< Éphésiens 5 >

1 Soyez donc les imitateurs de Dieu, comme enfants bien-aimés;
Saboda haka ku zama masu koyi da Allah, kamar kaunatattun 'ya'yansa.
2 Et marchez dans l’amour, comme le Christ nous a aimés et s’est livré lui-même pour nous en oblation à Dieu, et en hostie de suave odeur.
Ku yi zama cikin kauna kamar yadda Almasihu ya kaunace mu, ya kuma mika kansa sadaka da hadaya ga Allah dominmu, hadaya mai kanshi abin karba ga Allah.
3 Que la fornication et toute impureté, ou l’avarice ne soit pas même nommée parmi vous, comme il convient à des saints.
Fasikanci ko kowacce irin kazamta, ko kazamar lalata kada a ambace su a tsakaninku, don haka ya dace ga masu bi.
4 Point de turpitudes, de folles paroles, de bouffonneries, ce qui ne convient point; mais plutôt des actions de grâces.
Kada a ambaci batsa, maganar wauta ko alfasha wadanda ba su dace ba. Maimakon haka, mu zama masu godiya.
5 Car sachez comprendre qu’aucun fornicateur, ou impudique, ou avare, ce qui est une idolâtrie, n’a d’héritage dans le royaume du Christ et de Dieu.
Domin wannan kun sani cewa ba fasiki, ko mara tsarki, ko mai hadama wato mai bautar gumaka zai sami gado cikin mulkin Almasihu da Allah.
6 Que personne ne vous séduise par de vains discours, car c’est pour ces choses que vient la colère de Dieu sur les fils de la défiance.
Kada kowa ya rude ku da maganganun wofi. Saboda wadannan abubuwa ne fushin Allah ke zuwa kan kangararrun 'ya'ya.
7 N’ayez donc point de commerce avec eux.
Kada ku yi tarayya tare da su.
8 Car autrefois vous étiez ténèbres, mais maintenant vous êtes lumière dans le Seigneur. Marchez comme des enfants de la lumière
Domin da ku duhu ne, amma yanzu ku haske ne cikin Ubangiji. Sai ku yi tafiya kamar 'ya'yan haske.
9 (Or le fruit de la lumière consiste en toute bonté, justice et vérité),
Saboda amfanin haske shine dukan alheri, adalci da gaskiya.
10 Examinant ce qui est agréable à Dieu.
Kuna bidar abin da Ubangiji ke murna da shi.
11 Ne vous associez point aux œuvres infructueuses des ténèbres, mais plutôt réprouvez-les;
Kada ku sa hannu ga ayyuka marasa amfani da ayyukan duhu amma gara a tone su.
12 Car ce qu’ils font en secret est honteux même à dire.
Don abubuwan da suke yi a boye abin kunya ne a bayyana su.
13 Or tout ce qui est répréhensible se découvre par la lumière; car tout ce qui se découvre est lumière.
Dukan abu, idan haske ya bayyana su, za a gan su.
14 C’est pourquoi l’Ecriture dit: Lève-toi, toi qui dors; lève-toi d’entre les morts, et le Christ t’illuminera.
Domin duk abin da aka bayyana ya zama haske. Saboda haka aka ce, “Ka farka, kai mai barci, ka tashi daga cikin matattu; Almasihu kuwa zai haskaka bisanka”.
15 Ayez donc soin, mes frères, de marcher avec circonspection, non comme des insensés,
Saboda haka, ku maida hankali yadda kuke rayuwar ku, ba kamar mutane marasa hikima ba amma kamar masu hikima.
16 Mais comme des hommes sages, rachetant le temps, parce que les jours sont mauvais.
Ku yi lura yadda kuke amfani da lokaci don kwanakin miyagu ne.
17 Ne soyez donc pas imprudents, mais comprenez quelle est la volonté de Dieu;
Kada ku zama wawaye. Maimakon haka, ku fahimci ko menene nufin Ubangiji.
