< Exode 33 >

1 Le Seigneur parla ensuite à Moïse, disant: Va, monte de ce lieu, toi et ton peuple que j’ai retiré de la terre d’Egypte, en la terre que j’ai jurée à Abraham, à Isaac et à Jacob, disant: C’est à ta postérité que je la donnerai;
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka bar wannan wuri, kai da mutanen da ka fito da su daga Masar, ka haura zuwa ƙasar da na alkawarta da rantsuwa wa Ibrahim, Ishaku da Yaƙub cewa, ‘Zan ba zuriyarka.’
2 Et j’enverrai pour ton précurseur, un ange, afin que je chasse le Chananéen, l’Amorrhéen, l’Héthéen, le Phérézéen, l’Hévéen et le Jébuséen,
Zan aika da mala’ika a gabanka in kuma kori Kan’aniyawa, Amoriyawa, Hittiyawa, Ferizziyawa, Hiwiyawa da Yebusiyawa.
3 Et que tu entres dans une terre où coulent du lait et du miel. Car je ne monterai pas avec toi, parce que tu es un peuple d’un cou roide; de peur que je ne te détruise dans le chemin.
Ka haura zuwa ƙasar da take zub da madara da zuma. Amma ba zan tafi tare da ku ba, saboda ku mutane ne masu taurinkai domin mai yiwuwa in hallaka ku a hanya.”
4 Or, le peuple entendant cette parole très fâcheuse, pleura, et nul ne se revêtit, comme à l’ordinaire, de sa parure.
Da mutane suka ji wannan mugun magana, sai suka fara makoki. Ba kuma wanda ya sa kayan ado.
5 Ainsi le Seigneur dit à Moïse: Dis aux enfants d’Israël: Tu es un peuple d’un cou roide, je monterai une seule fois au milieu de toi, et je t’exterminerai. Dès maintenant, dépose tes ornements, afin que je sache ce que je te ferai.
Gama Ubangiji ya riga ya ce wa Musa, “Ka faɗa wa Isra’ilawa, ‘Ku mutane ne masu taurinkai. In na yi tafiya da ku ko na ɗan lokaci, mai yiwuwa in hallaka ku. Yanzu sai ku tuɓe kayan adonku, zan kuwa yanke shawara a kan abin da zan yi da ku.’”
6 Les enfants d’Israël déposèrent donc leurs ornements dès la montagne d’Horeb.
Saboda haka Isra’ilawa suka tuttuɓe kayan adonsu a Dutsen Horeb.
7 Moïse aussi prenant le tabernacle le dressa hors du camp au loin, et il l’appela du nom de Tabernacle d’alliance. Et tous ceux du peuple qui avaient quelque question, sortaient vers le tabernacle d’alliance, hors du camp.
Musa fa ya saba ɗaukan tenti yă kafa shi a bayan sansani da ɗan nisa, yana kiransa “Tentin Sujada.” Duk wanda yake neman wani abu daga wurin Ubangiji sai yă tafi Tentin Sujada a bayan sansani.
8 Et lorsque Moïse sortait vers le tabernacle, le peuple entier se levait, et se tenait chacun à la porte de son pavillon et regardait Moïse par derrière, jusqu’à ce qu’il entrait dans le tabernacle.
A sa’ad da kuma Musa ya fita zuwa Tentin, dukan mutanen sukan tashi su tsaya a ƙofofin tentinsu, suna kallon Musa, sai ya shiga tentin.
9 Or, Moïse entré dans le tabernacle d’alliance, la colonne de nuée descendait, et se tenait à la porte et le Seigneur parlait avec Moïse,
Yayinda Musa ya shiga cikin tentin, sai al’amudin girgije yă sauko, yă tsaya a ƙofar yayinda Ubangiji yana magana da Musa.
10 Tous voyant que la colonne de nuée se tenait à la porte du tabernacle. Et ils se tenaient eux-mêmes, et ils adoraient à la porte de leurs tentes.
Lokacin da mutane suka ga al’amudin girgije a tsaye a ƙofar tentin, sai duk su miƙe tsaye su yi sujada, kowa a ƙofar tentinsa.
