< Ézéchiel 14 >
1 Et vinrent vers moi des hommes des anciens d’Israël, et ils s’assirent devant moi.
Waɗansu dattawan Isra’ila suka zo wurina suka zauna a ƙasa a gabana.
2 Et la parole du Seigneur me fut adressée, disant:
Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
3 Fils d’un homme, ces hommes ont mis leurs impuretés dans leurs cœurs, et placé le scandale de leur iniquité devant leur face; est-ce que consulté, je leur répondrai?
“Ɗan mutum, waɗannan mutane sun kafa gumaka a cikin zukatansu suka sa mugayen abubuwan sa tuntuɓe a gabansu. Zan bar su, su taɓa nemi ni?
4 À cause de cela, parle-leur, et tu leur diras: Voici ce que dit le Seigneur Dieu: Tout homme de la maison d’Israël qui aura mis ses impuretés dans son cœur, et aura placé le scandale de son iniquité devant sa face, et sera venu vers le prophète, m’interrogeant par lui, moi le Seigneur, je lui répondrai selon la multitude de ses impuretés;
Saboda haka ka yi musu magana ka faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa sa’ad da wani mutumin Isra’ila ya kafa gumaka a cikin zuciyarsa ya kuma sa mugun abin tuntuɓe a gabansa sa’an nan ya tafi wurin annabi, Ni Ubangiji zan amsa masa da kaina game da babban bautar gumakarsa.
5 Afin que la maison d’Israël soit prise dans son cœur, par lequel ils se sont retirés de moi pour s’attacher à toutes leurs idoles.
Zan yi haka don in sāke ƙame zukatan mutanen Isra’ila, waɗanda duk suka yashe ni don gumakansu.’
6 À cause de cela, dis à la maison d’Israël: Voici ce que dit le Seigneur Dieu: Convertissez-vous, retirez-vous de vos idoles, et de toutes vos souillures détournez vos faces.
“Saboda haka ka faɗa wa gidan Isra’ila cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ku tuba! Ku juyo daga gumakanku ku kuma furta dukan ayyukanku masu banƙyama!
7 Car tout homme de la maison d’Israël, et quiconque d’entre les prosélytes est étranger en Israël, s’il s’est détourné de moi et qu’il ait mis ses idoles dans son cœur, et qu’il ait placé le scandale de son iniquité devant sa face, et qu’il soit venu vers le prophète pour me consulter par lui; moi, le Seigneur, je lui répondrai moi-même.
“‘Duk sa’ad da mutumin Isra’ila ko baƙo mai zama a Isra’ila ya rabu da ni ya kuma kafa gumaka a cikin zuciyarsa ya kuna sa mugun abin tuntuɓe a gabansa sa’an nan ya tafi wurin annabi don yă neme ni, Ni Ubangiji zan amsa masa da kaina.
8 Et je tournerai ma face contre cet homme, et je le donnerai en exemple et en proverbe, et je l’exterminerai du milieu de mon peuple; et vous saurez que je suis le Seigneur.
Zan yi gāba da mutumin in kuma sa ya zama misali da kuma abin karin magana. Zan ware shi daga mutanena. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.
9 Et lorsque le prophète a erré et qu’il a dit une parole, c’est moi, le Seigneur, qui ai trompé ce prophète; et j’étendrai ma main sur lui, et je l’effacerai du milieu de mon peuple d’Israël.
“‘In kuma aka ruɗi annabin har ya yi annabci, Ni Ubangiji na rinjayi wannan annabi, zan kuma miƙa hannuna gāba da shi in hallaka shi daga cikin mutanena Isra’ila.
10 Et ils porteront leur iniquité; selon l’iniquité de celui qui consulte, ainsi sera l’iniquité du prophète;
Za su ɗauki hakkin laifinsu annabin zai zama mai laifi daidai da wanda ya zo neman shawararsa.
11 Afin que la maison d’Israël ne s’égare plus en se retirant de moi, et qu’elle ne se souille point par toutes ses prévarications; mais qu’ils soient mon peuple, et que moi je sois leur Dieu, dit le Seigneur des armées.
Sa’an nan mutanen Isra’ila ba za su ƙara kauce daga gare ni ba, ba kuwa za su ƙara ƙazantar da kansu da dukan zunubansu ba. Za su zama mutanena, ni kuma zan zama Allahnsu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
12 Et la parole du Seigneur me fut adressée, disant:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
13 Fils d’un homme, quant à une terre, lorsqu’elle aura péché contre moi en multipliant ses prévarications, j’étendrai ma main sur elle, et je briserai la verge de son pain, et j’enverrai sur elle la famine, et j’en tuerai les hommes et les bêtes.
