< Actes 9 >
1 Cependant Saul, respirant encore menaces et meurtre contre les disciples du Seigneur, vint auprès du prince des prêtres,
Amma Shawulu, ya cigaba da maganganun tsoratarwa har ma da na kisa ga almajiran Ubangiji, ya tafi wurin babban firist
2 Et lui demanda des lettres pour les synagogues de Damas, afin que, s’il y trouvait des hommes et des femmes de cette voie, il les conduisît enchaînés à Jérusalem.
kuma ya roke shi wasiku zuwaga majami'un da ke Dimashku, domin idan ya sami wani da ke na wannan hanya, maza ko mata, ya kawo su Urushalima a daure.
3 Comme il était en chemin, et qu’il approchait de Damas, tout à coup une lumière du ciel brilla autour de lui.
Yayin da yana tafiya, ya kasance da ya iso kusa da Dimashku, nan da nan sai ga wani haske daga sama ya haskaka kewaye da shi;
4 Et, tombant à terre, il entendit une voix qui lui disait: Saul, Saul, pourquoi me persécutes-tu?
Sai ya fadi a kasa kuma yaji wata murya na ce da shi, ''Shawulu, Shawulu, me yasa kake tsananta mani?''
5 Il dit: Qui êtes-vous, Seigneur? Et le Seigneur: Je suis Jésus que tu persécutes; il t’est dur de regimber contre l’aiguillon.
Shawulu ya amsa, ''Wanene kai, Ubangiji?'' Ubangiji ya ce, ''Nine Yesu wanda kake tsanantawa;
6 Alors, tremblant et frappé de stupeur, il dit: Seigneur, que voulez-vous que je fasse?
amma ka tashi, ka shiga cikin birnin, kuma za a gaya maka abinda lallai ne kayi.
7 Et le Seigneur lui répondit: Lève-toi, entre dans la ville; car c’est là que te sera dit ce qu’il faut que tu fasses. Or les hommes qui l’accompagnaient demeuraient tout étonnés, entendant bien la voix, mais ne voyant personne.
Mutanen da ke tafiya tare da Shawulu suka tsaya shiru sun rasa abin fada, suna sauraron muryar, amma ba su ga kowa ba.
8 Saul se leva donc de terre, et, les yeux ouverts, il ne voyait rien. Ainsi, le conduisant par la main, ils le firent entrer dans Damas.
Shawulu ya tashi daga kasa, kuma daga ya bude idanunsa, baya ganin komai; sai suka kama hannuwansa suka yi masa jagora suka kawo shi cikin birnin Dimashku.
9 Et il y fut trois jours ne voyant point; et il ne but ni ne mangea.
Har kwana uku ba ya kallo, kuma ba ya ci balle sha.
10 Or il y avait un certain disciple à Damas, du nom d’Ananie; et le Seigneur lui dit en vision: Ananie. Et il dit: Me voici Seigneur.
Akwai wani almajiri a Dimashku mai suna Hananiya; sai Ubangiji ya yi magana da shi cikin wahayi, ya ce, ''Hananiya.'' Sai ya ce, ''Duba, gani nan Ubangiji.''
11 Et le Seigneur lui dit: Lève-toi, et va dans la rue qu’on appelle Droite, et cherche dans la maison de Judas un nommé Saul de Tarse; car il y est en prières.
Ubangiji ya ce masa, ''Tashi, ka tafi titin da ake kira Mikakke, kuma a gidan wani mai suna Yahuza ka tambaya mutum daga Tarsus mai suna Shawulu; gama yana addu'a;
12 (Saul vit aussi un homme du nom d’Ananie, entrant et lui imposant les mains, pour qu’il recouvrât la vue.)
kuma ya gani cikin wahayi mutum mai suna Hananiya na shigowa kuma ya daura masa hannu, domin idanunsa su bude.''
13 Ananie répondit: Seigneur, j’ai appris d’un grand nombre de personnes combien cet homme a fait de maux à vos saints dans Jérusalem;
Amma Hananiya ya amsa, ''Ubangiji, na ji labari daga wurin mutane da yawa game da mutumin nan, da irin muguntar da ya aikata ga tsarkakan mutanenka da ke Urushalima.
14 Ici même, il a pouvoir des princes des prêtres, pour charger de liens ceux qui invoquent votre nom.
An bashi izini daga babban firist domin ya kama dukan wanda ke kira bisa sunanka.''
15 Mais le Seigneur lui repartit: Va, car cet homme m’est un vase d’élection, pour porter mon nom devant les gentils, les rois et les enfants d’Israël.
