< Ézéchiel 16 >
1 Et la parole du Seigneur me fut adressée, disant:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 Fils d’un homme, fais connaître à Jérusalem ses abominations,
“Ɗan mutum, ka sa Urushalima ta san ayyukanta masu banƙyama
3 Et tu diras: Voici ce que dit le Seigneur Dieu à Jérusalem: Ta racine et ta génération sont de la terre de Chanaan; ton père était Amorrhéen, et ta mère Céthéenne.
ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa wa Urushalima, Asalinki da haihuwarki daga ƙasar Kan’ana ne; mahaifinki mutumin Amoriyawa ne, mahaifiyarki kuma mutuniyar Hitti ce.
4 Et quant tu es née, au jour de ta venue au monde, on n’a pas coupé le conduit par où tu étais nourrie dans le sein de ta mère, tu n’as pas été lavée de l’eau salutaire, ni lavée avec le sel, ni enveloppée de langes.
A ranar da aka haife ki ba a yanke cibiyarki ba, ba a kuma yi miki wanka don a tsabtacce ki ba, ba a kuma goge ki da gishiri ba ko a naɗe ki cikin tsummoki.
5 Aucun œil, ayant pitié de toi n’a cherché à te faire une seule de ces choses; mais tu as été jetée sur la face de la terre, en mépris de ton âme, le jour que tu es née.
Ba wanda ya dube ki da tausayi ko ya nuna miki isashen jinƙai don yă yi miki ɗaya daga cikin waɗannan abubuwa. A maimako, sai aka jefar da ke a fili, gama a ranar da aka haife ki an ji ƙyamarki.
6 Or, passant près de toi, je te vis foulée aux pieds dans ton sang, et je dis, lorsque tu étais ainsi dans ton sang: Vis; je te dis encore: Malgré ton sang, vis.
“‘Sa’an nan na wuce na ga kina birgima cikin jininki, yayinda kike kwance can cikin jininki sai na ce miki, “Ki rayu!”
7 Je t’ai multipliée comme la verdure des champs, et tu as crû, et tu as grandi, et tu es entrée en âge de prendre les parures de ton sexe; tes seins se sont formés, avec les autres signes de la puberté; mais tu étais nue et pleine de confusion.
Na sa kin yi girma kamar tsiro a fili. Kin yi girma kika kuma yi tsayi kika zama mafiya kyau na kayan ado. Nononki suka fito, gashinki kuwa suka yi girma, duk da haka tsirara kike tik.
8 Et j’ai passé près de toi, et je t’ai vue, et voici que ton temps était le temps d’être aimée; et j’ai étendu mon vêtement sur toi, et j’ai couvert ton ignominie: et je t’ai juré fidélité, et j’ai fait une alliance avec toi, dit le Seigneur Dieu, et tu es devenue à moi.
“‘Daga baya na wuce, da na dube ki sai na ga cewa kin yi girma sosai har kin kai a ƙaunace ki, na yafa gefen tufafina a kanki na kuma rufe tsiraincinki. Na rantse miki, na ƙulla alkawari da ke, kin kuwa zama tawa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
9 Et je t’ai lavée dans l’eau, et je t’ai purifiée de tes souillures, et je t’ai ointe d’huile.
“‘Na yi miki wanka na wanke miki jini daga gare ki na kuma shafa miki mai.
10 Et je t’ai revêtue de diverses couleurs, et je t’ai donné une chaussure d’hyacinthe; et je t’ai ceinte de byssus, et je t’ai parée des vêtements les plus fins.
Na rufe ki da rigar da aka yi wa ado na kuma sa miki takalman fata. Na sa miki riga ta lilin mai kyau na kuma rufe ki da riguna masu tsada.
11 Et je t’ai parée d’une belle parure, j’ai mis des bracelets à tes mains et un collier autour de ton cou.
Na yi miki ado da kayan ado masu daraja, na sa miki mundaye a hannuwanki da abin wuya a wuyanki,
12 Et j’ai mis un anneau au-dessus de ta bouche, et des boucles à tes oreilles, et une couronne d’éclat sur ta tête.
na kuma sa miki zobe a hancinki, abin kunne a kunnuwanki da rawani mai kyau a kanki.
13 Et tu as été ornée d’or et d’argent, et vêtue de byssus et d’un tissu de plusieurs fils et de couleurs variées; tu t’es nourrie de farine la plus pure, de miel et d’huile, tu es devenue extrêmement belle; et tu es parvenue à la royauté.
Haka kuwa aka caɓa miki zinariya da azurfa; tufafinki kuwa na lilin mai kyau da riguna masu tsada waɗanda aka yi musu ado. Abincinki na gari mai laushi ne, zuma da man zaitun. Kika zama kyakkyawa har kika kuma zama sarauniya.
