< Deutéronome 33 >
1 Voici la bénédiction dont Moïse, homme de Dieu, bénit les enfants d’Israël avant sa mort.
Wannan ita ce albarkar da Musa mutumin Allah ya furta a kan Isra’ilawa, kafin yă rasu.
2 Il dit donc: Le Seigneur est venu de Sinaï, et il s’est levé pour nous de Séir; il a apparu de la montagne de Pharan, et avec lui des milliers de saints. En sa main droite était une loi de feu.
Ya ce, “Ubangiji ya zo daga Sinai ya haskaka a bisansu daga Seyir; ya haskaka daga Dutsen Faran. Ya zo tare da dubban tsarkakansa daga kudu, daga gangara dutsensa.
3 Il a aimé des peuples; tous les saints sont dans sa main; et ceux qui s’approchent de ses pieds recevront de sa doctrine.
Tabbatacce kai ne wanda yake ƙaunar mutane; dukan tsarkaka suna a hannunka. A ƙafafunka, duk suka rusuna, daga wurinka kuma suka karɓi umarni,
4 Moïse nous a prescrit une loi, héritage de la multitude de Jacob.
dokar Musa ta ba mu dokoki, mallakar taron Yaƙub.
5 Il sera roi chez le peuple très juste, les princes du peuple étant assemblés avec les tribus d’Israël.
Shi ne sarki a bisa Yeshurun sa’ad da shugabannin mutane suka taru, tare da kabilan Isra’ila.
6 Que Ruben vive, et qu’il ne meure pas, mais qu’il soit en petit nombre.
“Bari Ruben yă rayu, kada yă mutu, kada mutanensa su zama kaɗan.”
7 Voici la bénédiction de Juda: Ecoutez, Seigneur, la voix de Juda et introduisez-le auprès de son peuple; ses mains combattront pour lui, et il sera son aide contre ses adversaires.
Ya kuma faɗa wannan game da Yahuda, “Ka ji, ya Ubangiji, kukan Yahuda; ka kawo shi wurin mutanensa. Da hannuwansa ya kāre kansa. Ka taimake shi a kan maƙiyansa!”
8 À Lévi aussi il dit: Seigneur, votre perfection et votre doctrine sont à l’homme, votre saint, que vous avez éprouvé par une tentation, et jugé aux Eaux de contradiction;
Game da Lawi ya ce, “Tummim da Urim na mutumin da ka nuna masa tagomashi ne. Ka gwada shi a Massa; ka yi faɗa da shi a ruwan Meriba.
9 Qui a dit à son père et à sa mère: Je ne vous connais pas; et à ses frères: Je ne sais qui vous êtes; et ils n’ont pas connu leurs enfants. Ceux-là ont gardé votre parole, et ont observé votre alliance,
Ya yi zancen mahaifinsa da mahaifiyarsa ya ce, ‘Ban kula da su ba.’ Bai gane da’yan’uwansa ba, ko yă yarda da’ya’yansa, amma ya kiyaye maganarka ya tsare alkawarinka.
10 Vos ordonnances, ô Jacob! et votre loi, ô Israël. Ils offriront de l’encens dans votre fureur, et un holocauste sur votre autel.
Ya koyar da farillanka ga Yaƙub, dokarka kuma ga Isra’ila. Ya miƙa turare a gabanka da kuma hadaya ta ƙonawa ɗungum a kan bagadenka.
11 Bénissez, Seigneur, sa force, et recevez les œuvres de ses mains. Frappez le dos de ses ennemis, et que ceux qui le haïssent ne se relèvent point.
Ka albarkaci ɗaukan dabarunsa, ya Ubangiji, ka kuma ji daɗin aikin hannuwansa. Ka murƙushe kwankwaso waɗanda suka tayar masa; ka bugi abokan gābansa har sai ba su ƙara tashi ba.”
12 Et à Benjamin il dit: Le bien-aimé du Seigneur habitera avec confiance en lui; il demeurera tout le jour comme dans une chambre nuptiale, et il se reposera entre ses bras.
Game da Benyamin ya ce, “Bari ƙaunataccen Ubangiji yă zauna lafiya kusa da shi, gama yana tsare shi dukan yini, wanda kuma Ubangiji yake ƙauna yana zama a tsakanin kafaɗunsa.”
13 À Joseph aussi il dit: Que la terre de Joseph soit remplie de la bénédiction du Seigneur, des fruits du ciel, de la rosée, et de l’abîme qui est en bas;
Game da Yusuf ya ce, “Bari Ubangiji yă albarkaci ƙasarsa da raɓa mai daraja daga sama a bisa da kuma zurfin ruwan da suke kwance a ƙarƙashi;
14 De toutes les sortes de fruits que mûrissent le soleil et la lune;
da abubuwa masu kyau da rana take kawo, da kuma abubuwa mafi kyau da wata zai iya haifar;
15 Des fruits du sommet des montagnes antiques et de ceux des collines éternelles,
da zaɓaɓɓun kyautai na daɗaɗɗun duwatsu, da kyawawan amfani na madawwaman tuddai.
