< Exode 17 >
1 Ainsi toute la multitude des enfants d’Israël étant partie du désert de Sin, et ayant fait des séjours, selon les paroles du Seigneur, ils campèrent à Raphidim, où il n’y avait pas d’eau à boire pour le peuple,
Dukan taron Isra’ilawa suka kama tafiya daga Hamadar Sin, suka yi ta tafiya suna sauka a wurare dabam-dabam bisa ga umarnin Ubangiji. A ƙarshe suka sauka a Refidim, suka zauna a can, amma ba ruwan da jama’a za su sha.
2 Qui querellant Moïse, dit: Donne-nous de l’eau, afin que nous buvions. Moïse leur répondit: Pourquoi me querellez-vous? pourquoi tentez-vous le Seigneur?
Saboda haka suka yi wa Musa maganganun banza suka ce, “Ba mu ruwa mu sha.” Musa ya amsa ya ce, “Don me kuke mini maganganun banza? Don me kuke gwada Ubangiji?”
3 Là donc le peuple eut soif à cause de la pénurie d’eau, et il murmura contre Moïse, disant: Pourquoi nous as-tu fait sortir de l’Egypte, pour nous faire mourir de soif, nous, nos enfants et nos bêtes?
Amma mutanen suka yi fama da ƙishirwa a can, suka yi gunaguni a kan Musa. Suka ce, “Don me ka fitar da mu daga Masar, ka sa mu da’ya’yanmu da dabbobinmu, mu mutu da ƙishirwa?”
4 Or Moïse cria au Seigneur, disant: Que ferai-je à ce peuple-ci? encore un peu, et il me lapidera.
Sai Musa ya yi kuka ga Ubangiji ya ce, “Me zan yi da wannan jama’a? Suna shiri su jajjefe ni da duwatsu.”
5 Et le Seigneur répondit à Moïse: Marche devant le peuple, et prends avec toi des anciens d’Israël; et la verge dont tu as frappé le fleuve, prends-la en ta main, et va.
Ubangiji amsa wa Musa, “Ka ɗauki sandan da ka bugi ruwan Nilu da shi. Ka kira waɗansu shugabannin Isra’ila, ku wuce a gaban jama’ar.
6 Voilà que moi, je me tiendrai là devant toi sur la pierre d’Horeb; et tu frapperas la pierre, et il en sortira de l’eau, afin que le peuple boive. Moïse fit ainsi devant les anciens d’Israël:
Zan tsaya a can a gabanka, kusa da dutsen Horeb. Ka bugi dutsen, ruwa kuwa zai fito daga gare shi domin mutane su sha.” Sai Musa ya yi haka a idon dattawan Isra’ila.
7 Et il appela ce lieu du nom de Tentation, à cause de la querelle des enfants d’Israël, et parce qu’ils avaient tenté le Seigneur, disant: Le Seigneur est-il parmi nous, ou non?
Sai suka ba wa wurin suna, Massa da Meriba, saboda Isra’ilawa sun yi jayayya, suka kuma gwada Ubangiji cewa, “Ubangiji yana tsakaninmu ko babu?”
8 Or Amalec vint, et il combattait contre Israël à Raphidim.
Amalekawa suka zo, suka yaƙi Isra’ilawa a Refidim.
9 Et Moïse dit à Josué: Choisis des hommes, et étant sorti, combats contre Amalec; demain moi, je me tiendrai au sommet de la colline, ayant la verge de Dieu en ma main.
Musa ya ce wa Yoshuwa, “Zaɓi waɗansu mazanmu, ka je ka yaƙi Amalekawa. Gobe zan tsaya a bisa tudu, da sandan Allah a hannuwana.”
10 Josué fit comme avait dit Moïse, et il combattait contre Amalec: mais Moïse et Aaron et Hur montèrent sur le sommet de la colline.
Sai Yoshuwa ya yaƙi Amalekawa kamar yadda Musa ya umarta, Musa, Haruna da Hur kuwa suka tafi bisa tudu.
11 Et lorsque Moïse élevait les mains, Israël était victorieux; mais s’il les abaissait un peu, Amalec l’emportait.
Muddin hannun Musa yana a miƙe, sai Isra’ilawa su yi ta cin nasara, amma da zarar hannunsa ya sauka, sai Amalekawa su yi ta cin nasara.
12 Or, les mains de Moïse étaient appesanties; prenant donc une pierre, ils la mirent sous lui; il s’y assit; mais Aaron et Hur soutenaient ses mains des deux côtés. Et il arriva que ses mains ne se lassèrent pas jusqu’au coucher du soleil.
Sa’ad da hannuwan Musa suka gaji, sai Haruna da Hur suka ɗauki dutse suka sa ya zauna a kai. Sa’an nan su kuma suka tsaya gefe da gefe, suna riƙe da hannuwansa har fāɗuwar rana.
13 Et Josué mit en fuite Amalec et son peuple, par le tranchant du glaive.
Sai Yoshuwa kuwa ya ci nasara a kan Amalekawa da takobi.
14 Or le Seigneur dit à Moïse: Écris ceci pour souvenir dans le livre, et fais-le entendre à Josué; car j’effacerai la mémoire d’Amalec sous le ciel.
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka rubuta wannan a cikin littafi, yă zama abin tuni, ka kuma faɗa wa Yoshuwa zan hallaka Amalekawa ƙaƙaf daga duniya.”
15 Et Moïse bâtit un autel et rappela du nom de: Le Seigneur est mon exaltation, disant:
Musa ya gina bagade, sai ya kira shi Ubangiji shi ne Tutata.
16 La main du trône du Seigneur et la guerre du Seigneur seront contre Amalec de génération en génération.
Ya ce, “Gama an ɗaga hannuwa sama zuwa kursiyin Ubangiji, Ubangiji zai yaƙi Amalekawa daga tsara zuwa tsara.”