14 Et ton nom est allé jusque chez les nations, à cause de ta beauté; parce que tu étais parfaire par l’éclat que j’avais mis en toi, dit le Seigneur Dieu.
Sunanki ya yaɗu a cikin al’ummai saboda kyanki, domin darajar da na ba ki ya sa kyanki ya zama cikakke, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
15 Mais, ayant confiance en ta beauté, tu as forniqué à la faveur de ton nom, tu t’es abandonnée à tout passant, afin d’être à lui.
“‘Amma kika dogara ga kyanki kika kuma yi amfani da sunan da kika yi don ki zama karuwa. Kin yi ta jibga alherai a kan kowa da ya wuce, sai kyanki ya zama naki.
16 Et prenant de tes vêtements, tu en as fait l’ornement de tes hauts lieux, après les avoir cousus d’un côté et de l’autre, et là tu y as forniqué comme il ne s’est pas fait, et comme il ne se fera pas.
Kin ɗauki waɗansu tufafinki don ki yi wa kanki masujadai masu ado, inda kike karuwancinki. Irin waɗannan abubuwa bai kamata su faru ba, bai kuma kamata su taɓa faruwa ba.
17 Et tu as pris les vases de ta gloire, faits de mon or et de mon argent, que je t’ai donnés; et tu en as fait des images d’hommes, et tu as forniqué avec elles.
Kika kuma ɗauki kayan ado masu kyau da na ba ki, kayan adon da aka yi da zinariya da azurfa, kika yi wa kanki gumakan maza kika kuma yi ta yin karuwanci da su.
18 Et tu as pris tes vêtements de couleurs variées, et tu les en a couvertes; et mon huile et mes parfums, tu les a apposés devant elles.
Kika ɗauki rigunanki masu ado don ki sa a kansu, kika kuma miƙa maina da turarena a gabansu.
19 Et le pain que je t’ai donné, la plus pure farine, et l’huile et le miel dont je t’ai nourrie, tu les as mis en leur présence, en odeur de suavité, et cela a été fait, dit le Seigneur Dieu.
Haka ma abincin da na tanada miki, lallausan gari, man zaitun, da zuman da na ba ki ki ci, kin miƙa su kamar turare mai ƙanshi a gabansu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
20 Et tu as pris tes fils et tes filles que tu m’as engendrés, et tu les leur as immolés pour être dévorés. Est-ce qu’elle est sans importance, ta fornication?
“‘Kika kuma kwashe’ya’yanki maza da mata waɗanda kin haifa mini kika miƙa su kamar abinci ga gumakanki. Karuwancinki bai isa ba ne?
21 Tu as immolé mes enfants et tu les leur as livrés, en les consacrant.
Kin kashe’ya’yana kika kuma miƙa su ga gumaka.
22 Et, après toutes tes abominations et tes fornications, tu ne t’es pas souvenue des jours de ta jeunesse, quand tu étais nue, pleine de confusion, foulée aux pieds dans ton sang.
Cikin dukan ayyukan banƙyamarki da karuwancinki ba ki tuna da kwanakin ƙuruciyarki ba, sa’ad da kike tsirara tik, kina birgima cikin jininki.
23 Et il est arrivé qu’après toute la malice (malheur, malheur à toi, dit le Seigneur Dieu),
“‘Kaito! Kaitonki, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Bugu da ƙari a kan dukan waɗansu muguntarki,
24 Tu as bâti pour toi un lieu de prostitution, et tu as préparé pour toi une maison de débauche sur toutes les places publiques.
kin gina wa kanki ɗakunan sama da gidajen tsafi a kowane dandali.
25 À toute entrée de la voie tu as dressé le signe de ta prostitution; et tu as rendu ta beauté abominable, et tu t’es livrée à tout passant, et tu as multiplié tes fornications.
A kowane titi kin gina ɗakin tsafi kika kuma wulaƙanta kyanki, kina miƙa jikinki da ƙarin fasikanci ga duk mai wucewa.
26 Et tu as forniqué avec les fils de l’Egypte, tes voisins d’une haute stature; et tu as multiplié ta fornication pour m’irriter.
Kin yi karuwanci da Masarawa, maƙwabtanki masu kwaɗayi, kika tsokane ni har na yi fushi da ƙarin fasikancinki.
27 Et voilà que moi j’étendrai ma main sur toi, et j’écarterai ta justification, et je te livrerai aux âmes des filles des Philistins, qui te haïssent, qui rougissent de ta voie criminelle.