“Ɗan mutum, in wata ƙasa ta yi mini zunubi ta wurin rashin aminci na kuma miƙa hannuna gāba da ita don in toshe hanyar samun abincinta na kuma aika da yunwa a kanta na kashe mutanenta da dabbobinta,
14 Et si ces trois hommes justes, Noé, Daniel et Job, sont au milieu d’elle, eux-mêmes, par leur justice, délivreront leurs âmes, dit le Seigneur des armées.
ko da waɗannan mutum uku Nuhu, Daniyel da kuma Ayuba suna a cikinta, za su iya ceton kansu ne kawai ta wurin adalcinsu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
15 Que si j’amène sur cette terre des bêtes cruelles, afin que je la dévaste, et qu’elle devienne inaccessible, pour qu’il n’y ait personne qui y passe à cause des bêtes;
“Ko kuwa in na aika da namun jeji su ratsa cikin wannan ƙasa suka kuma bar ta babu yaro, ta kuma zama kufai har babu wanda zai ratsa cikinta saboda namun jeji,
16 Si ces trois hommes y sont, je vis, moi, dit le Seigneur Dieu, ils ne délivreront ni leurs fils, ni leurs filles; mais eux seuls seront délivrés, et la terre sera désolée.
muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, ko da ma waɗannan mutum uku suna a cikinta, ba za su iya ceton’ya’yansu maza ko mata ba. Su kaɗai za a iya ceto, amma ƙasar za tă zama kufai.
17 Ou si j’amène le glaive sur cette terre, et que je dise au glaive: Passe par cette terre, et que j’en tue les hommes et les bêtes;
“Ko kuma in na kawo takobi a kan wannan ƙasa na kuma ce, ‘Bari takobin ya ratsa cikin dukan ƙasar,’ na kuma kashe mutanenta da dabbobinsu,
18 Et que ces trois hommes soient au milieu d’elle; je vis, moi, dit le Seigneur Dieu, ils ne délivreront ni leurs fils, ni leurs filles; mais eux seuls seront délivrés.
muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, ko da waɗannan mutum uku suna cikinta, ba za su iya ceton’ya’yansu maza ko mata ba. Su kaɗai za a iya ceto.
19 Mais si j’envoie la peste sur cette terre et que je répande mon indignation sur elle par le sang, afin que j’en enlève les hommes et les bêtes;
“Ko kuma in na aika da annoba a cikin wannan ƙasa na kuma yi fushi a kanta ta wurin kisa, ina kisan mutanenta da dabbobinsu,
20 Et que Noé, Daniel et Job soient au milieu d’elle, je vis, moi, dit le Seigneur Dieu, ils ne délivreront ni fils, ni fille; mais par leur justice ils délivreront leurs propres âmes.
muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, ko da Nuhu, Daniyel da Ayuba suna a cikinta, ba za su iya ceton ɗansu ko’yarsu ba. Za su iya ceton kansu ne kaɗai ta wurin adalcinsu.
21 Parce que voici ce que dit le Seigneur Dieu: Que si j’envoie à Jérusalem mes quatre jugements cruels, le glaive, la famine, les bêtes mauvaises, et la peste, afin que j’en tue homme et bétail,
“Gama ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa balle fa sa’ad da na aika wa Urushalima da hukuntaina guda huɗu masu zafi takobi da yunwa da namun jeji da annoba don su kashe mutanenta da dabbobinsu!
22 Cependant il y sera laissé des hommes qui se sauveront, et feront sortir leurs fils et leurs filles; voilà qu’eux-mêmes viendront vers vous, et que vous verrez leur voie et leurs inventions, et que vous serez consolés du mal que j’aurai amené sur Jérusalem, et de tous les fléaux dont je l’aurai accablée.
Duk da haka za a sami mutanen da za su ragu’ya’ya maza da matan da za a fitar daga cikinta. Za su zo wurinka, kuma sa’ad da ka gan halinsu da ayyukansu, za ka ta’azantu game da bala’in da na kawo a kan Urushalima kowane bala’in da na kawo a kanta.
23 Et ils vous consoleront, lorsque vous verrez leur voie et leurs inventions; et vous reconnaîtrez que ce n’est pas sans raison que j’aurai fait à Jérusalem tout ce que j’y aurai lait, dit le Seigneur Dieu.
Za ka ta’azantu sa’ad da ka ga halinsu da kuma ayyukansu, gama za ka san cewa ban aikata wani abu a cikinta ba dalili ba, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”