< Exode 12 >

1 Le Seigneur dit aussi à Moïse et à Aaron dans la terre d’Egypte:
Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna a Masar,
2 Ce mois sera pour vous le commencement des mois: il sera le premier dans les mois de l’année.
“Wannan wata za tă zama a gare ku wata na farko, wata na fari na shekararku.
3 Parlez à toute l’assemblée des enfants d’Israël, et dites-leur: Au dixième jour de ce mois, que chacun prenne un agneau par chacune de ses familles et de ses maisons.
Ka faɗa wa dukan jama’ar Isra’ila cewa a rana ta goma ga wannan wata, kowane mutum zai ɗauki ɗan rago domin iyalinsa, ɗaya domin kowane gida.
4 Mais si le nombre est trop petit pour qu’il puisse suffire à manger l’agneau, il prendra son voisin qui est proche de sa maison, selon le nombre des âmes qui peuvent suffire à manger l’agneau.
In akwai wani gidan da ba za su iya cinye rago guda ɗungum ba, saboda iyalin kima ne, to, sai su haɗa kai da maƙwabtansu, su ɗauki rago guda gwargwadon yawansu, bisa ga abin da mutum guda zai ci.
5 Or l’agneau sera sans tache, mâle, ayant un an. Conformément à ce rite vous prendrez aussi un chevreau.
Dabbobin da za ku zaɓa, dole su zama bana ɗaya, namiji marar tabo, za ku kuma kamo su daga cikin tumaki ko awaki.
6 Et vous le garderez jusqu’au quatorzième jour de ce mois; et toute la multitude des enfants d’Israël l’immolera vers le soir.
Za ku turke dabbar har rana ta goma sha huɗu ga wata, wato, sa’ad da dukan taron jama’ar Isra’ila za su yanka ragunansu da yamma.
7 Ils prendront de son sang, et ils en mettront sur les deux poteaux et sur les linteaux des maisons, en lesquelles ils les mangeront.
Sa’an nan za su ɗauki jinin, su shafa a gefen da yake saman dogaran ƙofa na gidajen da suke cin naman dabbobin.
8 Et ils mangeront cette nuit-là les chairs rôties au feu avec des pains azymes et avec des laitues sauvages.
A wannan dare, za su gasa naman, su ci da ganyaye masu ɗaci, da kuma burodi marar yisti.
9 Vous n’en mangerez rien cru, ni cuit dans l’eau, mais seulement rôti au feu; vous en mangerez la tête avec les pieds et les intestins.
Kada ku ci nama ɗanye, ko kuma dafaffe, amma a gasa shi, da kan, da ƙafafun, da kuma kayan cikin.
10 Il n’en demeurera rien jusqu’au matin: s’il y a quelque reste, vous le brûlerez au feu.
Kada ku bar kome yă kai gobe, abin da ya kai gobe kuwa, sai ku ƙone shi.
11 Or c’est ainsi que vous le mangerez: Vous ceindrez vos reins; et vous aurez votre chaussure à vos pieds, tenant un bâton en vos mains, et vous mangerez à la hâte; car c’est la Pâque, (c’est-à-dire) le passage du Seigneur.
Ga yadda za ku ci shi, ku yi ɗamara, takalma kuwa a ƙafafunku, kuna riƙe da sandunan tafiya a hannunku. Ku ci shi da gaggawa; Bikin Ƙetarewa ne na Ubangiji.
12 Et je passerai par la terre d’Egypte cette nuit-là, et je frapperai tout premier-né dans la terre d’Egypte, depuis l’homme jusqu’au bétail, et sur tous les dieux de l’Egypte j’exercerai des jugements, moi le Seigneur.
“A wannan dare, zan ratsa Masar, in bugi kowane ɗan fari, na mutum da na dabba, zan kuma hukunta dukan gumakan Masar. Ni ne Ubangiji.
13 Or le sang sera un signe en votre faveur dans les maisons où vous serez; car je verrai le sang, et je passerai au-delà de vous; et la plaie de destruction ne vous atteindra pas lorsque je frapperai la terre d’Egypte.
Jinin zai zama alama a gare ku, a gidajen da kuke; sa’ad da kuwa na ga jinin, zan ƙetare ku. Ba wata annoba mai hallakarwa da za tă taɓa ku yayinda na bugi Masar.
14 Ce jour sera pour vous un monument, et vous le célébrerez dans vos générations comme consacré au Seigneur par un culte éternel.
