< Deutéronome 17 >
1 Tu n’immoleras pas au Seigneur ton Dieu une brebis, ni un bœuf dans lequel est une tache, ou quelque défaut, parce que c’est une abomination pour le Seigneur ton Dieu.
Kada ku miƙa wa Ubangiji Allahnku, saniya ko tunkiyar da take da wani lahani, ko naƙasa a cikinta, gama wannan zai zama abar ƙyama gare shi.
2 Lorsqu’on aura trouvé chez toi, au dedans d’une de tes portes que le Seigneur ton Dieu te donnera, un homme ou une femme, qui font le mal en la présence du Seigneur ton Dieu, et qui transgressent son alliance,
In an sami wani namiji ko ta mace mai zama a cikinku, a ɗaya daga biranen da Ubangiji ya ba ku yana aikata abin da yake mugu a gaban Ubangiji Allahnku ta wurin karya alkawarinsa,
3 De manière à ce qu’ils aillent, et servent des dieux étrangers et les adorent: le soleil, la lune et toute la milice du ciel, choses que je n’ai point ordonnées.
wanda ya saba wa umarnina, har ya yi sujada ga waɗansu alloli, yana rusuna musu, ko ga rana, ko ga wata, ko kuwa ga taurarin sama,
4 Et lorsque cela t’aura été annoncé, et que l’ayant appris tu t’en seras informé exactement, et que tu auras trouvé que la chose est vraie, et que cette abomination a été faite en Israël,
in kuwa aka faɗa muku wannan, to, dole a bincika sosai. In kuwa gaskiya ne, aka kuma tabbatar cewa wannan abin ƙyama ya faru a cikin Isra’ila,
5 Tu amèneras l’homme et la femme qui ont fait cette chose très criminelle, aux portes de ta ville, et ils seront lapidés.
sai a ɗauki namijin, ko ta mace wanda ya aikata wannan mugun abu zuwa ƙofar birni, a jajjefe wannan mutum sai ya mutu.
6 C’est sur la parole de deux ou trois témoins que périra celui qui sera mis à mort. Que nul ne soit tué, un seul homme rendant témoignage contre lui.
Bisa ga shaidar mutum biyu ko uku, za a iya kashe mutum, amma ba za a iya kashe mutum bisa ga shaida mutum guda ba.
7 La main des témoins le tuera la première, et la main du reste du peuple se lèvera la dernière, afin que tu ôtes le mal d’au milieu de toi.
Hannuwan shaidun ne za su zama na farko a kisan wanda ake zargin, sa’an nan hannuwan dukan mutane. Dole ku fid da mugu daga cikinku.
8 Si tu aperçois qu’un jugement que tu as à porter entre sang et sang, cause et cause, lèpre et lèpre, est difficile et douteux, et que tu voies à tes portes que les avis des juges sont partagés, lève-toi, et monte au lieu qu’aura choisi le Seigneur ton Dieu.
In aka kawo ƙarar da yake da wuya sosai ga alƙali a kotunanku, ko wadda aka zub da jini ne, ko ta faɗa ce, ko kuwa ta wadda aka ci mutunci ce, ku kai su wurin da Ubangiji Allahnku zai zaɓa.
9 Et tu viendras vers les prêtres de la race Lévitique, et vers le juge qu’il y aura en ce temps-là; tu les interrogeras, et ils te découvriront la vérité du jugement.
Ku je wurin firistoci, waɗanda suke Lawiyawa, ga kuma alƙalin wanda yake mulki a lokacin. Ku bincika daga gare su, za su kuwa ba da hukunci.
10 Or, tu feras tout ce qu’auront dit ceux qui président au lieu qu’aura choisi le Seigneur, et ce qu’ils t’auront enseigné,
Dole ku aikata hukuncin da suka yi a wurin da Ubangiji zai zaɓa. Ku lura fa, ku aikata kome da suka faɗa muku.
