< Ézéchiel 7 >
1 Et la parole du Seigneur me fut adressée, disant:
Maganar Ubangiji ta zo gare ni cewa,
2 Et toi, fils d’un homme, voici ce que dit le Seigneur Dieu à la terre d’Israël: La fin vient, elle vient la fin sur les quatre côtés de la terre.
“Ɗan mutum, ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yake cewa wa ƙasar Isra’ila, “‘Ƙarshe ya zo! Ƙarshe ya zo a kan kusurwoyi huɗu na ƙasar.
3 Maintenant la fin est sur toi, et j’enverrai ma fureur contre toi; et je te jugerai selon tes voies, et je poserai contre toi toutes tes abominations.
Ƙarshe yanzu yana a kanki. Zan fashe fushina a kanki. Zan shari’anta ki bisa ga halinki in sāka miki kuma saboda dukan ayyukan banƙyamar da kika yi.
4 Et mon œil ne t’épargnera pas, et je n’aurai pas de pitié; mais tes voies, je les poserai sur toi, et tes abominations seront au milieu de toi; et vous saurez que je suis le Seigneur.
Ba zan dube ki da tausayi; ko in ƙyale ki ba. Tabbatacce zan sāka miki saboda halinki da kuma ayyukanki masu banƙyama a cikinki. Sa’an nan za ki san cewa ni ne Ubangiji.’
5 Voici ce que dit le Seigneur Dieu: Une affliction unique, une affliction, voici qu’elle vient.
“Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Masifa! Masifar da ba a taɓa gani ba tana zuwa.
6 La fin vient, elle vient la fin, elle s’est éveillée contre toi; voici qu’elle vient.
Ƙarshe ya zo! Ƙarshe ya zo! Ya farka a kanki. Ga shi, ya zo!
7 La ruine vient sur toi, qui habites la terre; il vient, le temps; il est près, le jour de la tuerie, et non de la gloire des montagnes.
Ƙaddara ta auko miki, ya ke wadda ke zama cikin ƙasar. Lokaci ya yi, rana ta gabato; akwai fargaba, ba farin ciki ba, a kan duwatsu.
8 C’est maintenant de près que je répandrai ma colère sur toi, et que j’assouvirai ma fureur sur toi; et que je te jugerai selon tes voies; et que je t’imposerai tous tes crimes;
Ina gab da fasa hasalata a kanki in kuma aukar da fushina a kanki; zan shari’anta ke bisa ga halinki in kuma sāka miki saboda dukan ayyukanki masu banƙyama.
9 Et mon œil n’épargnera pas, et je n’aurai pas de pitié; mais tes voies, je te les imposerai; et tes abominations seront au milieu de toi; et vous saurez que moi je suis le Seigneur qui frappe.
Ba zan dube ki da tausayi ko in ƙyale ke ba; zan sāka miki bisa ga halinki da kuma ayyukan masu banƙyama a cikinki. Sa’an nan za ki san cewa ni ne Ubangiji wanda yake bugunki.
10 Voici le jour, voici qu’il vient: la ruine est sortie, la verge a fleuri, l’orgueil a germé;
“‘Ga shi ranar ta zo! Ta iso! Ƙaddararki ta keto, sandar ta yi toho, girman kai ya yi fure!
11 L’iniquité s’est élevée sur la verge de l’impiété; il ne restera rien d’eux, ni du peuple, ni de leur bruit; et il n’y aura pas de repos pour eux.
Rikici ya yi girma ya zama sandar da za a hukunta mugunta; babu wani daga cikin mutanen da za a bari, babu wani dukiyarsu da za a bari, babu wani abin amfani.
12 Il est venu le temps, il s’est approché le jour; que celui qui achète ne se réjouisse point; et que celui qui vend ne s’afflige pas, parce que la colère est sur tout son peuple.
Lokaci ya yi! Ranar ta gabato! Kada mai saya ya yi farin ciki ko kuwa mai sayarwa ya yi baƙin ciki, gama hasala tana a kan dukan jama’a.
13 Parce que celui qui vend ne reviendra pas à ce qu’il a vendu, lors même qu’ils seraient encore au nombre des vivants; parce que la vision qui regarde tout le peuple ne reviendra pas sans être accomplie; et l’homme par l’iniquité ne sera pas affermi.
Mai sayarwa ba zai mayar da ƙasar da ya sayar tuntuni ba muddin dukansu suna da rai, gama ba za a sauya wahayin da ya shafi dukan jama’a ba. Saboda zunubansu, babu ɗayansu da zai adana ransa.
14 Sonnez de la trompette; que tous se préparent, et il n’est personne qui aille au combat; car ma colère est sur tout son peuple.
