je le ferai croître et que je le multiplierai grandement; il donnera naissance à douze chefs, et je le ferai père d’une grande nation.
Game da Ishmayel kuwa, na ji ka. Tabbatacce zan albarkace shi, zan sa yă azurta, zai kuma ƙaru ƙwarai. Zai zama mahaifin masu mulki goma sha biyu, zan kuma maishe shi babban al’umma!
21 Mais mon alliance, je l’établirai avec Isaac, que t’enfantera Sara en ce même temps, l’année prochaine.
Amma dai zan kafa alkawarina da Ishaku wanda Saratu za tă haifa maka war haka shekara mai zuwa.”
22 Et lorsque fut fini le discours de Dieu qui lui parlait, Dieu disparut de devant Abraham.
Da ya gama magana da Ibrahim, sai Allah ya tashi daga gare shi.
23 Abraham donc prit Ismaël son fils, tous les serviteurs nés dans sa maison et tous ceux qu’il avait achetés, tous mâles d’entre les hommes de sa maison, et il les circoncit aussitôt ce jour-là même, comme Dieu lui avait ordonné.
A wannan rana, Ibrahim ya ɗauki ɗansa Ishmayel da dukan waɗanda aka haifa cikin gidansa, da waɗanda aka sayo da kuɗinsa, ya kuwa yi wa kowane namiji a cikin gidansa kaciya kamar yadda Allah ya faɗa masa.
24 Or Abraham avait quatre-vingt-dix-neuf ans, quand il circoncit sa chair.
Ibrahim yana da shekara tasa’in da tara sa’ad da aka yi masa kaciya,
25 Et Ismaël son fils avait accompli treize ans au moment de sa circoncision.
Ishmayel ɗansa kuma yana da shekara goma sha uku.
26 Dans le même jour fut circoncis Abraham et Ismaël son fils.
Aka yi wa Ibrahim da ɗansa Ishmayel kaciya a rana ɗaya.
27 Et tous les hommes de sa maison, tant les serviteurs nés chez lui, que ceux qui avaient été achetés, et les étrangers furent pareillement circoncis.
Aka yi wa kowane namiji a gidan Ibrahim kaciya, da waɗanda aka haifa a gidansa, da waɗanda aka sayo da kuɗi daga baƙo.