< Deutéronome 23 >

1 Un eunuque dont les parties génératrices auront été froissées, ou amputées, ou arrachées, n’entrera point dans l’assemblée du Seigneur.
Duk wanda aka daƙe, ko yanke gabansa, ba zai shiga taron jama’ar Ubangiji ba.
2 Un bâtard, c’est-à-dire, un homme né d’une prostituée, n’entrera point dans l’assemblée du Seigneur, jusqu’à la dixième génération.
Duk wanda aka haifa ta wurin cikin shege, har tsara ta goma, zuriyarsa ba za su shiga taron jama’ar Ubangiji ba, har zuwa tsara ta goma.
3 L’Ammonite et le Moabite n’entreront point dans l’assemblée du Seigneur, même après la dixième génération, à jamais,
Ba mutumin Ammon, ko mutumin Mowab, ko kuwa wani zuriyarsu da zai shiga taron jama’ar Ubangiji, har tsara ta goma.
4 Parce qu’ils n’ont pas voulu venir au-devant de vous avec le pain et l’eau, dans le chemin, lorsque vous êtes sortis de l’Egypte; et parce qu’ils ont gagné contre toi Balaam, fils de Béor, de la Mésopotamie de Syrie, afin qu’il te maudît;
Gama ba su zo sun tarye ku da burodi da ruwa a hanyarku, sa’ad da kuka fito daga Masar ba, sai ma suka yi haya Bala’am ɗan Beyor daga Fetor a Aram-Naharayim yă furta la’ana a kanku.
5 Mais le Seigneur ton Dieu ne voulut point écouter Balaam, et il changea sa malédiction en bénédiction pour toi, parce qu’il t’aimait.
Amma Ubangiji Allahnku bai saurari Bala’am ba, sai ya mai da la’anar ta koma albarka gare ku, domin Ubangiji Allahnku yana ƙaunarku.
6 Tu ne feras point de paix avec eux, et tu ne rechercheras aucun bien pour eux durant tous les jours de ta vie, à jamais.
Kada ku yi yarjejjeniyar abuta da su, muddin kuna da rai.
7 Tu n’auras point l’Iduméen en abomination, parce qu’il est ton frère; ni l’Egyptien, parce que tu as été étranger dans sa terre.
Kada ku yi ƙyamar mutumin Edom, gama mutumin Edom ɗan’uwanku ne. Kada ku yi ƙyamar mutumin Masar, domin kun yi zama baƙunta a ƙasarsa.
8 Ceux qui seront nés d’eux, à la troisième génération, entreront dans l’assemblée du Seigneur.
’Ya’yan da aka haifa musu na tsara ta uku za su iya shiga taron jama’ar Ubangiji.
9 Quand tu sortiras contre tes ennemis pour un combat, tu te garderas de toute chose mauvaise.
Sa’ad da kuka yi sansani don ku yi yaƙi da abokan gābanku, ku kiyaye kanku daga duk wani abu marar tsabta.
10 S’il se trouve parmi vous un homme qui a été souillé dans un songe nocturne, il sortira hors du camp,
In ɗaya daga cikin mazanku ya ƙazantu saboda zubar da maniyyi, sai yă fita daga sansani yă zauna waje da sansani.
11 Et il n’y reviendra point, avant qu’il ne se soit lavé vers le soir, dans l’eau; et après le coucher du soleil, il reviendra dans le camp.
Amma yayinda yamma ke gabatowa sai yă wanke kansa, da fāɗuwar rana kuwa sai yă koma cikin sansani.
12 Tu auras un lieu hors du camp, où tu iras pour les besoins de la nature,
Ku keɓe wuri waje da sansani inda za ku iya zuwa don yin bayan gari.
13 Portant un pieu à la ceinture; et lorsque tu voudras l’asseoir, tu feras un trou en rond, et tu couvriras de terre ce qui est sorti de toi,
Sai ku ɗauki wani abin tona ƙasa, sa’ad da kuka yi bayan gari, sai ku tona rami, ku rufe bayan garinku.
