< Deutéronome 14 >

1 Soyez les enfants du Seigneur votre Dieu: vous ne vous ferez point d’incisions; et vous ne couperez point vos cheveux à cause d’un mort,
Ku’ya’yan Ubangiji Allahnku ne. Kada ku yi wa kanku zāne, ko ku yi wa kanku aski irin da akan bar sanƙo, saboda wanda ya mutu,
2 Parce que tu es un peuple consacré au Seigneur ton Dieu; et il t’a choisi, afin que tu sois son peuple particulier entre toutes les nations qui sont sur la terre.
gama ku jama’a ce mai tsarki ga Ubangiji Allahnku. Daga dukan mutane a fuskar duniya, Ubangiji ya zaɓe ku, ku zama abin mallakarsa.
3 Ne mangez pas ce qui est impur.
Kada ku ci wani haramtaccen abu.
4 Voici les animaux que vous devez manger: le bœuf, la brebis, la chèvre,
Waɗannan su ne dabbobin da za ku iya ci, saniya, tunkiya, akuya,
5 Le cerf, et la chèvre sauvage, le bubale, le tragélaphe, le pygargue, l’oryx, la girafe.
mariri, barewa, mariya, makwarna, mazo, gada da kuma tunkiyar dutse.
6 Tout animal qui a l’ongle fendu en deux et qui rumine, vous en mangerez.
Za ku iya cin duk dabbar da take da rababben kofato, wadda kuma take sāke tona abin da suka riga suka haɗiye.
7 Mais pour ceux qui ruminent, et qui n’ont pas l’ongle fendu, comme le chameau, le lièvre, le chœrogrylle, vous ne devez pas en manger: parce que ces animaux ruminent, mais qu’ils n’ont pas l’ongle fendu, ils seront impurs pour vous.
Amma, cikin waɗanda suke sāke tona abin da suka riga suka haɗiye ɗin, ko suke da rababben kofato, ba za ku ci raƙumi, zomo ko rema ba. Ko da yake suna sāke tona abin da suka riga suka haɗiye, suna kuma da rababben kofato, su ɗin marar tsarki ne gare ku.
8 Le pourceau aussi, puisqu’il a l’ongle fendu, mais qu’il ne rumine point, sera impur; vous ne mangerez point de leur chair, et vous ne toucherez point leurs corps morts.
Alade ma marar tsarki ne; ko da yake yana da rababben kofato, shi ba ya sāke tona abin da ya riga ya haɗiye. Ba za ku ci namansu ko ku taɓa gawarsu ba.
9 Voici les bêtes que vous mangerez entre toutes celles qui vivent dans les eaux: celles qui ont des nageoires et des écailles, mangez-les;
Cikin dukan halittun da suke cikin ruwa, za ku iya cin duk wani da yake da ƙege da ɓamɓaroki.
10 Celles qui sont sans nageoires et sans écailles, ne les mangez point, parce qu’elles sont impures.
Amma duk wani abin da ba shi da ƙege da ɓamɓaroki, ba za ku ci ba; gama marar tsarki ne gare ku.
11 Mangez tous les oiseaux purs.
Za ku iya cin kowane tsuntsu mai tsabta.
12 Ne mangez point les impurs: c’est-à-dire l’aigle, le griffon et l’aigle de mer,
Amma waɗannan ba za ku ci ba, gaggafa, ungulu, ungulun kwakwa,
13 L’ixion, le vautour et le milan, selon son espèce;
duki, buga zaɓi, kowace irin shirwa,
14 Tout ce qui est de l’espèce du corbeau;
kowane irin hankaka,
15 L’autruche, le hibou, le larus et l’épervier, selon son espèce;
jimina, ƙururu, bubuƙuwa, kowane irin shaho,
16 Le héron, le cygne, l’ibis,
da mujiya, da babbar mujiya, ɗuskwi,
17 Le plongeon, le porphyrion, la chouette,
kwasakwasa, ungulu, da babba da jaka,
18 L’onocrotale et le pluvier, chacun dans son espèce; la huppe aussi et la chauve-souris.
zalɓe, kowane irin jinjimi, katutu, da kuma jamage.
19 Et tout ce qui rampe sur la terre et qui a des ailes, sera impur, et ne se mangera pas.
Dukan’yan ƙwari masu fikafikai masu rarrafe, haram ne a gare ku, kada ku ci su.
