< Amos 3 >

1 Ecoutez la parole que le Seigneur a dite sur vous, fils d’Israël, et sur toute la famille que j’ai retirée de la terre d’Egypte.
Ku ji wannan maganar da Ubangiji ya yi game da ku, ya ku jama’ar Isra’ila, a kan dukan iyalin da na fitar daga Masar.
2 C’est seulement vous que j’ai connus de toutes les familles de la terre; c’est pour cela que je visiterai en vous toutes vos iniquités.
“Ku ne kaɗai na zaɓa cikin dukan al’umman duniya; saboda haka zan hukunta ku saboda dukan zunubanku.”
3 Est-ce que deux hommes marcheront ensemble, si cela ne leur convient pas?
Mutum biyu za su iya yin tafiya tare in ba su yarda su yi haka ba?
4 Est-ce qu’un lion rugira dans la forêt, s’il n’a pas une proie? est-ce que le petit d’un lion fera entendre sa voix de sa tanière, s’il n’a rien saisi?
Zaki yakan yi ruri a jeji in bai sami kama nama ba? Zai yi gurnani a cikin kogonsa in bai kama kome ba?
5 Est-ce qu’un oiseau tombera dans un lacs posé sur la terre, sans qu’un oiseleur l’ait tendu? est-ce qu’on enlèvera un lacs de dessus la terre, avant qu’il ait rien pris?
Tsuntsu yakan fāɗa a tarko a ƙasa inda ba a sa tarko ba, ko tarko yakan zargu daga ƙasa in ba abin da ya taɓa shi?
6 Si une trompette sonne, le peuple ne sera-t-il pas épouvanté? Y aurait-il un mal dans une cité, que le Seigneur n’aura pas fait?
Idan aka busa ƙaho a ciki birni mutane ba sa yin rawar jiki? Sa’ad da bala’i ya auko wa birni, ba Ubangiji ne ya sa a kawo shi ba?
7 Car le Seigneur Dieu n’a rien fait, s’il n’a auparavant révélé son secret à ses serviteurs les prophètes.
Ba shakka, Ubangiji Mai Iko Duka ba ya yin wani abu ba tare da ya sanar wa bayinsa annabawa ba.
8 Un lion rugira, qui ne craindra? le Seigneur Dieu a parlé, qui ne prophétisera?
Zaki ya yi ruri, wa ba zai tsorata ba? Ubangiji Mai Iko Duka ya yi magana, wa ba zai yi annabci ba?
9 Faites-le entendre sur les édifices d’Azot et sur les édifices de la terre d’Egypte, et dites: Assemblez-vous sur les montagnes de Samarie, voyez des folies nombreuses au milieu d’elle, et ceux qui souffrent l’oppression dans son enceinte.
Ku yi shela ga kagarun Ashdod da kuma ga kagarun Masar. “Ku tara kanku a tuddan Samariya; ku ga rashin jituwar da take a cikinta, da kuma zaluncin da ake yi a cikin mutanenta.”
10 Et ils n’ont pas su faire le bien, dit le Seigneur, thésaurisant l’iniquité et la rapine dans leurs maisons.
“Ba su ma san yadda za su yi abin da yake daidai ba,” in ji Ubangiji, “sun ɓoye ganima da abubuwan da suka washe a cikin kagarunsu.”
11 À cause de cela, voici ce que dit le Seigneur Dieu: La terre sera pressurée et cernée; et ta force te sera ôtée, et tes édifices seront pillés.
Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce, “Abokin gāba zai ƙwace ƙasar, zai saukar da mafakarku, zai washe kagarunku.”
12 Voici ce que dit le Seigneur: Comme si le pasteur arrachait de la gueule du lion deux jambes ou un bout d’oreille, ainsi seront arrachés des mains de l’ennemi les fils d’Israël qui habitent dans Samarie sur le coin d’un petit lit et sur un grabat de Damas.
Ga abin da Ubangiji ya ce, “Kamar yadda makiyayi yakan ceci daga bakin zaki ƙasusuwa ƙafafu biyu kawai ko kunne ɗaya, haka za a ceci Isra’ilawa, masu zama a Samariya da kan gado kawai da kuma a ɗan ƙyalle a kan dogayen kujerunsu.”
13 Ecoutez, et déclarez à la maison de Jacob, dit le Seigneur Dieu des armées,
“Ku ji wannan ku kuma yi wa gidan Yaƙub gargaɗi,” in ji Ubangiji, Ubangiji Allah Maɗaukaki.
14 Disant: Au jour où je commencerai à visiter les prévarications d’Israël, et les autels de Béthel, alors seront arrachées les cornes de l’autel et elles tomberont par terre.
“A ranar da zan hukunta Isra’ila saboda zunubanta, zan hallaka bagadan Betel; za a yayyanka ƙahonin bagadan za su fāɗa ƙasa
15 Et je frapperai la maison d’hiver avec la maison d’été, et les maisons d’ivoire périront, et des édifices nombreux seront détruits, dit le Seigneur.
Zan rushe gidan rani da na damina; gidajen da aka yi musu ado da hauren giwa za a rushe su haka ma duk za a rurrushe manyan gidaje,” in ji Ubangiji.

< Amos 3 >