Amma Ubangiji ya ce masa, ''Jeka, gama shi zababben kayan aiki na ne, wanda zai yada sunana ga al'ummai da sarakuna da 'ya'yan Isra'ila;
16 Aussi je lui montrerai combien il faut qu’il souffre pour mon nom.
Domin zan nuna masa irin wahalar da zai sha sabo da sunana.''
17 Et Ananie alla, et il entra dans la maison; et lui imposant les mains, il dit: Saul mon frère, le Seigneur Jésus, qui t’a apparu dans le chemin par où tu venais, m’a envoyé pour que tu voies et que tu sois rempli de l’Esprit-Saint.
Sai Hananiya ya tafi, ya shiga gidan. Ya dora masa hannu a kai, ya ce, ''Dan'uwa Shawulu, Ubangiji Yesu, wanda ya bayyana a gareka a hanya sa'adda kake zuwa, ya aiko ni domin ka sami ganin gari ka kuma cika da Ruhu Mai Tsarki.''
18 Et aussitôt tombèrent de ses yeux comme des écailles, et il recouvra la vue; et, se levant, il fut baptisé.
Nan take wani abu kamar bawo ya fado daga idanun Shawulu, kuma ya sami ganin gari; ya tashi aka yi masa baftisma;
19 Et lorsqu’il eut pris de la nourriture, il fut fortifié. Or il demeura quelques jours avec les disciples qui étaient à Damas.
kuma ya ci abinci sai aka karfafa shi. Ya zauna tare da almajirai a Dimashku kwanaki da yawa.
20 Et aussitôt il prêchait dans les synagogues que c’est Jésus qui est le Fils de Dieu.
Nan take ya fara shellar Yesu cikin haikali, yana cewa shine dan Allah.
21 Or tous ceux qui l’écoutaient étaient étonnés et disaient: N’est-ce pas là celui qui poursuivait dans Jérusalem ceux qui invoquaient ce nom, et qui est venu ici pour les conduire chargés de liens aux princes des prêtres?
Dukan wadanda suka saurare shi suka yi mamaki suka ce ''Ba wannan mutumin ne yake hallaka mutanen Urushalima da ke kira bisa ga wannan suna ba? Ya kuma zo nan domin ya ba da su a daure ga manyan firistoci.''
22 Cependant Saul se fortifiait de plus en plus, et confondait les Juifs qui demeuraient à Damas, affirmant que Jésus est le Christ.
Amma Shawulu kuwa ya sami iko sosai, kuma yana haddasa damuwa tare da rinjaya tsakanin Yahudawan dake zama a Dimashku ta wurin tabbatar da Yesu shine Almasihu.
23 Lorsque beaucoup de jours se furent passés, les Juifs prirent ensemble la résolution de le faire mourir.
Bayan kwanaki da yawa, sai Yahudawan suka yi shiri domin su kashe shi.
24 Mais leurs trames furent découvertes à Saul. Or comme ils gardaient nuit et jour les portes pour le tuer,
Amma shirin su ya zama sananne ga Shawulu. Suna fakkon sa ta wurin tsaron kofar birnin dare da rana domin su kashe shi.
25 Les disciples le prirent et le descendirent de nuit par la muraille, le mettant dans une corbeille.
Amma da tsakar dare almajiransa suka daukeshi a kwando, suka zurara shi ta katanga.
26 Lorsqu’il fut venu à Jérusalem, il cherchait à se joindre aux disciples; mais tous le craignaient, ne croyant pas qu’il fût disciple.
Sa'adda ya zo Urushalima, Shawulu ya yi niyyar hada kai da almajirai, amma dukansu suna tsoronsa, domin ba su yarda cewa shima ya zama almajiri ba.
27 Alors Barnabé l’ayant pris avec lui, le conduisit aux apôtres, et leur raconta comment il avait vu le Seigneur dans le chemin, que le Seigneur lui avait parlé, et comment, à Damas, il avait agi avec assurance au nom de Jésus.
Amma Barnaba ya dauke shi ya kawo shi wurin manzannin. Ya kuwa gaya musu yadda Shawulu ya sadu da Ubangiji a hanya, har Ubangiji ya yi magana da shi, kuma yadda Shawulu ya yi wa'azi cikin sunan Yesu gabagadi a Dimashku.
28 Saul demeurait donc avec eux à Jérusalem, agissant avec assurance au nom du Seigneur.
Ya sadu da su lokacin shigar su da fitar su a Urushalima. Ya yi wa'azi gabagadi cikin sunan Ubangiji Yesu
29 Il parlait aussi aux gentils, et disputait avec les Grecs; or ceux-ci cherchaient à le tuer.
kuma yana muhawara da Yahudawan Helenanci; amma sun ci gaba da kokarin kashe shi.
