< Deutéronome 5 >

1 Or, Moïse appela tout Israël et lui dit: Ecoute, Israël, les cérémonies et les ordonnances que moi, je vous fais entendre aujourd’hui; apprenez-les et les accomplissez par vos œuvres.
Musa ya tattara dukan Isra’ila ya ce, Ku ji, ya Isra’ila, ƙa’idodi da dokokin da na furta a kunnuwanku a yau. Ku koye su, ku kuma tabbata kun bi su.
2 Le Seigneur notre Dieu a fait avec nous une alliance à Horeb.
Ubangiji Allahnmu ya yi alkawari da mu a Horeb.
3 Ce n’est pas avec nos pères qu’il a fait cette alliance, mais avec nous qui sommes maintenant et qui vivons.
Ba da kakanninmu ba ne Ubangiji ya yi wannan alkawari, amma da mu ne, da dukanmu waɗanda muke da rai a yau.
4 Il nous a parlé face à face sur la montagne du milieu du feu.
Ubangiji ya yi magana fuska da fuska da ku daga wuta a kan dutse.
5 C’est moi qui fus l’interprète et le médiateur entre le Seigneur et vous en ce temps-là, pour vous annoncer ses paroles; car vous craignîtes le feu, et vous ne montâtes pas sur la montagne, et il dit:
(A wannan lokaci na tsaya tsakanin Ubangiji da ku, don in furta muku maganar Ubangiji, domin kun ji tsoron wutar, ba ku kuwa hau dutsen ba.) Ya ce,
6 Je suis le Seigneur ton Dieu qui t’ai retiré de la terre d’Egypte, de la maison de servitude.
“Ni ne Ubangiji Allahnka, wanda ya fitar da ku daga Masar, daga ƙasar bauta.
7 Tu n’auras point de dieux étrangers en ma présence.
“Ba za ka kasance da waɗansu alloli a gabana ba.
8 Tu ne te feras point d’image taillée au ciseau, ni de représentation de tout ce qui est dans le ciel en haut, et de ce qui est sur la terre en bas, et de ce qui se trouve dans les eaux sous la terre.
Ba za ka yi wa kanka gunki, ko wata siffar abin da take a sama a bisa, ko siffar abin da yake a duniya a ƙasa, ko siffar abin da yake a cikin ruwa a ƙarƙashin ƙasa ba.
9 Tu ne les adoreras pas et tu ne les serviras pas. Car c’est moi qui suis le Seigneur ton Dieu, Dieu jaloux, rejetant l’iniquité des pères sur les enfants jusqu’à la troisième et la quatrième génération de ceux qui me haïssent,
Ba za ka rusuna musu, ko ka yi musu sujada ba. Gama Ni, Ubangiji Allahnka, Allah ne mai kishi, nakan hukunta’ya’ya saboda zunuban iyaye har tsara ta uku da ta huɗu na waɗanda suka ƙi ni.
10 Et faisant miséricorde dans plusieurs milliers de générations, à ceux qui m’aiment et gardent mes préceptes.
Amma nakan nuna ƙauna ga dubban tsararraki na waɗanda suke ƙaunata, suke kuma kiyaye dokokina.
11 Tu ne prendras point le nom du Seigneur ton Dieu en vain: car il ne sera pas impuni, celui qui pour une chose vaine prendra son nom.
Ba za ka yi amfani da sunan Ubangiji Allahnka a banza ba, gama Ubangiji zai ba wa duk mai yin amfani da sunansa a banza laifi.
12 Observe le jour du sabbat, afin de le sanctifier, comme t’a ordonné le Seigneur ton Dieu.
Ka kiyaye ranar Asabbaci ta wurin kiyaye ta da tsarki, yadda Ubangiji Allahnka ya umarce ka.
13 Pendant six jours tu travailleras, et tu feras tous tes ouvrages.
Kwanaki shida za ka yi aiki, ka kuma yi dukan aikinka,
14 Mais le septième jour est celui du sabbat, c’est-à-dire le repos du Seigneur ton Dieu. Tu ne feras en ce jour aucun ouvrage, ni toi, ni ton fils, ni ta fille, ni ton serviteur, ni ta servante, ni ton bœuf, ni ton âne, ni aucune de tes bêtes, ni l’étranger qui est au-dedans de tes portes; afin que ton serviteur et ta servante se reposent comme toi aussi.
amma rana ta bakwai, Asabbaci ne ga Ubangiji Allahnka. A kanta ba za ka yi wani aiki ba, ko kai, ko ɗanka, ko’yarka, ko bawanka, ko baiwarka, ko saniyarka, ko jakinka, ko wani daga dabbobinka, ko baƙo a ƙofofinka, don bayinka maza da mata su ma su huta, kamar ka.
15 Souviens-toi que toi-même aussi tu as servi en Egypte, et que le Seigneur ton Dieu t’en a retiré par une main puissante et un bras étendu. C’est pourquoi il t’a ordonné d’observer le jour du sabbat.
Ka tuna fa, dā kai bawa ne a ƙasar Masar amma Ubangiji Allahnka ya fitar da kai daga can da iko da kuma ƙarfi. Saboda haka Ubangiji Allahnka ya umarce ka ka kiyaye ranar Asabbaci.
16 Honore ton père et ta mère, comme t’a ordonné le Seigneur ton Dieu, afin que tu vives longtemps, et que bien t’arrive dans la terre que le Seigneur ton Dieu va te donner.
Ka ba da girma ga mahaifinka da mahaifiyarka, yadda Ubangiji Allahnka ya umarce ka, don ka yi tsawon rai, ka kuma sami zaman lafiya a ƙasar da Ubangiji Allahnka yake ba ka.