11 Selon sa loi; et tu suivras leur avis, et tu ne te détourneras point à droite ni à gauche.
Ku yi bisa ga dokar da suka koyar muku da kuma hukuncin da suka yi muku. Kada ku juya daga abin da suka faɗa muku, ko zuwa dama, ko zuwa hagu.
12 Mais celui qui s’enorgueillira, ne voulant pas obéir au commandement du prêtre qui, en ce temps-là, sera ministre du Seigneur ton Dieu, ni à l’arrêt du juge, cet homme-là mourra, et tu ôteras le mal d’Israël;
Duk mutumin da ya yi rashin hankali wa alƙali, ko ga firist wanda yake aiki a nan wa Ubangiji Allahnku, dole a kashe shi. Dole ku fid da mugu daga Isra’ila.
13 Et tout le peuple entendant craindra, en sorte que nul désormais ne s’enflera d’orgueil.
Dukan mutane kuwa za su ji, su kuma ji tsoro, ba kuwa za su ƙara yin rashin hankali kuma ba.
14 Lorsque tu seras entré dans la terre que le Seigneur ton Dieu te donnera, que tu la posséderas, que tu habiteras en elle, et que tu diras: J’établirai sur moi un roi, comme en ont toutes les nations d’alentour;
Sa’ad da kuka shiga ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku, kuka mallake ta, kuka kuma zauna a cikinta, sai kuka ce, “Bari mu naɗa sarki a kanmu kamar sauran al’umman da suke kewaye da mu,”
15 Tu établiras celui que le Seigneur ton Dieu aura choisi du nombre de tes frères. Tu ne pourras faire roi un homme d’une autre nation, et qui ne soit pas ton frère.
ku tabbata kun naɗa sarki a kanku wanda Ubangiji Allahnku ya zaɓa ne. Dole yă zama daga cikin’yan’uwanku. Kada ku sa baƙo a kanku, wanda ba mutumin Isra’ila ɗan’uwanku ba.
16 Et lorsqu’il aura été établi, il ne multipliera point pour lui des chevaux, et il ne ramènera point le peuple en Egypte, soutenu par une nombreuse cavalerie, surtout puisque le Seigneur vous a commandé de ne jamais plus retourner par la même voie.
Sarkin, ba zai nemi dawakai da yawa wa kansa ba, ko yă sa mutane su koma Masar don su sami ƙarin dawakai ba, gama Ubangiji ya faɗa muku, “Ba za ku ƙara koma wancan hanya kuma ba.”
17 Il n’aura pas un grand nombre de femmes qui entraînent son esprit, ni une immense quantité d’argent et d’or.
Sarkin ba zai auri mata masu yawa ba, in ba haka ba zuciyarsa za tă karkata. Ba zai tara azurfa da zinariya da yawa ba.
18 Après qu’il se sera assis sur le trône de son royaume, il écrira pour lui le Deutéronome de cette loi dans un livre, recevant une copie des prêtres de la tribu Lévitique;
Sa’ad da ya hau kursiyin mulkinsa, sai yă rubuta wa kansa a littafin kofin wannan doka da aka ɗauka daga na firistoci, waɗanda suke Lawiyawa.
19 Et il l’aura avec lui, et il le lira tous les jours de sa vie, afin d’apprendre à craindre le Seigneur son Dieu et à garder ses paroles et ses cérémonies, qui sont prescrites dans la loi.
Zai kasance tare da shi, zai kuma karanta shi dukan kwanakin ransa, saboda yă koyi girmama Ubangiji Allahnsa, yă kuma bi dukan kalmomin wannan doka da kuma waɗannan ƙa’idodi a hankali
20 Que son cœur ne s’élève point par l’orgueil au-dessus de ses frères, et qu’il ne se détourne point vers le côté droit ou le gauche, afin qu’il règne longtemps, lui-même et ses fils, sur Israël.
don kada yă ɗauki kansa ya fi’yan’uwansa, yă kuma juya daga dokar zuwa dama, ko zuwa hagu. Sa’an nan shi da kuma zuriyarsa za su daɗe suna mulki a Isra’ila.