“Wannan rana za tă zama muku abin tunawa dukan zamananku masu zuwa, za ku kiyaye ta kamar biki ga Ubangiji, dawwammamiyar farilla ce har abada.
15 Pendant sept jours vous mangerez des azymes: dès le premier jour il n’y aura point de levain dans vos maisons; quiconque mangera du pain levé, depuis le premier jour jusqu’au septième jour, son âme périra du milieu d’Israël.
Kwana bakwai za ku ci burodi marar yisti. A rana ta fari, za ku fid da yisti daga gidajenku gama duk wanda ya ci abu mai yisti daga rana ta fari har zuwa rana ta bakwai, za a fid da shi daga Isra’ila.
16 Le premier jour sera saint et solennel, et le septième jour sera vénérable par la même solennité: vous ne ferez aucun travail en ces jours-là, excepté ce qui regarde la nourriture.
A rana ta fari, za ku yi taro mai tsarki, haka kuma za ku sāke yi a rana ta bakwai. Kada ku yi aiki a waɗannan ranaku, sai dai ku shirya abinci domin kowa, abin da za ku yi ke nan kawai.
17 Vous observerez donc la fête des Azymes; car c’est en ce même jour que je conduirai votre armée hors de la terre d’Egypte: ainsi vous garderez ce jour en vos générations par un rite perpétuel.
“Ku yi Bikin Burodi Marar Yisti domin a wannan rana ce na fitar da ku ɓangare-ɓangare daga Masar. Ku kiyaye wannan rana ta zama muku dawwammamiyar farilla wa tsara masu zuwa.
18 Au premier mois, le quatorzième jour du mois, vers le soir, vous mangerez des azymes jusqu’au vingt-unième jour du même mois, vers le soir.
A wata na fari, za ku ci burodi marar yisti daga yammancin ranar goma sha huɗu har zuwa yammancin ranar ashirin da ɗaya.
19 Sept jours durant, on ne trouvera point de levain dans vos maisons: celui qui mangera du pain levé, son âme périra du milieu de l’assemblée d’Israël, qu’il soit étranger ou naturel du pays.
Kada a sami yisti a gidajenku har kwana bakwai. Kuma duk wanda ya ci wani abu mai yisti, za a fid da shi daga taron jama’ar Isra’ila, ko baƙo ne, ko haifaffen ɗan ƙasa.
20 Vous ne mangerez rien de fermenté; dans toutes vos habitations vous mangerez des azymes.
Kada ku ci wani abincin da aka yi da yisti. Ko’ina kuka zauna, dole ku ci burodi marar yisti.”
21 Or Moïse appela tous les anciens des enfants d’Israël et leur dit: Allez, et prenez un animal par chacune de vos familles, et immolez la Pâque.
Sa’an nan Musa ya kira dukan dattawan Isra’ila ya ce musu, “Ku je da sauri ku zaɓi dabbobin iyalanku, ku yanka ragon Bikin Ƙetarewa.
22 Trempez un bouquet d’hysope dans le sang qui est sur le seuil de la porte, et vous en aspergerez le linteau et les deux poteaux, et que nul de vous ne sorte hors de la porte de sa maison jusqu’au matin.
Ku ɗauki ƙunshin itacen hizzob, ku tsoma cikin jinin da yake a kwano, ku yayyafa wa dogaran ƙofa duka biyu, da bisa kan ƙofar. Kada wani daga cikinku yă fita daga ƙofar gidansa sai da safe.
23 Car le Seigneur passera frappant les Egyptiens; et lorsqu’il verra le sang sur le linteau et sur les poteaux, il passera au-delà de la porte de la maison, et il ne permettra pas que le destructeur entre dans vos maisons et vous frappe.
Sa’ad da Ubangiji yake ratsa ƙasar don yă bugi Masarawa, zai ga jinin a bisa da kuma gefen madogaran ƙofa, zai ƙetare ƙofar, ba zai bar mai hallakawa yă shiga gidajenku, yă buge ku ba.
24 Garde cette parole comme une loi éternelle pour toi et pour tes enfants.
“Ku kiyaye waɗannan dokokin a matsayin dawwammamiyar farilla, da ku da’ya’yanku har abada.
25 Et lorsque vous serez entrés dans le pays que le Seigneur doit vous donner, comme il a promis, vous observerez ces cérémonies.
