< Esdras 5 >

1 Or Aggée, le prophète, et Zacharie, fils d’Addo, prophétisèrent, prophétisant aux Juifs qui étaient en Judée et à Jérusalem, au nom du Dieu d’Israël.
Sai annabi Haggai, da annabi Zakariya zuriyar Iddo, suka yi wa Yahudawa a Yahuda da Urushalima annabci a cikin sunan Allah na Isra’ila wanda yake da mulki a kansu.
2 Alors se levèrent Zorobabel, fils de Salathiel, et Josué, fils de Josédec, et ils commencèrent à bâtir le temple de Dieu à Jérusalem, et avec eux les prophètes de Dieu qui les aidaient.
Sa’an nan Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel da Yeshuwa ɗan Yozadak suka yi shiri suka kama aikin sāke gina gidan Allah a Urushalima. Annabawan Allah kuwa suna tare da su, suna taimakonsu.
3 Or, en ce temps-là, vinrent vers eux Thathanaï, qui était chef au-delà du fleuve, et Stharbuzanaï, et leurs conseillers, et c’est ainsi qu’ils leur dirent: Qui vous a donné le conseil de bâtir cette maison et de restaurer ses murs?
A wannan lokaci, Tattenai gwamnan Kewayen Kogin Yuferites, da Shetar-Bozenai da abokansu suka je wurinsu suka tambaye su cewa, “Wa ya ba ku iko ku sāke gina wannan haikali har ku gyara katangar?”
4 À quoi nous répondîmes en leur disant quels étaient les noms des hommes auteurs de cette construction.
Suka kuma tambaye su “Ina sunayen waɗanda suke wannan gini?”
5 Or l’œil de leur Dieu fut sur les anciens des Juifs, et ils ne purent les empêcher. Et il leur plut que l’affaire fût renvoyée à Darius, et qu’alors ils répondraient à cette accusation.
Amma Allah yana tsaron dattawan Yahudawa, saboda haka ba a hana su aikin ba har sai rahoto ya kai wurin Dariyus aka kuma sami amsarsa a rubuce tukuna.
6 Copie de la lettre que Thathanaï, chef de la contrée au-delà du fleuve, et Stharbuzanaï et ses conseillers Arphasachéens, qui étaient au-delà du fleuve, envoyèrent à Darius, le roi.
Ga wasiƙar da Tattenai, gwamnan Kewayen Kogin Yuferites, da Shetar-Bozenai da abokansu masu riƙe da muƙamai a Kewayen Kogin Yuferites suka aika wa Sarki Dariyus.
7 La parole qu’ils lui avaient envoyée était écrite ainsi: À Darius, le roi, toute paix.
Ga rahoton da suka aika masa. Zuwa ga Sarki Dariyus. Gaisuwa da fatan alheri.
8 Qu’il soit connu du roi que nous sommes allés dans la province de Judée, dans la maison du grand Dieu que l’on bâtit de pierres non polies et dont on pose les bois sur les murailles. Or cet ouvrage s’élève avec diligence et s’accroît entre leurs mains.
Ya kamata sarki yă sani cewa mun je yankin Yahuda, zuwa gidan Allah mai girma. Muka ga mutanen suna ginin haikalin da manyan duwatsu, suna sa katakai a bangon. Ana aikin da ƙwazo, aikin kuma yana cin gaba sosai, suna kuma lura da shi.
9 Nous avons donc interrogé les vieillards, et c’est ainsi que nous leur avons dit: Qui vous a donné le pouvoir de bâtir cette maison et de rétablir ces murs?
Mun tambayi dattawan muka ce musu, “Wa ya ba ku iko ku sāke gina wannan haikali, ku kuma sāke gyara katangarsa?”
10 Mais nous leur avons aussi demandé leurs noms, afin de vous les indiquer, et nous avons écrit les noms des hommes qui sont les princes parmi eux.
Muka kuma tambaye su sunayensu don mu rubuta mu sanar da kai waɗanda suke shugabanninsu.
11 Or ils nous ont répondu ces paroles, disant: Nous sommes serviteurs du Dieu du ciel et de la terre; nous bâtissons le temple qui était construit beaucoup d’années avant celles-ci, et que le grand roi d’Israël avait bâti et construit.
Wannan ita ce amsar da suka ba mu. “Mu bayin Allah na sama da ƙasa ne, muna sāke gina haikalin da aka gina tun shekaru da yawa da suka wuce, da wani babban sarkin Isra’ila ya gina ya kuma gama.
12 Mais après que nos pères eurent provoqué au courroux le Dieu au ciel, il les livra entre les mains de Nabuchodonosor, roi de Babylone, Chaldéen; et il détruisit même cette maison, et transporta son peuple à Babylone.
Amma domin kakanninmu sun ɓata wa Allah na sama rai, sai ya bari suka fāɗa cikin hannun Nebukadnezzar mutumin Kaldiya, sarkin Babilon, wanda ya rushe wannan haikali, ya kuma kwashe mutane zuwa Babilon.
13 Or, à la première année de Cyrus, roi de Babylone, le roi Cyrus publia un édit afin que cette maison de Dieu fût bâtie.
“Duk da haka, a shekara ta farko ta mulkin Sairus sarkin Babilon, Sarki Sairus ya ba da umarni cewa a sāke gina wannan gidan Allah.
14 Et même les vases d’or et d’argent du temple de Dieu, que Nabuchodonosor avait enlevés du temple qui était à Jérusalem, et qu’il avait apportés dans le temple de Babylone, le roi Cyrus les tira du temple de Babylone, et ils furent donnés à un nommé Sassabasar, qu’il établit même prince.
Ya kuma kwashe kwanonin zinariya da azurfa na gidan Allah daga haikalin Babilon waɗanda Nebukadnezzar ya kwasa daga haikali a Urushalima. Sa’an nan sarki Sairus ya ba wa wani mutum mai suna Sheshbazzar umarni wanda ya sa ya zama gwamna,
15 Et il lui dit: Prends ces vases, et va, et mets-les dans le temple qui est à Jérusalem, et que la maison de Dieu soit bâtie en son lieu.
ya ce masa, ‘Ka kwashe kayan nan ka je ka zuba su a cikin haikalin Allah a Urushalima. Ka kuma sāke gina gidan Allah a wurin da yake a dā.’
16 Alors donc ce Sassabasar vint, et posa les fondements du temple de Dieu à Jérusalem, et, depuis ce temps-là jusqu’à présent, on le bâtit, et il n’est pas encore achevé.
“Saboda haka Sheshbazzar ya so ya aza harsashin gina gidan Allah a Urushalima. Tun daga wancan lokaci har zuwa yau ana kan gina shi amma ba a gama ba.”
17 Maintenant donc, s’il semble bon au roi, qu’il recherche dans la bibliothèque du roi, qui est à Babylone, s’il a été ordonné par le roi Cyrus que la maison de Dieu serait rebâtie à Jérusalem, et qu’il nous envoie la volonté du roi sur cela.
Yanzu in sarki yana so, bari a duba cikin littattafan tarihi na sarakuna na Babilon a gani ko lalle sarki Sairus ya ba da umarni a sāke gina gidan Allah a Urushalima. Bari sarki yă aiko mana da abin da ya gani game da wannan abu.

< Esdras 5 >