16 De tous les grains de la terre et de son abondance. Que la bénédiction de celui qui a apparu dans un buisson vienne sur la tête de Joseph, et sur la tête de celui qui est nazaréen entre ses frères.
Tare da kyautai mafi kyau na duniya da cikarta, da tagomashi na wanda yake zama a ƙaramin itace mai ƙonewa. Bari duk waɗannan su zauna a kan Yusuf, a goshin sarki a cikin’yan’uwansa.
17 Sa beauté est comme celle du premier-né d’un taureau; les cornes du rhinocéros sont ses cornes; avec elles il fera sauter en l’air des nations jusqu’aux extrémités de la terre. Telle seront les troupes nombreuses d’Ephraïm, et tels les milliers de Manassé,
Cikin daraja yana yi kamar ɗan fari na bijimi; ƙahoninsa ƙahonin ɓauna ne. Tare da su zai tukwiyi al’ummai, har ma da waɗanda suke ƙarshen duniya. Haka dubu dubban Efraim suke; haka dubban Manasse suke.”
18 Et à Zabulon il dit: Réjouis-toi, Zabulon, dans ta sortie, et, Issachar, dans tes tabernacles.
Game da Zebulun ya ce, “Ka yi farin ciki, Zebulun, a fitowarka, kai kuma Issakar, a cikin tentunanka.
19 Ils appelleront des peuples sur la montagne; là, ils immoleront des victimes de justice. Ils suceront comme le lait les eaux débordantes de la mer, et les trésors cachés dans les sables.
Za su kira mutane zuwa dutse, a can za su miƙa hadayun adalci; za su yi biki a yalwan tekuna, a dukiyoyin da aka ɓoye a cikin yashi.”
20 Et à Gad il dit: Béni Gad dans son étendue! il s’est reposé comme un lion, puis il a saisi un bras et une tête.
Game da Gad ya ce, “Mai albarka ne wanda ya fadada mazaunin Gad! Gad yana zama a can kamar zaki, yana yayyage a hannu da kai.
21 Et il a vu sa primauté, qui est que dans son partage était placé un docteur: et il a été avec les princes d’un peuple, et il a exécuté les justices du Seigneur et son jugement avec Israël.
Ya zaɓi ƙasa mafi kyau wa kansa; aka ajiye masa rabon shugaba. Sa’ad da shugabannin mutane suka taru, ya aikata adalcin Ubangiji da kuma hukuncinsa game da Isra’ila.”
22 À Dan aussi il dit: Dan est le petit d’un lion, il se répandra de Basan au loin.
Game da Dan ya ce, “Dan ɗan zaki ne, yana tsalle daga Bashan.”
23 Et à Nephtali il dit: Nephtali jouira de l’abondance et il sera rempli des bénédictions du Seigneur; il possédera la mer et le midi.
Game da Naftali ya ce, “Naftali ƙosasshe ne da tagomashin Ubangiji, ya kuma cika albarkarsa; zai gāji gefen kudu zuwa tafki.”
24 À Aser aussi il dit: Béni Aser entre les fils d’Israël! qu’il soit agréable à ses frères, et qu’il trempe son pied dans l’huile.
Game da Asher ya ce, “Mafi albarka na’ya’yan, shi ne Asher; bari yă sami tagomashi daga’yan’uwansa, bari kuma yă wanke ƙafafunsa a cikin mai.
25 Le fer et l’airain seront sa chaussure. Ta vieillesse sera comme les jours de ta jeunesse.
Madogaran ƙofofinka za su zama ƙarfe da tagulla, ƙarfinka kuma zai zama daidai da kwanakinka.
26 Il n’est pas un autre Dieu comme le Dieu du peuple très juste; celui qui monte sur le ciel est ton aide. Par sa magnificence les nuées courent de toutes parts;
“Babu wani kamar Allah na Yeshurun, wanda yake hawa a bisa sammai don yă taimake ka a kan gizagizai kuma a cikin darajarsa.
27 Son habitacle est en haut; et au-dessous sont ses bras éternels; il chassera de ta face l’ennemi, et il dira: Sois brisé.
Allah madawwami shi ne mafakarka, a ƙarƙashina kuma madawwamin hannuwa ne. Zai kore abokin gābanka a gabanka, yana cewa, ‘Ka hallaka shi!’
28 Israël habitera avec assurance et seul. L’œil de Jacob sera fixé sur une terre de vin et de blé, et les cieux seront obscurcis par la rosée.
Haka Isra’ila zai zauna lafiya shi kaɗai; zuriyar Yaƙub a tsare a ƙasar hatsi da sabon ruwan inabi, inda sammai za su zuba raɓa.
29 Tu es heureux, Israël: qui est semblable à toi, peuple, qui es sauvé dans le Seigneur? il est le bouclier de ta défense, et le glaive de ta gloire; tes ennemis te renieront, et tu fouleras aux pieds leurs cous.
Kai mai albarka ne, ya Isra’ila! Wane ne yake kamar ka, mutanen da Ubangiji ya ceta? Shi ne mafakarka da mai taimakonka da kuma takobinka mai ɗaukaka. Abokan gābanka za su zo neman jinƙai a gabanka, za ka kuwa tattake masujadansu.”