30 Ce que les frères ayant su, ils le conduisirent à Césarée, et l’envoyèrent à Tarse.
Da 'yan'uwa suka gane haka, sai suka kawo shi Kaisariya, suka kuwa tura shi zuwa Tarsus.
31 L’Eglise cependant jouissait de la paix dans toute la Judée, la Galilée et le pays de Samarie; elle s’établissait marchant dans la crainte du Seigneur, et elle était remplie de la consolation du Saint-Esprit.
Sa'annan iklisiya dake dukan kasar Yahudiya, Galili da kuma Samariya suka sami salama da kuma ginuwa; suka kuwa ci gaba da tafiya cikin tsoron Ubangiji, da kuma ta'aziyar Ruhu Mai Tsarki, iklisiyar kuwa ta karu da yawan mutane.
32 Or il arriva que Pierre, en les visitant tous, vint voir les saints qui habitaient Lydde.
Har ta kai, yayin da Bitrus ya zaga dukan yankin kasar, ya dawo wurin masu bi dake zama a garin Lidda.
33 Et il trouva là un homme du nom d’Enée, gisant depuis huit ans sur un grabat, étant paralytique.
A can kuwa ya sami wani mutum mai suna Iniyasu, wanda yake shanyayye ne, yana kwance har tsawon shekara takwas a kan gado.
34 Et Pierre lui dit: Enée, le Seigneur Jésus-Christ te guérit; lève-toi et fais toi-même ton lit. Et aussitôt il se leva.
Bitrus ya ce masa, ''Iniyasu, Yesu Almasihu ya warkar da kai. Tashi ka nade shimfidarka.'' Nan take sai ya mike.
35 Et tous ceux qui habitaient Lydde et Sarone le virent, et ils se convertirent au Seigneur.
Sai duk mazauna kasar Lidda da kasar Sarona suka ga mutumin, suka kuma juyo ga Ubangiji.
36 Il y avait à Joppé, parmi les disciples, une femme du nom de Tabithe, qui veut dire par interprétation Dorcas. Elle était remplie de bonnes œuvres et elle faisait beaucoup d’aumônes.
Yanzu kuwa a Yafa akwai wata almajira, mai suna Tabita, ma'ana ''Dokas.'' Wannan matar kuwa tana chike da ayyukan nagarta da halin tausayi da take yi ga mabukata.
37 Or il arriva en ces jours-là qu’étant tombée malade, elle mourut. Après qu’on l’eut lavée, on la mit dans une chambre haute.
Ya kai ga cewa a kwanakin can ta yi rashin lafiya har ta mutu; da suka wanke gawar ta suka kwantar da ita a bene.
38 Et comme Lydde était près de Joppé, les disciples ayant appris que Pierre y était, envoyèrent vers lui deux hommes, pour lui faire cette prière: Hâte-toi de venir jusqu’à nous.
Da shike Lidda na kusa da Yafa, almajiran kuma sun ji cewa Bitrus yana can, suka aika mutane biyu wurinsa. Suna rokansa, ''Ka zo garemu ba tare da jinkiri ba.''
39 Or Pierre, se levant, vint avec eux. Et lorsqu’il fut arrivé, ils le conduisirent dans le cénacle, et toutes les veuves l’entourèrent pleurant, et lui montrant des tuniques et des vêtements que leur faisait Dorcas.
Bitrus ya tashi ya tafi da su, da isowar sa, suka kai shi benen. Sai dukan gwamrayen suka tsaya kusa da shi suna kuka, sai suka dauko riguna da sutura da Dokas ta dinka lokacin da take tare da su.
40 Alors, ayant fait sortir tout le monde, Pierre, s’agenouillant, pria; et, se tournant vers le corps, il dit: Tabithe, lève-toi. Et elle ouvrit les yeux, et ayant vu Pierre, elle se mit sur son séant.
Bitrus ya fitar da su duka daga cikin dakin, ya durkusa, ya yi addu'a; sai, ya juya wurin gawar, ya ce, ''Tabita, tashi.'' Ta bude idanunta, da ta ga Bitrus ta zauna,
41 Alors, lui donnant la main, il la leva; et quand il eut appelé les saints et les veuves, il la leur rendit vivante.
Bitrus kuwa ya mika hannunsa ya tashe ta; sa'annan ya kira masu bi da gwamrayen, ya mika ta a raye garesu.
42 Cela fut connu dans tout Joppé; et beaucoup crurent au Seigneur.
Wannan al'amari ya zama sananne cikin dukan Yafa, kuma mutane da yawa suka bada gaskiya ga Ubangiji.
43 Or il arriva qu’il demeura un grand nombre de jours à Joppé, chez un certain Simon, corroyeur.
Ya kasance, cewa, Bitrus ya zauna kwanaki da dama a Yafa tare da wani mutum mai suna Saminu, majemi.