Saboda haka na miƙa hannuna gāba da ke na kuma rage iyakarki; na ba da ke ga abokan gābanki masu haɗama,’yan matan Filistiyawa, waɗanda suka sha mamaki saboda halinki na lalata.
28 Et tu as forniqué avec les fils des Assyriens, parce que tu n’étais pas encore assouvie; et après que tu as ainsi forniqué, tu n’as pas été encore rassasiée.
Kin kuma yi karuwanci da Assuriyawa, domin ba kya ƙoshi; kai ko bayan wannan, ba ki ƙoshi ba.
29 Et tu as multiplié ta fornication dans la terre de Chanaan avec les Chaldéens; et tu n’as pas encore été rassasiée.
Sai kika ƙara fasikancinki da ya haɗa da ƙasar cinikin Babilon, amma duk da haka ba ki ƙoshi ba.
30 Avec quoi purifierai-je ton cœur, dit le Seigneur Dieu, lorsque tu fais les œuvres d’une prostituée, et d’une impudente?
“‘Kina da rashin ƙarfi a zuci, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, sa’ad da kika yi duk waɗannan abubuwa, kina yi kamar karuwar da aka watsa!
31 Parce que tu t’es formé un lieu de débauche à la tête de toute voie, et tu l’es fait un haut lieu sur toute place publique; et tu n’as pas été comme une prostituée, augmentant son prix par dédain pour celui qui lui est offert,
Sa’ad da kika gina ɗakunan samanki a kowane gefen titi kika kuma gina ɗakunan tsafinki a kowane dandali, ba kamar karuwa kike ba, domin kin karɓi kuɗi.
32 Mais comme une femme adultère, qui préfère des étrangers à son mari.
“‘Ke mazinaciyar mace! Kin gwammace baƙi a maimakon mijinki!
33 À toutes les prostituées on donne des récompenses; mais toi tu as donné des récompenses à tous tes amants, et tu leur faisais beaucoup de présents, afin qu’ils vinssent de toutes parts pour forniquer avec toi.
Kowace karuwa kan karɓi kuɗi, amma kina ba da kyautai ga dukan kwartayenki, kina ba su cin hanci don su zo wurinki daga ko’ina don alherai marasa ƙa’ida.
34 Et il est arrivé en toi dans tes fornications le contraire de la coutume des autres femmes; et après toi il n’y aura pas de fornication, car par cela même que tu as donné des récompenses, et que tu n’as pas reçu de récompenses, il est arrivé en toi le contraire des autres.
Saboda haka cikin karuwancinki kin sha bamban da saura; babu wanda yake binki saboda alheranki. Ke dai dabam ce, gama kikan biya kuma ba mai biyanki.
35 À cause de cela, femme de mauvaise vie, écoute la parole du Seigneur.
“‘Saboda haka, ke karuwa, ki ji maganar Ubangiji!
36 Voici ce que dit le Seigneur Dieu: Parce que ton argent a été dissipé, et que ton ignominie s’est révélée dans tes fornications avec tes amants et avec tes idoles abominables, et dans le sang de tes enfants que tu leur as donnés:
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa domin kin zubar da dukiyarki kika bayyana tsiraicinki cikin fasikancinki da kwartayenki, kuma saboda dukan gumakan banƙyamarki, kuma saboda kin ba su jinin’ya’yansu,
37 Voilà que moi j’assemblerai tous tes amants, auxquels tu t’es prostituée, et tous ceux que tu as aimés avec tous ceux que tu haïssais; et je les assemblerai contre toi de toutes parts, et je mettrai à nu ton ignominie devant eux, et ils verront toute ta turpitude.
saboda haka zan tattara dukan kwartayenki, waɗanda kike jin daɗinsu, waɗanda kike ƙauna da waɗanda kike ƙi. Zan tattara su gāba da ke daga dukan kewaye zan kuma tuɓe ki a gabansu, za su kuwa ga dukan tsiraicinki.
38 Et je te jugerai comme on juge les femmes adultères et qui ont répandu le sang; et je livrerai ton sang à la fureur et à la jalousie.
Zan hukunta ki da hukuncin matan da suke zina da kuma waɗanda suke zub da jini; zan kawo hakkin jini na fushina da kuma fushin kishina.
39 Et je te livrerai à leurs mains et ils détruiront ta maison de débauche, et ils renverseront ta maison de prostitution, et ils te dépouilleront de tes vêtements, et ils enlèveront les ornements de ta gloire, et ils te laisseront nue et pleine d’ignominie;
Sa’an nan zan miƙa ki ga kwartayenki, za su kuwa rurrushe ɗakunan samanki su kuma farfashe ɗakunan tsafinki. Za su tuɓe miki tufafinki su kuma kwashe kayan adonki masu kyau su bar ki tsirara tik.