20 Mangez tout ce qui est pur.
Amma duk wata halitta mai fikafikai mai tsabta ce, za ku iya ci.
21 Quant à tout animal qui est crevé, n’en mangez point; donne-le à l’étranger qui est au-dedans de tes portes, afin qu’il en mange, ou vends-lui, parce que toi, tu es le peuple saint du Seigneur ton Dieu. Tu ne feras point cuire un chevreau dans le lait de sa mère.
Kada ku ci abin da kun samu ya riga ya mutu. Za ku iya ba wa baren da yake zama a cikin wani daga biranenku, zai kuwa iya cinsa, ko kuwa za ku iya sayar da shi wa baƙo. Amma ku jama’a ce mai tsarki ga Ubangiji Allahnku. Kada ku dafa ɗan akuya a cikin madara mamansa.
22 Tu sépareras la dixième partie de tous les fruits qui naissent dans la terre tous les ans;
Ku tabbata kun keɓe kashi ɗaya bisa goma na amfanin gonakinku kowace shekara.
23 Et tu en mangeras en la présence du Seigneur ton Dieu, au lieu qu’il aura choisi, afin que son nom y soit invoqué, le dixième de ton blé, de ton vin, de ton huile, et les premiers-nés de ton gros bétail et de tes brebis; afin que tu apprennes à craindre le Seigneur ton Dieu en tout temps.
Ku ci zakkar hatsinku, da na sabon ruwan inabinku, da na manku, da kuma na’ya’yan fari na garkunanku na shanu da na tumaki a gaban Ubangiji Allahnku, a wurin da ya zaɓa a matsayin mazauni don Sunansa, don ku koyi girmama Ubangiji Allahnku kullum.
24 Mais lorsque le chemin sera trop long jusqu’au lieu qu’aura choisi le Seigneur ton Dieu, et lorsqu’il t’aura béni, et que tu ne pourras pas lui apporter toutes ces offrandes,
Amma in wurin nan yana da nisa sosai, Ubangiji Allahnku kuma ya albarkace ku, ba za ku kuwa iya riƙe zakkarku ba (Saboda wurin da Ubangiji ya zaɓa yă sa Sunansa ya yi nisa sosai),
25 Tu vendras tout, tu en feras de l’argent, puis tu le porteras en ta main, et tu partiras pour le lieu qu’aura choisi le Seigneur ton Dieu;
to, sai ku sayar da zakkar, ku tafi da kuɗin wurin da Ubangiji Allahnku ya zaɓa.
26 Tu achèteras avec ce même argent tout ce qui te plaira, soit en gros bétail, soit en brebis, du vin aussi et de la cervoise, et tout ce que désire ton âme; et tu mangeras devant le Seigneur ton Dieu, et tu feras un festin, toi et ta maison;
Yi amfani da kuɗin ku saya duk abin da kuke so, ko shanu, ko tumaki, ko ruwan inabi, ko dai wani abin shan da ya yi tsami, ko kuwa duk abin da kuke so. Sai ku da gidanku, ku ci a can, a gaban Ubangiji Allahnku, ku kuma yi farin ciki.
27 Et le Lévite qui est au-dedans de tes portes, garde-toi de l’abandonner, parce qu’il n’a pas d’autre part dans ta sion.
Kada dai ku manta da Lawiyawan da suke zama a biranenku, gama ba su da rabo, ko gādo na kansu.
28 À la troisième année, tu sépareras une autre dîme de tout ce qui te vient en ce temps, et tu la réserveras au-dedans de tes portes.
A ƙarshen kowace shekara uku, ku kawo dukan zakkarku na amfanin gona na wannan shekara, ku ajiye su a cikin birane,
29 Et il viendra, le Lévite qui n’a point de part ni de possession avec toi, ainsi que l’étranger, l’orphelin et la veuve qui sont au dedans de tes portes, et ils mangeront et se rassasieront, afin que le Seigneur ton Dieu te bénisse dans tous les ouvrages de tes mains que tu feras.
saboda Lawiyawa (waɗanda ba su da rabo ko gādo na kansu) da baƙo, da marayu, da kuma gwauraye, waɗanda suke zama a biranenku, su zo su ci su ƙoshi, ta haka Ubangiji Allahnku zai albarkace ku cikin dukan ayyukan hannuwanku.

< Deutéronome 14 >