< Genèse 10 >
1 Voici les générations des fils de Noé, Sem, Cham et Japheth: car il leur naquit des fils après le déluge.
Wannan shi ne labarin Shem, Ham da Yafet,’ya’yan Nuhu maza, waɗanda su ma sun haifi’ya’ya maza bayan ambaliyar.
2 Les fils de Japheth sont: Gomer, Magog, Madaï, Javan, Thubal, Mosoch et Thiras.
’Ya’yan Yafet maza su ne, Gomer, Magog, Madai da Yaban, Tubal, Meshek, da kuma Tiras.
3 Les fils de Gomer: Ascenez, Riphath et Thogorma.
’Ya’yan Gomer maza su ne, Ashkenaz, Rifat, da Togarma.
4 Et les fils de Javan: Elisa, Tharsis, Cetthim et Dodanim.
’Ya’yan maza Yaban su ne, Elisha, Tarshish, Kittim da Rodanim.
5 C’est par eux que furent divisées les îles des nations dans leurs pays, chacun selon sa langue et ses familles dans leurs nations.
(Daga waɗannan mutane ne masu zama a bakin teku suka bazu zuwa cikin ƙasashensu da kuma cikin al’ummansu, kowanne da yarensa.)
6 Les fils de Cham: Chus, Mesraïm, Phuth et Chanaan.
’Ya’yan Ham maza su ne, Kush, Masar, Fut, da Kan’ana.
7 Les fils de Chus: Saba, Hévila, Sabatha, Regma et Sabatacha. Les fils de Regma: Saba et Dadan.
’Ya’yan Kush maza su ne, Seba, Hawila, Sabta, Ra’ama da Sabteka.’Ya’yan Ra’ama maza kuwa su ne, Sheba da Dedan.
8 Or Chus engendra Nemrod; c’est lui qui commença à être puissant sur la terre.
Kush shi ne mahaifin Nimrod wanda ya yi girma ya zama jarumin yaƙi a duniya.
9 C’était un fort chasseur devant le Seigneur. De là est venu le proverbe: Comme Nemrod, fort chasseur devant le Seigneur.
Shi babban maharbi ne a gaban Ubangiji. Shi ya sa akan ce, kamar Nimrod babban maharbi a gaban Ubangiji.
10 Le commencement de son royaume fut Babylone, Arach, Achad et Chalanné, dans la terre de Sennaar.
Cibiyoyin mulkinsa na farko su ne Babilon, Erek, Akkad, da Kalne a cikin Shinar.
11 De ce pays sortit Assur qui bâtit Ninive, les rues de cette ville et Chalé,
Daga wannan ƙasa, sai ya tafi Assuriya, inda ya gina Ninebe, Rehobot Ir, Kala
12 Et aussi Résen entre Ninive et Chalé: c’est la grande ville.
da Resen, wadda take tsakanin Ninebe da Kala; wanda yake babban birni.
13 Quant à Mesraïm, il engendra Ludim, Anamim, Laabim, Nephthuim,
Mizrayim shi ne mahaifin Ludiyawa, Anamawa, Lehabiyawa, Naftuhiyawa,
14 Phétrusim et Chasluim, d’où sont sortis les Philistins et les Caphtorins.
Fetrusiyawa, da Kasluhiyawa (inda Filistiyawa suka fito) da kuma Kaftorawa.
15 Chanaan engendra Sidon, son premier-né, l’Héthéen,
Kan’ana shi ne mahaifin, Sidon ɗan farinsa, da na Hittiyawa,
16 Le Jébuséen, l’Amorrhéen, le Gergéséen,
Yebusiyawa, Amoriyawa, Girgashiyawa,
17 L’Hévéen, l’Aracéen, le Sinéen,
Hiwiyawa, Arkiyawa, Siniyawa,
18 L’Aradien, le Samaréen et l’Amathéen: et après cela se sont dispersés les peuples des Chananéens.
Arbadiyawa, Zemarawa, da Hamawa. Daga baya zuriyar Kan’aniyawa suka yaɗu
19 Et les limites des Chananéens furent depuis Sidon en venant à Gérara, jusqu’à Gaza; et en venant à Sodome, Gomorrhe, Adama et Séboïm, jusqu’à Lésa.
har iyakar Kan’ana ta kai Sidon ta wajen Gerar har zuwa Gaza, sa’an nan ta milla zuwa Sodom, Gomorra, Adma da Zeboyim, har zuwa Lasha.
20 Ce sont là les enfants de Cham selon leur parenté, leurs langues, leurs générations, leurs pays et leurs nations.
Waɗannan su ne’ya’yan Ham maza bisa ga zuriyarsu da yarurrukansu, cikin ƙasashensu da kuma al’ummominsu.
21 De Sem aussi, père de tous les enfants d’Héber et frère aîné de Japheth, naquirent des fils.
Aka kuma haifa wa Shem, wan Yafet,’ya’ya maza. Shem shi ne kakan’ya’yan Eber duka.
22 Les fils de Sem sont: Elam, Assur, Arphaxad, Lud et Aram.
’Ya’yan Shem maza su ne, Elam, Asshur, Arfakshad, Lud da Aram.
23 Les fils d’Aram: Us, Hul, Géther et Mes.
’Ya’yan Aram maza su ne, Uz, Hul, Geter da Mash.
24 Or Arphaxad engendra Salé, dont est né Héber.
Arfakshad ne mahaifin Shela. Shela kuma shi ne mahaifin Eber.
25 À Héber naquirent deux fils: le nom de l’un fut Phaleg, parce qu’en ses jours la terre fut divisée; et le nom de son frère, Jectan.
Aka haifa wa Eber’ya’ya maza biyu. Aka ba wa ɗaya suna Feleg, gama a zamaninsa ne aka raba duniya; aka kuma sa wa ɗan’uwansa suna Yoktan.
26 Lequel Jectan engendra Elmodad, Saleph, Asarmoth, Jaré,
Yoktan shi ne mahaifin, Almodad, Shelef, Hazarmawet, Yera,
29 Ophir, Hévila et Jobab: tous ceux-là sont les fils de Jectan.
Ofir, Hawila da Yobab. Dukan waɗannan’ya’yan Yoktan maza ne.
30 Et leur habitation s’étendit de Messa jusqu’à Séphar, montagne qui est à l’orient.
Yankin da suka zauna ya miƙe daga Mesha zuwa wajen Sefar a gabashin ƙasar tudu.
31 Voilà les fils de Sem, selon leur parenté, leurs langues, leurs pays et leurs nations.
Waɗannan su ne’ya’yan Shem maza bisa ga zuriyarsu da yarurrukansu, cikin ƙasashensu da kuma al’ummominsu.
32 Et voilà les familles de Noé, selon leurs peuples et leurs nations. C’est par elles qu’ont été divisées toutes les nations sur la terre après le déluge.
Waɗannan su ne zuriyar’ya’yan Nuhu maza bisa ga jerin zuriyarsu cikin al’ummominsu. Daga waɗannan ne al’ummomi suka bazu ko’ina a duniya bayan ambaliya.