< Actes 4 >

1 Or, pendant qu’ils parlaient au peuple, survinrent les prêtres, et le magistrat du temple, et les sadducéens,
Yayin da Bitrus da Yahaya suna kan magana da mutanen, sai firistoci da shugaban masu tsaron Haikali da kuma Sadukiyawa suka afko masu.
2 Courroucés de ce qu’ils enseignaient le peuple, et annonçaient en Jésus la résurrection des morts;
Sun damu sosai domin Bitrus da Yahaya suna koyar da mutane game da Yesu kuma suna shelar tashinsa daga matattu.
3 Et ils mirent la main sur eux, et les jetèrent en prison jusqu’au lendemain, car il était déjà soir.
Suka kama su suka jefa kurkuku sai washegari, domin yamma ta riga ta yi.
4 Cependant beaucoup de ceux qui avaient entendu la parole crurent, et le nombre des hommes fut de cinq mille.
Amma mutane da yawa da suka ji sakon suka ba da gaskiya; kimanin mazaje dubu biyar ne kuwa suka ba da gaskiya.
5 Or il arriva le lendemain que leurs chefs, les anciens et les scribes, s’assemblèrent à Jérusalem,
Washegari, da shugabaninsu, da dattawansu, da Marubuta suka taru a Urushalima.
6 Et aussi Anne, prince des prêtres, Caïphe, Jean, Alexandre, et tous ceux qui étaient de la race sacerdotale.
Anas babban firist, yana nan, da Kayafa, da Yahaya da Iskandari, da dukan dangin babban firist
7 Et les faisant placer au milieu, ils demandaient: Par quelle puissance et en quel nom avez-vous fait cela, vous?
Da suka kawo Bitrus da Yahaya a tsakiyarsu sai suka tambaye su, “Da wanne iko, ko cikin wanne suna k ka yi haka?”
8 Alors, rempli de l’Esprit-Saint, Pierre leur dit: Princes du peuple, et vous, anciens, écoutez:
Sai Bitrus, cike da Ruhu Mai Tsarki, ya ce, “Ku shugabanni da dattawan jama'a,
9 Puisque aujourd’hui nous sommes jugés à cause d’un bienfait en faveur d’un homme infirme, et à cause de celui en qui il a été guéri,
idan mu yau ana tuhumarmu saboda aikin kirki da aka yi ga wannan mara lafiya - ta yaya wannan mutum ya sami lafiya?
10 Qu’il soit connu de vous tous et de tout le peuple d’Israël que c’est au nom de Notre Seigneur Jésus-Christ de Nazareth, que vous avez crucifié et que Dieu a ressuscité des morts; c’est par lui que cet homme est ici devant vous, debout et sain.
Bari ku da dukan mutanen Isra'ila, ku san wannan, cikin sunan Yesu Almasihu Banazare, wanda kuka giciye, wanda Allah ya tayar daga matattu ta dalilinsa ne wannan mutumin yake tsaye a gaban ku lafiyayye.
11 Ce Jésus est la pierre qui a été rejetée par vous qui bâtissiez, et qui est devenue un sommet d’angle;
Yesu Almasihu ne dutsen da ku magina kuka ki, amma an mai da shi kan gini.
12 Et il n’y a de salut en aucun autre; car nul autre nom n’a été donné sous le ciel aux hommes, par lequel nous devions être sauvés.
Babu ceto daga kowanne mutum, domin babu wani suna da aka bayar karkashin sama, a cikin mutane wanda ta wurinsa za a iya samu ceto.''
13 Voyant donc la constance de Pierre et de Jean, et ayant appris que c’étaient des hommes sans lettres, et du commun, ils s’étonnaient; ils savaient d’ailleurs qu’ils avaient été avec Jésus.
Sa'adda, suka ga karfin halin Bitrus da Yahaya, suka gane mutane ne talakawa marasa ilimi, sai suka yi mamaki, suka kuma lura suka gane Bitrus da Yahaya sun kasance tare da Yesu.
14 Voyant aussi debout près d’eux l’homme qui avait été guéri, ils ne pouvaient rien dire contre.
Da yake suna ganin mutumin nan da aka warkar tare da su, sai suka rasa abin yi.
15 Mais ils leur ordonnèrent de sortir du Conseil, et ils conféraient entre eux,
Amma bayan sun fitar da manzannin daga majalisa sai suka tattauna a tsakaninsu.
16 Disant: Que ferons-nous à ces hommes? Car un miracle fait par eux est connu de tous les habitants de Jérusalem; cela est manifeste, et nous ne pouvons le nier.
Suka ce, “Yaya za mu yi da wadannan mutane? Babu shakka aikin al'ajibi ya faru ta wurinsu, kuma sananne ne ga dukan mazauna Urushalima, kuma ba mu da iko mu musanci haka.
17 Mais, afin qu’il ne se divulgue pas davantage parmi le peuple, défendons-leur avec menaces de parler désormais en ce nom à aucun homme.
Amma saboda kada ya cigaba da yaduwa cikin mutane, bari mu yi masu kashedi kada su kara magana da kowa cikin wannan suna.''