40 Et ils amèneront contre toi une multitude, et ils t’accableront de pierres, et ils t’égorgeront avec leurs glaives.
Za su kawo taron jama’a a kanki, waɗanda za su jajjefe ki da dutse su sassare ki gunduwa-gunduwa da takubansu.
41 Et ils mettront le feu à tes maisons, et ils exerceront contre toi des jugements aux yeux d’un très grand nombre de femmes; et tu cesseras de forniquer, et tu ne donneras plus de récompenses.
Za su ƙone gidajenki su kuma hukunta ki a idon mata masu yawa. Zan kawo ƙarshen karuwancinki, ba za ki kuma ƙara biyan kwartayenki ba.
42 Alors s’apaisera mon indignation contre toi, et ma jalousie se retirera de toi, et je me tiendrai en paix, et je ne m’irriterai plus.
Sa’an nan fushina a kanki zai huce fushin kishina kuma ya kwanta; zan huce ba kuwa zan ƙara yin fushi ba.
43 Parce que tu ne t’es pas souvenue des jours de ta jeunesse, et que tu m’as provoqué en tout ceci; c’est pourquoi moi aussi j’ai mis tes voies sur ta tête, dit le Seigneur Dieu; et je ne t’ai pas traitée selon tes crimes dans toutes tes abominations.
“‘Domin ba ki tuna da kwanakin ƙuruciyarki ba amma kika husatar da ni da waɗannan abubuwa, tabbatacce zan sāka miki alhakin ayyukanki, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Ba kin ƙara lalata ga dukan waɗansu ayyuka masu banƙyamarki ba?
44 Voilà que quiconque dit ordinairement des proverbes se servira de celui-ci contre toi en disant: Comme est la mère, ainsi sa fille.
“‘Duk mai yin amfani da karin magana zai faɗi wannan karin magana a kanki cewa, “Kamar yadda mahaifiya take haka’yar take.”
45 Toi, tu es vraiment la fille de ta mère qui a abandonné son mari et ses enfants; et tu es la sœur de tes sœurs, qui ont abandonné leurs maris et leurs enfants; votre mère était Céthéenne, et votre père Amorrhéen.
Ke’yar mahaifiyarki ce da gaske, wadda ta ƙi mijinta da’ya’yanta; ke kuma’yar’uwar’yar’uwanki mata ce da gaske, waɗanda suka ƙi mazansu da’ya’yansu. Mahaifiyarki mutuniyar Hitti ce, mahaifinki kuma mutumin Amoriyawa ne.
46 Et ta sœur aînée est Samarie, elle et ses filles, qui habitent à ta gauche; mais ta sœur puînée, qui habite à ta droite, est Sodome et ses filles.
Babbar’yar’uwarki mutuniyar Samariya ce, wadda take zaune da’ya’yanta mata wajen arewa da ke; ƙanuwarki ita ce Sodom wadda take zaune kudu da ke tare da’ya’yanta mata.
47 Mais tu n’as pas même marché dans leurs voies, et quant à leurs crimes, tu n’en as pas fait moins qu’elles; tu as fait des choses presque plus criminelles, dans toutes tes voies.
Ba ki bi hanyoyinsu da abubuwansu na banƙyama kaɗai ba, sai ka ce wannan ya yi miki kaɗan, amma kin lalace fiye da su.
48 Je vis, moi, dit le Seigneur Dieu, Sodome ta sœur, elle et ses filles, n’ont pas fait comme tu as fait, toi et tes filles.
Muddin in raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka,’yar’uwarki Sodom da’ya’yanta mata ba su yi abin da’ya’yanki mata suka yi ba.
49 Voici quelle a été l’iniquité de Sodome ta sœur: l’orgueil, l’excès de nourriture, l’abondance, et l’oisiveté d’elle et de ses filles; et elles ne tendaient pas la main à l’indigent et au pauvre.
“‘To, fa, ga zunubin’yar’uwarki Sodom. Ita da’ya’yanta mata sun yi girman kai, sun ƙoshi fiye da kima kuma ba su kula da wani abu ba; ba su taimaki matalauta da kuma masu bukata ba.
50 Et elles se sont élevées, et elles ont fait des abominations devant moi; et je les ai détruites comme tu as vu.
Su masu girman kai ne kuma suka aikata abubuwa masu banƙyama a gabana. Saboda haka na kau da su kamar yadda ka gani.
51 Et Samarie n’a pas commis la moitié de tes péchés; mais tu les as surpassées par tes crimes, et tu as justifié tes sœurs par toutes tes abominations que tu as faites.