18 Et ne vous enivrez pas de vin qui renferme la luxure; mais soyez remplis de l’Esprit-Saint;
Kuma Kada ku bugu da ruwan inabi, don yana iya lalata rayuwa. Maimakon haka, ku cika da Ruhu Mai Tsarki.
19 Vous entretenant entre vous de psaumes, d’hymnes et de cantiques spirituels, chantant et psalmodiant du fond de vos cœurs à la gloire du Seigneur;
Kuna magana da junanku cikin zabura da wakoki da wakokin ruhaniya, kuna rairawa da yabo da zuciyarku ga Ubangiji.
20 Rendant grâces toujours et pour toutes choses, au nom de Notre Seigneur Jésus-Christ, à Dieu et Père;
Kullum kuna ba da gaskiya domin dukan abubuwa cikin sunan Ubangiji Yesu ga Allah Uba.
21 Soumis les uns aux autres dans la crainte du Christ.
Kuna sarayadda kanku ga juna cikin girmama Almasihu.
22 Que les femmes soient soumises à leurs maris comme au Seigneur;
Mata, ku yi biyayya ga mazan ku kamar ga Ubangiji.
23 Parce que l’homme est le chef de la femme, comme le Christ est le chef de l’Eglise, et il est aussi le Sauveur de son corps.
Domin miji shine shugaban matarsa kamar yadda Almasihu yake shugaban ikilisiya. Shine kuma mai ceton jiki.
24 Comme donc l’Eglise est soumise au Christ, ainsi le soient en toutes choses les femmes à leurs maris.
Amma kamar yadda ikilisiya take biyayya ga Almasihu, haka kuma dole mata suyi ga mazajen su cikin kowanne abu.
25 Maris, aimez vos femmes, comme le Christ a aimé l’Église, et s’est livré lui-même pour elle,
Mazaje, ku kaunaci matanku kamar yadda Almasihu ya kaunaci ikilisiya har ya ba da kansa dominta,
26 Afin de la sanctifier, la purifiant par le baptême d’eau, par la parole de vie,
Ya yi wannan domin ya tsarkake ta. Ya wanke mu da ruwan wanki ta wurin kalma.
27 Pour la faire paraître devant lui une Eglise glorieuse, n’ayant ni tache, ni ride, ni rien de semblable, mais pour qu’elle soit sainte et immaculée.
Ya yi wannan domin ya mika ma kansa ikilisiya mai daraja, ba tare da tabo ko cikas ko wani abu kamar wadannan, amma ta zama da tsarki da kuma mara aibi.
28 Ainsi les maris doivent aimer leurs femmes comme leur propre corps. Celui qui aime sa femme, s’aime lui-même.
Hakannan kuma, mazaje su kaunaci matansu kamar jikunnansu. Wanda yake kaunar matarsa yana kaunar kansa.
29 Car personne n’a jamais haï sa chair, mais il la nourrit et la soigne, comme le Christ l’Eglise;
Ba wanda ya taba kin jikinsa. Amma, yakan ciyadda shi yana kaunarsa, kamar yadda Almasihu ya kaunaci ikilisiya.
30 Parce que nous sommes les membres de son corps, formés de sa chair et de ses os.
Domin mu gabobin jikinsa ne.
31 À cause de cela l’homme laissera son père et sa mère, et s’attachera à sa femme; et ils seront deux dans une seule chair.;
“Domin wannan mutum zai rabu da ubansa da uwarsa ya manne wa matarsa, su biyu su zama nama daya”.
32 Ce sacrement est grand, je dis dans le Christ et dans l’Eglise.
Wannan asirin gaskiyar, da girma yake, amma ina magana ne game da Almasihu da ikilisiyarsa.
33 Que chacun de vous donc aime sa femme comme lui-même; mais que la femme craigne son mari.
Duk da haka, kowannenku dole ya kaunaci matarsa kamar kansa, matar kuma dole ta girmama mijinta.

< Éphésiens 5 >