< Actes 6 >

1 Or en ces jours-là, le nombre des disciples croissant, il s’éleva un murmure des Grecs contre les Hébreux, de ce que leurs veuves étaient négligées dans la distribution de chaque jour.
A wadannan kwanaki, yawan almajiran ya ci gaba da ribanbanya, sai Yahudawan da suke zama a kasar Helanawa suka fara gunaguni game da Yahudawan Isra'ila, domin basu damu da gwamrayensu, wajen raba abinci da ake yi kullum.
2 Les douze donc, convoquant la multitude des disciples, dirent: Il n’est pas juste que nous abandonnions la parole de Dieu, et que nous vaquions au service des tables.
Manzannin nan sha biyu suka kira taron almajiran suka ce masu, ''Bai kamata mu bar maganar Allah mu shiga hidimar rabon abinci ba.
3 Cherchez donc parmi vous, mes frères, sept hommes de bon témoignage, pleins de l’Esprit-Saint et de sagesse, que nous puissions préposer à cette œuvre.
Don haka ku zabi 'yan'uwa maza daga cikinku, mutane bakwai wadanda a ke ganin su da daraja, cike da Ruhu da kuma hikima, wadanda za mu zaba suyi wannan hidima.
4 Poumons, nous nous appliquerons à la prière et au ministère de la parole.
Mu kuwa mu ci gaba da da addu'a da kuma hidimar kalmar.''
5 Ce discours plut à toute la multitude. Et ils élurent Etienne, homme plein de foi et de l’Esprit-Saint, Philippe, Prochore, Nicanor, Timon, Parménas et Nicolas, prosélyte d’Antioche.
Maganar su kuwa ta farantawa dukan jama'a rai sosai. Sai suka zabi Istifanus, shi kuwa mutum ne cike da bangaskiya kuma da Ruhu Mai Tsarki da Filibus, da Birokoros, da Nikanar, da Timan, da Barminas, da kuma Nikolas, mutmin Antakiya wanda ya yi tuban Yahudanci.
6 Ils les présentèrent aux apôtres, et ceux-ci, priant, leur imposèrent les mains.
Masu bin kuwa suka gabatar da wadannan mutanen a gaban manzannin, su kuwa suka yi masu addu'a suka kuma dora hannuwansu a kansu.
7 Et la parole du Seigneur croissait, et le nombre des disciples se multipliait grandement à Jérusalem; et même un grand nombre de prêtres obéissaient à la foi.
Sai maganar Allah ta yawaita; yawan almajiran kuwa ya rubanbanya matuka a Urushalima; firistoci da yawa na Yahudawa suka bada gaskiya.
8 Or Etienne, plein de grâce et de force, faisait des prodiges et de grands miracles parmi le peuple.
Sai Istifanus, cike da alheri da iko, ya rika yin ayyukan ban mamaki da alamu a cikin jama'a.
9 Mais quelques-uns de la synagogue qui est appelée des Affranchis, de celle des Cyrénéens et des Alexandrins, et de ceux qui étaient de Cilicie et d’Asie, se levèrent, disputant contre Etienne;
Amma sai ga wadansu mutane daga wata majami'a da ake kira majami'ar Yantattu, wato su Kuramiyawa da Iskandariyawa, da kuma wasu daga kasar Kilikiya da Asiya. Wadannan mutanen kuwa suna muhawara da Istifanus.
10 Et ils ne pouvaient résister à la sagesse et à l’Esprit-Saint qui parlait.
Amma suka kasa yin tsayayya da Istifanus, saboda irin hikima da Ruhun da Istifanus ya ke magana da shi.
11 Alors ils subornèrent des hommes pour dire qu’ils l’avaient entendu proférer des paroles de blasphème contre Moïse et contre Dieu.
Sai a asirce suka zuga wasu mutane su je su ce, ''Ai munji Istifanus yana maganganun sabo game da Musa da kuma Allah.''
12 Ils soulevèrent ainsi le peuple, les anciens et les scribes: et ceux-ci accourant ensemble, l’entraînèrent et l’amenèrent au conseil,
Sai suka zuga mutanen, har da dattawa da marubuta suka tunkari Istifanus, suka kama shi, suka kawo shi gaban majalisa.
13 Et ils produisirent de faux témoins pour dire: Cet homme ne cesse de parler contre le lieu saint et contre la loi;
Suka kawo masu shaidar karya suka ce, ''Wannan mutumin har yanzu bai dena maganganun gaba akan wannan wuri mai tsarki da kuma shari'a ba.
14 Car nous l’avons entendu disant que ce Jésus de Nazareth détruira ce lieu, et changera les traditions que nous a données Moïse.
Domin kuwa mun ji shi, yana cewa wannan Yesu Banazarat zai rushe wannan wuri zai kuma canza al'adun da muka gada daga wurin Musa.''
15 Et tous ceux qui siégeaient dans le conseil, ayant fixé les yeux sur lui, ils virent son visage comme le visage d’un ange.
Dukan wadanda suke zaune a majalisar suka zuba masa ido, sai suka ga fuskarsa kamar ta mala'ika.

< Actes 6 >