Samariya ba tă aikata ko rabin zunubanki ba. Kin aikata abubuwa masu banƙyama fiye da su, suka kuma sa’yan’uwanki mata suka zama kamar masu adalci ta wurin dukan waɗannan abubuwa da kika aikata.
52 Porte donc aussi ta confusion, toi qui as surpassé tes sœurs par les péchés, agissant plus criminellement qu’elles: car elles ont été justifiées par toi; sois donc confondue, et porte ton ignominie, toi qui as justifié tes sœurs.
Ki sha kunyarki, gama kin yi rangwame wa’yan’uwanki mata. Saboda zunubanki sun yi muni fiye da nasu, sai suka zama kamar sun fi ki adalci. Saboda haka, ki sha kunya ki kuma sha ƙasƙancinki, gama kin sa’yan’uwanki mata suka zama kamar su masu adalci ne.
53 Et je les ferai retourner en les rétablissant par le retour de Sodome avec ses filles, et par le retour de Samarie et de ses filles, et je te ferai retourner au milieu d’elles,
“‘Amma fa, zan komo da nasarar Sodom da’ya’yanta mata da ta Samariya da’ya’yanta mata, nasararki kuma tare da su,
54 Afin que tu portes ton ignominie, et que tu sois confondue de tout ce que tu as fait, de manière à les consoler.
domin ki sha ƙasƙancinki ki kuma sha kunyar dukan abin da kika aikata ta wurin ta’azantar da su.
55 Ta sœur Sodome et ses filles retourneront à leur ancien état. Samarie et ses filles retourneront à leur ancien état; et toi et tes filles, vous retournerez à votre ancien état.
’Yan’uwanki kuwa, Sodom da’ya’yanta mata da Samariya tare da’ya’yanta mata, za su koma kamar yadda suke a dā; ke kuma da’ya’yanki mata za ku koma kamar yadda kike a dā.
56 Mais le nom même de Sodome, ta sœur, n’a pas été entendu sortir de ta bouche, au jour de ton orgueil,
Ba za ki ma iya ambaci’yar’uwarki Sodom a ranar fariyarki ba,
57 Avant qu’eût été révélée ta méchanceté, comme elle l’a été en ce temps où tu es devenue l’opprobre des filles de Syrie et de toutes les filles de la Palestine qui t’environnent de toutes parts.
kafin a tone muguntarki. Ko da ma haka, yanzu’ya’yan Arameyawa mata da dukan maƙwabtanta da kuma’ya’yan Filistiyawa mata suna miki dariyar, dukan waɗanda suke kewaye da ke da suka rena ki.
58 Tu as porté ton crime et ton ignominie, dit le Seigneur Dieu.
Za ki ɗauki hakkin lalatarki da kuma ayyukanki masu banƙyama, in ji Ubangiji.
59 Parce que voici ce que dit le Seigneur Dieu: Je te ferai comme tu as fait, toi qui as méprisé un serment, afin de rendre vaine une alliance.
“‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan hukunta kamar yadda ya dace da ke, domin kin ƙyale rantsuwana ta wurin karya alkawari.
60 Et moi je me souviendrai de mon alliance avec toi aux jours de ta jeunesse, et j’établirai avec toi une alliance éternelle.
Duk da haka zan tuna da alkawarin da na yi da ke a kwanakin ƙuruciyarki, zan kuma kafa madawwamin alkawari da ke.
61 Et tu te souviendras de tes voies, et tu seras confondue, lorsque tu recevras avec toi tes sœurs aînées et tes sœurs puînées; et je te les donnerai pour filles, mais non par une alliance qui vienne de toi.
Sa’an nan za ki tuna da hanyoyinki ki kuma ji kunya sa’ad da kika karɓi’yan’uwanki mata, waɗanda suka girme ki da kuma waɗanda kika girme su. Zan ba da su kamar’ya’ya mata gare ki, amma ba bisa alkawarina da ke ba.
62 Et moi j’établirai mon alliance avec toi; et tu sauras que je suis le Seigneur,
Ta haka zan kafa alkawarina da ke, za ki kuma san cewa ni ne Ubangiji.
63 Afin que tu te souviennes et que tu sois confondue, et qu’il n’y ait plus lieu pour toi d’ouvrir la bouche, à cause de ta confusion, lorsque je t’aurai pardonné tout ce que tu as fait, dit le Seigneur Dieu.
Sa’an nan, sa’ad da na yi kafara saboda ke domin dukan abin da kika aikata, za ki tuna ki kuma ji kunya har ki kāsa buɗe bakinki saboda kunya, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”