Sa’ad da kuka shiga ƙasar da Ubangiji zai ba ku yadda ya alkawarta, ku kiyaye wannan biki.
26 Et quand vos enfants vous demanderont: Quel est ce culte religieux?
Sa’ad da kuma’ya’yanku suka tambaye ku, ‘Mece ce manufar wannan biki?’
27 Vous leur direz: C’est la victime du passage du Seigneur, quand il passa par-dessus les maisons des enfants d’Israël en Egypte, frappant les Egyptiens, et préservant nos maisons. Alors le peuple profondément incliné adora.
Sai ku faɗa musu, ‘Hadaya ce ta Bikin Ƙetarewa ga Ubangiji, domin ya tsallake gidajen Isra’ilawa a Masar, lokacin da ya kashe Masarawa, amma bai taɓa gidajenmu ba.’” Sai mutane suka rusuna, suka yi sujada.
28 Et étant sortis, les enfants d’Israël firent comme le Seigneur avait ordonné à Moïse et à Aaron.
Isra’ilawa suka tafi suka yi yadda Ubangiji ya umarci Musa da Haruna.
29 Or il arriva au milieu de la nuit que le Seigneur frappa tous les premiers-nés dans la terre d’Egypte, depuis le premier-né de Pharaon qui était assis sur son trône, jusqu’au premier-né de la captive qui était en prison, et tout premier-né des bêtes.
Da tsakar dare, sai Ubangiji ya karkashe dukan’ya’yan fari a ƙasar Masar, tun daga ɗan farin Fir’auna, wato, magājinsa, har zuwa ɗan fari na ɗan sarƙa da yake kurkuku, har da’ya’yan fari na dabbobi.
30 Et Pharaon se leva la nuit, et tous ses serviteurs et tout son peuple, et il s’éleva un grand cri en Egypte, car il n’était pas de maison dans laquelle ne gésît un mort.
Fir’auna da dukan fadawansa da kuma dukan Masarawa, suka tashi a cikin daren da kuka mai zafi, aka kuma ji kukan a ko’ina a cikin ƙasar Masar, gama ba gidan da ba a yi mutuwa ba.
31 Pharaon ayant donc appelé Moïse et Aaron pendant la nuit, leur dit: Levez-vous, et sortez du milieu de mon peuple, vous et les enfants d’Israël; allez, sacrifiez au Seigneur, comme vous dites.
A cikin daren, Fir’auna ya aika a kira Musa da Haruna ya ce, “Ku tashi, ku da jama’arku, ku fita daga cikin jama’ata. Ku tafi, ku bauta wa Ubangiji yadda kuka ce.
32 Prenez aussi vos brebis et votre gros bétail, comme vous aviez demandé, et vous en allant, bénissez-moi.
Ku kwashi garkunanku na tumaki da na awaki, da na shanu, ku yi tafiyarku kamar yadda kuka ce, amma ku sa mini albarka.”
33 Et les Egyptiens pressaient le peuple de sortir de leur pays promptement, disant; Nous mourrons tous.
Masarawa suka matsa wa Isra’ilawa su fita daga ƙasarsu da sauri. Gama mutanen Masar sun ce, “Ai, za mu mutu duka, in ba su tafi ba!”
34 Le peuple prit donc de la farine pétrie avant qu’elle fût levée, et la liant dans les manteaux, il la mit sur ses épaules.
Sai mutanen suka ɗauki garin da sun kwaɓa ba yisti a ciki, tare da ƙwaryansu na aikin kwaɓan, suka nannaɗe su a mayafansu, suka rataye a kafaɗunsu.
35 Alors les enfants d’Israël firent comme avait ordonné Moïse; et ils demandèrent aux Egyptiens des vases d’argent et d’or et beaucoup de vêtements.
Isra’ilawa kuwa suka yi yadda Musa ya umarce su, suka roƙi Masarawa kayan adonsu na azurfa da na zinariya, da kuma tufafi.
36 Or le Seigneur fit trouver grâce au peuple devant les Egyptiens, pour qu’ils les leur prêtassent; et ils dépouillèrent les Egyptiens.
Ubangiji kuwa ya sa Isra’ilawa suka yi farin jini a wurin Masarawa, Masarawa kuma suka saki hannu wa mutanen, suka ba su duk abin da suka roƙa; ta haka Isra’ilawa suka washe Masarawa.