11 Or, le Seigneur parlait à Moïse face à face, comme a coutume de parler un homme à son ami. Et lorsque Moïse retournait au camp, son serviteur Josué, jeune homme, fils de Nun, ne s’éloignait pas du tabernacle.
Ubangiji yakan yi magana da Musa fuska da fuska, kamar yadda mutum yake magana da abokinsa. Sa’an nan Musa yă koma sansani, amma saurayin nan Yoshuwa ɗan Nun mai taimakonsa ba ya barin tentin.
12 Or, Moïse dit au Seigneur: Vous m’ordonnez d’emmener ce peuple, et vous ne m’indiquez pas celui que vous devez envoyer avec moi, quoique cependant vous m’ayez dit: Je te connais nommément, et tu as trouvé grâce devant moi.
Musa ya ce wa Ubangiji, “Kana ta faɗa mini cewa, ‘Ka jagoranci mutane nan,’ amma ba ka faɗa mini wanda zai tafi tare da ni ba. Ga shi ka ƙara ce mini, ‘Na san ka, na san sunanka, ka kuma sami tagomashi a wurina.’
13 Si donc j’ai trouvé grâce en votre présence, montrez-moi votre visage, afin que je vous connaisse, et que je trouve grâce devant vos yeux: regardez votre peuple, cette nation.
In ka ji daɗina, ka koya mini hanyarka don in san ka, in kuma ci gaba da samun tagomashi daga gare ka. Ka tuna cewa wannan al’umma mutanenka ne.”
14 Et le Seigneur répondit: Ma face te précédera, et je te donnerai le repos.
Ubangiji ya amsa ya ce, “Zan tafi tare da kai, zan kuma rage maka nauyin kaya.”
15 Et Moïse reprit: Si vous ne nous précédez vous-même, ne nous retirez pas de ce lieu.
Musa kuwa ya ce masa, “In ba za tă tafi tare da mu ba, to, kada ka ɗaga mu daga nan.
16 Car en quoi pourrons-nous savoir, moi et votre peuple, que nous avons trouvé grâce en votre présence, si vous ne marchez avec nous, afin que nous soyons glorifiés par tous les peuples qui habitent sur la terre?
Yaya wani zai sani ko ka ji daɗina da kuma mutanenka, in ba ka tafi tare da mu ba? Mene ne kuma zai bambanta ni da mutanenka daga sauran jama’ar da suke a duniya?”
17 Or le Seigneur dit à Moïse: Cette parole même que tu as dite, je l’accomplirai: car tu as trouvé grâce devant moi, et je te connais toi-même nommément.
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Zan yi yadda ka faɗa, gama ka sami tagomashi a wurina, na san ka, na kuma san sunanka.”
18 Moïse dit: Montrez-moi votre gloire.
Musa kuwa ya ce, “To, ka nuna mini ɗaukakarka.”
19 Le Seigneur répondit: Moi, je te montrerai toute sorte de biens, je prononcerai le nom du Seigneur devant toi, je ferai miséricorde à qui je voudrai, et je serai clément envers qui il me plaira.
Sai Ubangiji ya ce, “Zan wuce a gabanka, Ni Ubangiji zan yi shelar sunana a gabanka. Zan yi alheri ga duk wanda na so in yi masa alheri, zan nuna jinƙai ga duk wanda na so in yi masa jinƙai.
20 Et de nouveau il dit: Tu ne pourras voir ma face; car l’homme ne saurait me voir et vivre.
Amma ya ce, ba za ka ga fuskata ba, don ba mutumin da zai gan ni yă rayu.”
21 Et encore: Voici, dit-il, un lieu près de moi, et tu te tiendras sur là pierre.
Sa’an nan Ubangiji ya ce, “Ga wani wuri kusa da ni inda za ka tsaya bisa dutsen.
22 Et lorsque passera ma gloire, je te placerai à l’ouverture de la pierre et je te couvrirai de ma droite, jusqu’à ce que je sois passé,
A sa’ad da ɗaukakata tana wucewa, zan sa ka a cikin tsaguwar dutsen, in rufe ka da hannuna har sai na wuce.
23 J’ôterai alors ma main, et tu me verras par derrière; mais ma face, tu ne la verras point.
Sa’an nan zan ɗauke hannuna, ka kuwa ga bayana; amma fuskata, ba za ka gani ba.”

< Exode 33 >