“‘Ko da yake suna busa ƙaho suna kuma shirya kome, ba wanda zai tafi yaƙi, gama hasalata tana a kan dukan jama’a.
15 Le glaive au dehors; et la peste et la famine au dedans; celui qui est dans la campagne mourra par l’épée; et ceux qui sont dans la cité seront dévorés par la peste et par la famine.
A waje takobi ne, a ciki annoba ne da yunwa; waɗanda suke fili za su mutu ta wurin takobi, waɗanda kuma suke cikin birni yunwa da annoba za su cinye su.
16 Et seront sauvés ceux qui d’entre eux auront fui: mais ils seront sur les montagnes comme les colombes des vallées, tout tremblants, chacun dans son iniquité.
Duk waɗanda suka tsira suka tsere za su kasance a cikin duwatsu, suna kuka kamar kurciyoyin kwaruruka, kowanne saboda zunubansa.
17 Toutes les mains seront affaiblies, et l’eau coulera de tous les genoux.
Kowane hannu zai raunana, kowace gwiwa kuma za tă zama marar ƙarfi kamar ruwa.
18 Et ils se revêtiront de cilices, et la frayeur les couvrira; sur toute face sera la confusion, et sur toutes les têtes la calvitie.
Za su sa tufafin makoki su kuma rufu da fargaba. Fuskokinsu kuma za su rufu da kunya a kuma aske kawunansu.
19 Leur argent sera jeté dehors, et leur or sera comme du fumier. Leur argent et leur or ne pourront les délivrer au jour de la fureur du Seigneur; ils ne rassasieront pas leur âme, et leurs ventres ne seront pas remplis, parce que c’est devenu une pierre d’achoppement dans leur iniquité.
“‘Za su zubar da azurfarsu a tituna, zinariyarsu kuma za tă zama ƙazantacciyar aba. Azurfarsu da zinariyarsu ba za su iya cetonsu a ranar hasalar Ubangiji ba. Ba za su ƙosar da yunwansu ko su cika cikinsu da shi ba, gama su ne sanadin tuntuɓensu cikin zunubi.
20 Ils ont fait servir l’ornement de leurs colliers à leur orgueil; et ils en ont fait les images de leurs abominations et de leurs simulacres; à eau se de cela, je l’ai rendu pour eux un objet immonde;
Sun yi fariya kyan kayan adonsu suka kuma yi amfani da su don su yi gumakansu masu banƙyama, da ƙazantattun abubuwa.
21 Et je le livrerai aux mains des étrangers pour être pillé, et aux impies de la terre pour être leur proie; et ils le souilleront,
Zan ba da su duka kamar ganima ga baƙi da kuma kamar abin da aka washe ga mugayen duniya, za su kuma ƙazantar da su.
22 Et je détournerai ma face d’eux; et ils violeront mon secret; et des émissaires y entreront et le souilleront.
Zan juye fuskata daga gare su, za su kuwa ƙazantar da wurina mai daraja;’yan fashi za su shiga su kuma ƙazantar da shi.
23 Fais la conclusion, parce que la terre est pleine de jugements de sang et que la cité est remplie d’iniquité.
“‘Ka shirya sarƙoƙi, domin ƙasar ta cika da alhakin jini, birnin kuma ya cika da rikici.
24 Et j’amènerai les plus méchants d’entre les nations, et ils posséderont leurs maisons; et je ferai cesser l’orgueil des puissants, et ces méchants posséderont leurs sanctuaires.
Zan kawo al’ummai mafi mugunta su mallaki gidajenku; zan kawo ƙarshen fariyar masu ƙarfi, Wurare Masu Tsarkinsu za su ƙazantu.
25 L’angoisse survenant, ils chercheront la paix, et il n’y en aura pas.
Sa’ad da wahala ta zo, za su nemi salama, amma ba za su same ta ba.
26 Trouble sur trouble viendra, et bruit sur bruit; ils chercheront quelque vision auprès d’un prophète, et la loi manquera au prêtre, et le conseil aux anciens.
Masifa a kan masifa za su zo, jita-jita kuma a kan jita-jita. Za su yi ƙoƙarin samun wahayi daga annabi; koyarwar doka ta wurin firist za tă ɓace, kamar yadda shawarar dattawa za tă ɓace.
27 Le roi sera en deuil, le prince sera couvert de tristesse, et les mains du peuple de la terre trembleront. Selon leur voie je leur rendrai, et selon leurs jugements je les jugerai; et ils sauront que je suis le Seigneur.
Sarki zai yi makoki, yerima zai fid da zuciya, hannuwan mutanen ƙasar kuma za su yi rawa. Zan sāka musu bisa ga ayyukansu, zan kuma hukunta su bisa ga ma’auninsu. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.’”