37 Et les enfants d’Israël partirent de Ramessès pour Socoth, environ six cent mille hommes de pied, sans les petits enfants.
Isra’ilawa suka kama tafiya daga Rameses zuwa Sukkot. Akwai maza dubu ɗari shida da suke tafiya da ƙafa, ban da mata da yara.
38 Mais une foule innombrable de gens de toute espèce monta avec eux, ainsi que des brebis, du gros bétail et des animaux de divers genres en très grand nombre.
Waɗansu mutane da yawa da ba Isra’ilawa ba, suka haura tare da su, da garkunan shanu, da na tumaki da awaki.
39 Ils firent cuire aussi la farine qu’ils avaient apportée d’Egypte déjà toute pétrie, et firent des pains azymes cuits sous la cendre; car il? ne pouvaient fermenter, les Egyptiens les forçant de partir, et ne leur permettant de prendre aucun délai; et ils n’avaient pas eu la facilité d’apprêter aucun aliment.
Suka toya burodi marar yisti da garin da aka kwaɓa wanda suka kawo daga Masar. Garin da aka kwaɓan ba shi da yisti, domin an kore su daga Masar, ba su kuwa sami damar shirya wa kansu abinci ba.
40 Or l’habitation des enfants d’Israël pendant qu’ils demeurèrent en Egypte, fut de quatre cent trente ans.
Zaman da Isra’ilawa suka yi a Masar, ya kai shekara 430.
41 Lesquels accomplis, toute l’armée du Seigneur sortit le même jour de la terre d’Egypte.
A ranar da shekara 430 ɗin nan suka cika, a ran nan ne dukan ɓangare-ɓangare na mutanen Ubangiji suka bar Masar.
42 Cette nuit doit être observée en l’honneur du Seigneur, quand il les retira de la terre d’Egypte, et tous les enfants d’Israël doivent l’observer dans leurs générations.
Gama Ubangiji ya yi tsaro a wannan dare, domin yă fitar da su daga Masar, a wannan dare, dole dukan Isra’ilawa su yi tsaro, don su girmama Ubangiji, cikin dukan tsararraki masu zuwa.
43 Et le Seigneur dit à Moïse et à Aaron: Voici le rite de la Pâque: Aucun étranger n’en mangera.
Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna, “Waɗannan ne ƙa’idodin Bikin Ƙetarewa. “Ba baƙon da zai ci shi.
44 Mais tout esclave acheté sera circoncis, et alors il en mangera.
Duk bawan da kuka sayo, yana iya ci, in dai an yi masa kaciya,
45 L’étranger et le mercenaire n’en mangeront point.
amma wanda ba ya zama tare da ku na ɗinɗinɗin, da kuma wanda aka ɗauki hayansa, ba zai ci ba.
46 C’est dans une même maison qu’on la mangera; et vous ne porterez point de sa chair au dehors, et vous n’en romprez aucun os.
“Dole a ci shi a cikin gida ɗaya; kada a kai naman waje. Kada a karya wani daga ƙasusuwansa.
47 Toute l’assemblée d’Israël la fera.
Dole dukan taron jama’ar Isra’ila su yi bikin.
48 Que si quelqu’un des étrangers veut entrer dans votre colonie et faire la Pâque du Seigneur, tous ses enfants mâles seront circoncis auparavant, et alors il la célébrera selon le rite; et il sera comme un naturel du pays; mais si quelqu’un n’a pas été circoncis, il n’en mangera pas.
“Baƙon da yake zama tare da ku da yake so yă yi Bikin Ƙetarewar Ubangiji, dole yă yi wa dukan mazan da suke cikin gidansa kaciya; sa’an nan ne zai iya yin abubuwa kamar haifaffen ɗan ƙasa.
49 La même loi sera pour l’indigène et pour le colon qui séjournent chez vous.
Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla ta shafi ɗan ƙasa da kuma baƙon da yake zama a tsakaninku.”
50 Et tous les enfants d’Israël firent comme avait ordonné le Seigneur à Moïse et à Aaron.
Dukan Isra’ilawa suka yi na’am da shi, suka yi yadda Ubangiji ya umarci Musa da Haruna.
51 Et le même jour le Seigneur retira les enfants d’Israël de la terre d’Egypte, selon leurs bandes.
A wannan rana, Ubangiji ya fito da Isra’ilawa ɓangare-ɓangare daga Masar.

< Exode 12 >