< Ézéchiel 22 >
1 Et la parole du Seigneur me fut adressée, disant:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 Et toi, fils d’un homme, est-ce que tu ne juges pas la cité du sang?
“Ɗan mutum, za ka shari’anta ta? Za ka shari’anta wannan birni mai kisankai? To, sai ka kalubalance ta da dukan ayyukanta na banƙyama
3 Et tu lui montreras toutes ses abominations, et tu diras: Voici ce que dit le Seigneur Dieu: Une cité répandant le sang au milieu d’elle, afin que vienne son temps, et qui a fait des idoles contre elle-même, afin de se souiller,
ka kuma ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce ya birnin da take kawo wa kansa hallaka ta wurin kisankai a cikinta kina kuma ƙazantar da kanki ta wurin yin gumaka,
4 Par le sang qui par toi a été répandu, tu t’es rendue coupable, et par les idoles que tu as faites tu t’es souillée, et tu as avancé tes jours et amené le temps de tes années; à cause de cela, je t’ai rendue l’opprobre des nations et la dérision de tous les pays.
kin zama mai laifi saboda jinin da kika zubar kika kuma zama ƙazantacciya ta wurin gumakan da kika yi. Kin kawo kwanakinki ga ƙarshe, kuma ƙarshen shekarunki sun zo. Saboda haka zan mai da ke abar ba’a ga al’ummai da abin dariya ga dukan ƙasashe.
5 Ceux qui sont près et ceux qui sont loin de toi triompheront de toi, souillée, noble, grande par ta ruine.
Waɗanda suke kusa da waɗanda suke nesa za su yi miki ba’a, ya ke birni marar kunya, cike da rigima.
6 Voilà que les princes d’Israël ont usé chacun de leur bras chez toi, pour répandre le sang.
“‘Duba yadda kowane yerima Isra’ila waɗanda suke cikinki yake yin amfani da ikonsa yana kisankai.
7 Ils ont accablé d’outrages père et mère au milieu de toi; ils ont calomnié l’étranger au milieu de toi, et ils ont contristé la veuve et l’orphelin chez toi.
A cikinki sun rena mahaifi da mahaifiya; a cikinki sun zalunci baƙo suka wulaƙanta maraya da gwauruwa.
8 Tu as méprisé mes sanctuaires, et souillé mes sabbats.
Kin rena abubuwana masu tsarki kika kuma ƙazantar da Asabbataina.
9 Des hommes détracteurs ont été chez toi pour répandre le sang; et sur les montagnes ils ont mangé chez toi, ils ont opéré le crime au milieu de toi.
A cikinki akwai mutane waɗanda suka nace su yi kisankai; a cikinki akwai waɗanda suke ci a dutsen tsafi suna yin ayyukan lalata.
10 Ils ont découvert la nudité du père chez toi, ils ont humilié l’impureté de la femme qui était dans ses mois chez toi;
A cikinki akwai waɗanda suke kwana da matan mahaifansu; a cikinki akwai waɗanda suke kwana da mata a lokacin da suke al’adarsu, sa’ad da suke da rashin tsarki.
11 Et chacun d’eux a commis une abomination sur la femme de son prochain, et le beau-père a souillé sa belle-fille par un crime horrible; le frère a fait violence à sa propre sœur, à la fille de son père chez toi.
A cikinki mutum guda yakan yi laifi abin ƙyama da matar maƙwabcinsa, wani cikin rashin kunya ya ƙazantar da matar ɗansa, wani kuma ya kwana da’yar’uwansa,’yar mahaifinsa.
12 Ils ont reçu des présents chez toi, pour répandre le sang; tu as reçu un intérêt et un profit de surplus; et par avarice, tu calomniais tes’proches, et tu m’as oublié, dit le Seigneur Dieu.
A cikinki mutane suna karɓan cin hanci don su yi kisankai; kina ba da rance da ruwa da ƙari, kina kuma cin riba a kan maƙwabcinki ta wurin ƙwace. Kina kuma manta da ni, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
13 Voici que moi j’ai frappé des mains contre ton avarice, et contre le sang qui a été répandu au milieu de toi.
“‘Tabbatacce zan tafa hannuwana a kan ƙazamar riba da kika ci da jinin da kin zubar a cikinki.
14 Est-ce que ton cœur se soutiendra, ou tes mains prévaudront-elles, aux jours malheureux que je ferai pour toi? c’est moi le Seigneur qui ai parlé, et j’exécuterai.
Ƙarfin halinki zai jure ko kuwa hannuwanki za su yi ƙarfi a ranar da na gamu da ke? Ni Ubangiji na faɗa, zan kuma aikata.
15 Et Je te disperserai parmi les nations, et je te jetterai au vent dans divers pays, et je ferai disparaître ton impureté du milieu de toi.
Zan watsar da ke cikin al’ummai in warwatsa ke cikin ƙasashe; zan kuma kawo ƙarshen rashin tsarkinki.
16 Et je te posséderai en présence des nations, et tu sauras que je suis le Seigneur.
Sa’ad da ki ƙazantu a idanun al’umma, za ki san cewa ni ne Ubangiji.’”
