< Deutéronome 25 >

1 S’il survient un débat entre quelques hommes, et qu’ils en appellent aux juges, celui qu’ils reconnaîtront pour juste, ils lui donneront la palme de la justice, et celui qu’ils reconnaîtront pour impie, ils le condamneront d’impiété.
Idan mūsu ya tashi tsakanin mutum biyu har abin ya kai su kotu, alƙalai kuwa suka yanke hukunci a kan batun, suka kuɓutar da marar laifi sa’an nan suka hukunta mai laifi,
2 Que s’ils jugent celui qui a péché, digne de coups, ils le renverseront, et le feront battre devant eux. C’est selon la mesure du péché, que sera la mesure des coups;
in mai laifin ya cancanci bulala, alƙali zai sa yă kwanta a yi masa bulala a gabansa da yawan bulalan da ya dace da laifin,
3 En sorte seulement, qu’elle n’excède pas le nombre de quarante, de peur que ton frère ne s’en aille ayant été horriblement déchiré devant tes yeux.
amma kada yă yi masa bulala fiye da arba’in. In ya yi masa fiye da haka, za a ƙasƙantar da ɗan’uwanku, zai kuma zama rainanne a idonku.
4 Tu ne lieras point la bouche d’un bœuf qui foule tes grains dans l’aire.
Kada ku yi wa saniya takunkumi sa’ad da take tattaka hatsi.
5 Quand deux frères habitent ensemble, et que l’un d’eux meurt sans enfants, que la femme du défunt n’en épouse point un autre; mais le frère de son mari la prendra, et il suscitera des enfants à son frère;
In’yan’uwa suna zama tare, in ɗayansu ya mutu babu ɗa, kada gwauruwar tă yi aure waje da iyalin. Ɗan’uwan mijinta zai ɗauke ta, yă aure ta, yă kuma cika abin da yă kamaci ɗan’uwan miji yă yi.
6 Et il appellera le fils premier-né d’elle du nom de son frère, afin que le nom de son frère ne soit pas effacé d’Israël.
Ɗan farin da ta haifa zai ɗauki sunan ɗan’uwan da ya rasu saboda kada sunansa yă ɓace daga Isra’ila.
7 Mais s’il ne veut pas prendre la femme de son frère qui lui est due en vertu de la loi, cette femme ira à la porte de la ville, elle s’adressera aux anciens et dira: Le frère de mon mari ne veut pas ressusciter le nom de son frère en Israël, ni me prendre pour femme.
Amma fa, in mutum ba ya so yă auri matar ɗan’uwansa, sai tă tafi wurin dattawa a ƙofar gari tă ce, “Ɗan’uwan mijina ya ƙi yă wanzar da sunan ɗan’uwansa a Isra’ila. Ya ƙi yă cika abin da ya kamaci ɗan’uwan miji yă yi gare ni.”
8 Et aussitôt ils le feront appeler, et ils l’interrogeront. S’il répond: Je ne veux pas la prendre pour femme,
Sai dattawan garinsa su kira shi, su kuma yi masa magana. In ya nace yana cewa, “Ba na so in aure ta,”
9 La femme s’approchera de lui devant les anciens, et lui ôtera la chaussure de son pied, elle crachera sur sa face, et dira: C’est ainsi qu’il sera fait à l’homme qui n’édifie pas la maison de son frère.
sai gwauruwan nan, matar ɗan’uwansa tă haura wurinsa a gaban dattawa, tă tuɓe takalminsa guda, ta tofa masa miyau a fuska, tă ce, “Haka za a yi ga mutumin da zai ƙi kafa gidan ɗan’uwansa.”
10 Et il sera appelé en Israël du nom de Maison du déchaussé.
Za a kira zuriyarsa a Isra’ila Iyalin da aka tuɓe masa takalmi.
11 Si deux hommes ont une dispute entre eux, et que l’un commence à quereller l’autre, et que la femme de l’un voulant arracher son mari de la main du plus fort, étende la main et saisisse ses parties secrètes,
In mutane biyu suna faɗa, sai matar mutum ɗaya daga cikinsu ta zo don tă kuɓutar da mijinta daga abokin faɗarsa, ta kuma miƙa hannu ta kama marainan wancan,
12 Tu couperas sa main, et tu ne te laisseras fléchir par aucune compassion pour elle.
sai ku yanke hannunta. Kada ku ji tausayinta.
13 Tu n’auras point dans ton sachet deux poids, l’un plus gros et l’autre plus petit;
Kada ku kasance da ma’auni iri biyu a jakarku, ɗaya babba, ɗaya ƙarami.
14 Et il n’y aura point dans ta maison un boisseau plus grand et un plus petit.
Kada ku kasance da mudu iri biyu a jakarku, ɗaya babba, ɗaya ƙarami.
15 Tu auras un poids juste et véritable, et il y aura chez toi un boisseau égal et véritable, afin que tu vives longtemps sur la terre que le Seigneur ton Dieu t’aura donnée;
Dole ku kasance da ma’aunin da kuma mudun da yake daidai, kuma na gaskiya, saboda ku yi tsawon rai a ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku.
16 Car le Seigneur ton Dieu a en abomination celui qui fait ces choses, et il déteste toute injustice.
Gama Ubangiji Allahnku yana ƙyamar duk mai yi waɗannan abubuwa, da kuma mai rashin gaskiya.
17 Souviens-toi de ce que t’a fait Amalec dans le chemin, quand tu sortais de l’Egypte.
Ku tuna da abin da Amalekawa suka yi muku a hanya, sa’ad da kuka fito Masar.
18 Comment il marcha contre toi, et tailla en pièces les derniers de ton armée, qui, fatigués, s’étaient arrêtés, quand toi-même tu étais épuisé de faim et de fatigue, et il ne craignit pas Dieu.
Yadda suka yi muku kwanto a hanya, suka fāɗa muku ta baya, suka karkashe waɗanda suka gaji tiɓis. Ba su ko ji tsoron Allah ba.
19 Lors donc que le Seigneur ton Dieu t’aura donné le repos, et qu’il t’aura assujetti toutes les nations d’alentour, dans la terre qu’il t’a promise, tu effaceras son nom de dessous le ciel. Prends garde que tu ne l’oublies.
Sa’ad da Ubangiji Allahnku ya ba ku hutu daga dukan abokan gābanku kewaye da ku, a ƙasar da yake ba ku ku mallaka a matsayin gādo, sai ku shafe Amalekawa daga duniya, don kada a ƙara tunawa da su. Kada fa ku manta!

< Deutéronome 25 >