17 Tu ne tueras point.
Kada ka yi kisankai.
18 Tu ne commettras point d’adultère.
Kada ka yi zina.
19 Et tu ne feras point de vol.
Kada ka yi sata.
20 Tu ne porteras point de faux témoignage contre ton prochain.
Kada ka ba da shaidar ƙarya a kan maƙwabcinka.
21 Tu ne convoiteras point la femme de ton prochain, ni sa maison, ni son champ, ni son serviteur, ni sa servante, ni son bœuf, ni son âne, ni aucune des choses qui sont à lui.
Kada ka yi ƙyashin matar maƙwabcinka. Kada kuma ka yi sha’awar gidan maƙwabcinka, ko gonarsa, ko bayinsa maza da mata, ko saniyarka, ko jakinsa, ko dai wani abin da yake na maƙwabtanka.”
22 Ce sont là les paroles qu’a dites le Seigneur à toute votre multitude, sur la montagne, du milieu du feu, de la nuée et de l’obscurité, avec une voix forte, n’ajoutant rien de plus; et il les écrivit sur deux tables de pierre, qu’il me remit.
Waɗannan su ne dokokin da Ubangiji ya furta da babbar murya ga taronku gaba ɗaya, a can dutse ta tsakiyar wuta, girgije da kuma baƙin duhu; bai kuma ƙara kome ba. Sa’an nan ya rubuta su a kan alluna biyu na dutse, ya kuma ba ni su.
23 Mais vous, après que vous eûtes entendu sa voix du milieu des ténèbres et que vous eûtes vu la montagne embrasée, vous vous approchâtes de moi, tous les princes des tribus, et les anciens, et vous dites:
Sa’ad da kuka ji muryar daga duhu, yayinda dutsen yana cin wuta, dukan manyan kabilanku da dattawanku suka zo wurina.
24 Voilà que le Seigneur notre Dieu nous a montré sa majesté et sa grandeur; nous avons entendu sa voix du milieu du feu, et nous avons éprouvé aujourd’hui, que Dieu ayant parlé avec l’homme, l’homme conserve la vie.
Kuka kuma ce, “Ubangiji Allahnmu ya nuna mana ɗaukakarsa da zatinsa, mun kuma ji muryarsa a tsakiyar wutar. A yau mun ga cewa mutum zai iya rayu idan ma Allah ya yi magana da shi.
25 Pourquoi donc mourrons nous, et ce très grand feu nous dévorera-t-il? Car si nous entendons encore la voix du Seigneur notre Dieu, nous mourrons.
Amma yanzu, don me za mu mutu? Wannan wuta mai girma za tă cinye mu, za mu kuwa mutu in muka ci gaba da jin muryar Ubangiji Allahnmu.
26 Qu’est toute chair, pour qu’elle entende la voix du Dieu vivant, qui parle du milieu du feu, comme nous avons entendu, et qu’elle puisse vivre?
Gama wanda ɗan adam ne ya taɓa jin muryar Allah mai rai yana magana daga wuta, kamar yadda muka ji, ya kuma tsira?
27 Approche plutôt, toi, et écoute tout ce que te dira le Seigneur notre Dieu; tu nous le rapporteras ensuite, et, l’ayant entendu, nous le ferons.
Kai, ka matsa kusa, ka saurara ga dukan abin da Ubangiji Allahnmu ya faɗa. Sa’an nan ka faɗa mana dukan abin da Ubangiji Allahnmu ya faɗa maka. Za mu saurara, mu kuma yi biyayya.”
28 Ce qu’ayant entendu le Seigneur, il me dit: J’ai entendu la voix des paroles de ce peuple, lorsqu’ils t’ont parlé: ils ont bien dit toutes ces choses.
Ubangiji ya ji ku, sa’ad da kuka yi magana da ni, sai Ubangiji ya ce mini, “Na ji abin da wannan mutane suka faɗa maka. Abin da suka faɗa daidai ne.
29 Qui leur donnera d’avoir un esprit tel, qu’ils me craignent, et qu’ils gardent tous mes commandements en tout temps, afin que bien leur arrive, à eux et à leurs enfants pour jamais.
Kash, da a ce zukatansu za su zama masu tsorona, su kuma kiyaye dukan dokokina kullum mana, saboda kome yă zama da lafiya gare su, da kuma’ya’yansu har abada!
30 Va, et dis-leur: Retournez en vos tentes.
“Je, ka faɗa musu su koma tentunansu.
31 Mais toi, demeure ici avec moi, et je te dirai tous mes commandements, les cérémonies et les ordonnances, que tu leur enseigneras, afin qu’ils les pratiquent dans la terre que je leur donnerai en possession.
Kai kuwa ka tsaya a nan tare da ni saboda in ba ka umarnai, ƙa’idodi da kuma dokoki duka, da za ka koya musu don su bi a ƙasar da nake ba su, su mallaka.”
32 Gardez donc et faites ce que vous a ordonné le Seigneur votre Dieu; vous ne vous détournerez ni à droite ni à gauche;
Sai ku yi hankali don ku yi abin da Ubangiji Allahnku ya umarce ku; kada ku juya dama ko hagu.
33 Mais c’est par la voie qu’a prescrite le Seigneur votre Dieu que vous marcherez, afin que vous viviez et que bien vous arrive, et que vos jours soient prolongés dans la terre de votre possession.
Ku yi tafiya cikin dukan hanyar da Ubangiji Allahnku ya umarce ku, saboda ku zauna, ku yi nasara, ku kuma yi tsawon rai a ƙasar da za ku mallaka.

< Deutéronome 5 >