14 Après que tu te seras relevé de là (car le Seigneur ton Dieu marche au milieu de ton camp, pour te délivrer, et te livrer tes ennemis); ainsi, que ton camp soit saint, et qu’il n’y paraisse aucune saleté, de peur qu’il ne t’abandonne.
Gama Ubangiji Allahnku yana zagawa a cikin sansaninku don yă tsare ku, yă kuma bashe abokan gābanku gare ku. Dole sansaninku yă kasance da tsarki, saboda kada yă ga wani abu marar kyau a cikinku, har yă juya daga gare ku.
15 Tu ne livreras point à son maître l’esclave qui se sera réfugié près de toi;
In bawa ya tsere zuwa wurinku don mafaka, kada ku miƙa shi ga ubangidansa.
16 Il habitera avec toi dans le lieu qui lui plaira, et il se reposera dans une de tes villes; ne le contriste pas.
Ku bar shi yă zauna a cikinku a duk inda yake so, da kuma a kowane garin da ya zaɓa. Kada ku tsananta masa.
17 Il n’y aura point de femme publique d’entre les filles d’Israël, ni de prostitué d’entre les enfants d’Israël.
Kada mutumin Isra’ila ko mutuniyar Isra’ila yă zama karuwar haikali.
18 Tu n’offriras point la récompense de la prostitution, ni le prix d’un chien, dans la maison du Seigneur ton Dieu, quoi que ce soit que tu aies voué, parce que l’un et l’autre est une abomination auprès du Seigneur ton Dieu.
Kada ku kawo kuɗin a cikin gida Ubangiji Allahnku da aka samu ta wurin karuwanci wanda mace ko namiji ya yi don biyan wani alkawari, domin Ubangiji Allahnku yana ƙyamar su duka.
19 Tu ne prêteras à usure à ton frère, ni argent, ni grains, ni quelque autre chose que ce soit;
Kada ku nemi ɗan’uwanku yă biya bashin da kuka ba shi da ruwa, ko kuɗi, ko abinci, ko kowane irin abin da yana iya ba da ruwa.
20 Mais à l’étranger. Quant à ton frère, ce sera sans usure, que tu lui prêteras ce dont il aura besoin, afin que le Seigneur ton Dieu te bénisse en toutes tes œuvres, dans la terre dans laquelle tu entreras pour la posséder.
Za ku iya nemi ruwa a bashin da kuka ba baƙo, amma ba ɗan’uwanku mutumin Isra’ila ba, domin Ubangiji Allahnku yă sa muku albarka a kowane abin da kuka sa hannunku a kai, a ƙasar da kuke shiga ku ci gādonta.
21 Lorsque tu auras voué un vœu au Seigneur ton Dieu, tu ne tarderas point à l’acquitter, parce que le Seigneur ton Dieu te le redemandera; et si tu diffères il te sera imputé à péché.
In fa kuka yi alkawari ga Ubangiji Allahnku, to, kada ku yi jinkirin cikawa, gama tabbatacce Ubangiji Allahnku zai neme shi daga gare ku, za ku kuma zama masu laifin zunubi.
22 Si tu ne veux point promettre, tu seras sans péché.
Amma in ba ku yi alkawari ba, ba kuwa zai zama muku zunubi ba.
23 Mais ce qui une fois est sorti de tes lèvres, tu l’observeras, et tu feras comme tu as promis au Seigneur ton Dieu; car tu as parlé par ta propre volonté et par ta bouche.
Duk abin da ya fita daga bakinku, sai ku lura ku cika shi, kamar yadda kuka yarda da kanku, kuka yi alkawarin ga Ubangiji Allahnku da bakinku.
24 Entré dans la vigne de ton prochain, mange des raisins autant qu’il te plaira; mais n’en emporte point dehors avec toi.
In kun shiga gonar inabin maƙwabcinku, za ku iya cin inabin da kuke so, amma kada ku sa wani a kwandonku.
25 Si tu entres dans les blés de ton ami, tu cueilleras des épis et tu les broieras avec la main; mais tu n’en couperas pas avec la faux.
In kun shiga gonar hatsin maƙwabcinku, za ku iya murmure tsabar da hannuwanku, amma kada ku sa lauje ku yanka hatsinsa da yake tsaye.

< Deutéronome 23 >