17 Et la parole du Seigneur me fut adressée, disant:
Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
18 Fils d’un homme, la maison d’Israël s’est changée pour moi en scorie; tous sont de l’airain, et de l’étain, et du fer et du plomb, au milieu d’un fourneau; ils sont devenus une scorie d’argent.
“Ɗan mutum, gidan Isra’ila ta zama ƙwan maƙera a gare ni; dukansu tagulla ne, kuza, ƙarfe da darma da suka rage a tanderu. Su ƙwan maƙerar azurfa ne kawai.
19 À cause de cela, voici ce que dit le Seigneur Dieu: Parce que vous avez été tous changés en scorie, à cause de cela, voilà que moi, je vous assemblerai au milieu de Jérusalem,
Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ‘Domin ku duka kun zama ƙwan maƙera, zan tattara ku a Urushalima.
20 Comme on met ensemble l’argent, et l’airain, et le plomb, et le fer, au milieu d’un fourneau; comme j’y allumerai un feu pour les fondre, ainsi je vous rassemblerai dans ma fureur et dans ma colère; et je me reposerai, et je vous fondrai;
Kamar yadda mutane sukan tattara azurfa, tagulla, ƙarfe, darma da kuza a cikin tanderu don su narkar da su da wuta, haka zan tattara ku cikin fushina da kuma hasalata in sa ku cikin birnin in narkar da ku.
21 Et je vous rassemblerai, et je vous embraserai par le feu de ma fureur, et vous serez fondus au milieu de Jérusalem.
Zan tattara ku zan kuma hura muku wutar hasalata, za ku kuma narke a cikinta.
22 Comme l’argent fond au milieu d’un fourneau, ainsi vous serez au milieu d’elle; et vous saurez que je suis le Seigneur, lorsque j’aurai répandu mon indignation sur vous.
Kamar yadda azurfa kan narke a tanderu, haka za ku narke a cikinta, kuma za ku san cewa Ni Ubangiji na zubo muku da zafin fushina.’”
23 Et la parole du Seigneur me fut adressée, disant:
Har yanzu maganar Ubangiji ta zo gare ni cewa,
24 Fils d’un homme, dis-lui: Tu es une terre impure, et qui n’a point été arrosée de pluie au jour de la fureur.
“Ɗan mutum, ka faɗa wa ƙasar, ‘Ke ƙasa ce marar ruwan sama ko yayyafi a ranar hasala.’
25 La conjuration de ses prophètes est au milieu d’elle; comme un lion rugissant et ravissant une proie, ils ont dévoré les âmes, ils ont reçu des richesses et des récompenses, ils ont multiplié ses veuves au milieu d’elle.
Akwai haɗin bakin sarakunanki a cikinki kamar rurin zaki mai yayyage ganimarsa; suna cin mutane, suna kwashe dukiya da abubuwa masu daraja suna mai da yawanci gwauraye a cikinki.
26 Ses prêtres ont méprisé ma loi, ils ont souillé mes sanctuaires; entre le saint et le profane ils n’ont pas mis de différence; et entre l’impur et le pur ils n’ont pas distingué; et de mes sabbats, ils ont détourné leurs yeux, et j’étais souillé au milieu d’eux.
Firistocinki suna karya dokokina, sun ƙazantar da tsarkakan abubuwana; ba sa bambanta tsakanin tsarki da marar tsarki; suna koyarwa cewa babu bambanci tsakanin marar tsarki da mai tsarki; suna kuma rufe idanunsu ga kiyaye Asabbataina, da haka suke saɓon sunana.
27 Ses princes sont au milieu d’elle comme des loups ravissant une proie pour répandre le sang, perdre les âmes, et par avarice courir après le gain.
Shugabanninki a cikinki suna kama da kyarketai masu yayyage ganimarsu; suna kisa suna kuma kashe mutane don samun ƙazamar riba.
28 Mais ses prophètes les enduisaient sans mélange, voyant des choses vaines, et leur prédisant le mensonge, disant: Voici ce que dit le Seigneur Dieu, quoique le Seigneur n’ait point parlé.
Annabawanki sun yi wa waɗannan ayyuka shafe da farar ƙasa ta wurin wahayin ƙarya da duban ƙarya. Suna cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa’ alhali kuwa Ubangiji bai faɗa ba.
29 Les peuples du pays ajoutaient calomnie à calomnie, et commettaient des rapines avec violence; ils affligeaient l’indigent et le pauvre, et ils opprimaient l’étranger par la calomnie sans jugement.
Mutanen ƙasar na yin ƙwace suna yin fashi; suna cin zalin matalauta da mabukata suna wulaƙanta baƙo suna hana musu adalci.
30 Et j’ai cherche parmi eux un homme, qui mît une haie entre moi et eux, et qui se tînt opposé à moi pour cette terre, afin que je ne la détruisisse point; et je n’en ai pas trouvé.
“Na nemi mutum guda a cikinsu wanda zai gina katanga ya tsaya a gabana a tsakani a madadin ƙasar don kada in hallaka ta, amma ban sami ko ɗaya ba.
31 C’est pourquoi j’ai répandu mon indignation sur eux; dans le feu de ma colère je les ai consumés, j’ai ramené leur voie sur leur tête, dit le Seigneur Dieu.
Saboda haka zan zuba hasalata a kansu in cinye su da wutar fushina, ina ɗora alhakin ayyukansu a bisa kawunansu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”