18 Et les ayant appelés, ils leur enjoignirent de ne parler ni d’enseigner en aucune sorte au nom de Jésus.
Suka kira Bitrus da Yahaya suka dokace su kada su kara magana ko kuma koyarwa ko kadan a cikin sunan Yesu.
19 Mais Pierre et Jean, répondant, leur dirent: S’il est juste devant Dieu de vous obéir plutôt qu’à Dieu, jugez-en?
Amma Bitrus da Yahaya suka amsa suka ce, ''Ko ya yi daidai a gaban Allah mu yi maku biyayya fiye da shi, ku hukunta.
20 Car nous ne pouvons pas ne point parler de ce que nous avons vu et entendu.
Baza mu iya daina magana game da abubuwan da muka ji kuma muka gani ba.''
21 Mais eux les renvoyèrent avec menaces, ne trouvant pas comment les punir à cause du peuple, parce que tous vantaient beaucoup ce qui était arrivé dans cet événement.
Bayan sun sake yi wa Bitrus da yahaya kashedi, sai suka sake su, su tafi. Domin ba su iya samu wata hujja da za su hore su a kai ba, domin dukan mutane suna yabon Allah saboda abin da ya faru.
22 Car il avait plus de quarante ans, l’homme sur qui avait été fait ce miracle de la guérison.
Mutumin da ya sami wannan al'ajibi na warkarwa yana sama da shekara arba'in.
23 Ainsi renvoyés, ils vinrent vers les leurs, et leur racontèrent tout ce que les princes des prêtres et les anciens leur avaient dit.
Bayan an sake su, Bitrus da Yahaya suka zo cikin mutanensu suka ba da rahoton duk abin da manyan firistoci da dattawa suka fada masu.
24 Ce qu’ayant entendu, ceux-ci élevèrent unanimement la voix vers Dieu, et dirent: Seigneur, c’est vous qui avez fait le ciel et la terre, et la mer, et tout ce qui est en eux;
Da suka ji haka, suka daga muryarsu tare ga Allah suka ce, ''Ubangiji, kai da ka yi sama da duniya da teku da duk abin da ke cikinsu,
25 Qui par l’Esprit-Saint et par la bouche de nôtre père David, votre serviteur, avez dit: Pourquoi les nations ont-elles frémi, et les peuples médité des choses vaines?
kai wanda ta wurin Ruhu Mai Tsarki ta bakin ubanmu Dauda bawanka, ya ce, 'Me ya sa al'ummai suka tunzura, kuma mutane suke tunanin abubuwan banza?
26 Pourquoi les rois de la terre se sont-ils levés, et les princes se sont-ils ligués contre le Seigneur et contre son Christ?
Sarakunan duniya sun hada kansu tare, kuma shugabanninsu sun taru don su yi gaba da Ubangiji, da kuma Almasihunsa.'
27 Car Hérode et Ponce-Pilate se sont vraiment ligués dans cette cité avec les gentils et les peuples d’Israël, contre votre saint Fils Jésus que vous avez consacré par votre onction,
Hakika, Hiridus da Buntus Bilatus, tare da al'ummai da mutanen Isra'ila, sun taru a wannan birni domin su yi jayayya da bawanka mai tsarki Yesu, shafaffe.
28 Pour faire ce que votre bras et votre conseil avaient décrété qui serait fait.
Sun taru domin su aiwatar da dukan abin da hannunka da nufinka ya shirya zai faru.
29 Et maintenant. Seigneur, regardez leurs menaces, et donnez à vos serviteurs d’annoncer votre parole en toute confiance,
Yanzu, Ya Ubangiji ka dubi kashedin su, ka ba bayin ka ikon furta maganar ka gabagadi.
30 En étendant votre main pour que des guérisons, des miracles et des prodiges soient faits par le nom de votre saint Fils Jésus.
Sa'adda ka mika hannunka domin warkarwa, alamu da al'ajibai su faru ta wurin sunan bawanka mai tsarki Yesu.”
31 Et quand ils eurent prié, le lieu où ils étaient assemblés trembla, et ils furent tous remplis de l’Esprit-Saint, et ils annonçaient la parole de Dieu avec confiance.
Bayan sun gama addu'a, wurin da suka taru ya girgiza, suka cika da Ruhu Mai Tsarki, suka furta maganar Allah gabagadi.
32 Or la multitude des croyants n’avait qu’un cœur et qu’une âme; et nul ne regardait comme étant à lui rien de ce qu’il possédait; mais toutes choses leur étaient communes.
Babban taron da suka ba da gaskiya kansu hade yake; kuma ba wanda ya ce da abinda ya mallaka nasa ne; maimakon haka, komai na su daya ne.
33 Et les apôtres rendaient témoignage avec une grande force de la résurrection du Seigneur Jésus-Christ, et une grande grâce était en eux tous.
Da iko mai karfi manzannin suka yi shelar shaidarsu game da tashin Yesu Ubangiji daga matattu, babban alheri kuma na bisansu.
34 Aussi il n’y avait aucun pauvre parmi eux; car tout ce qu’il y avait de possesseurs de champs ou de maisons, les vendaient, et apportaient le prix de ce qu’ils avaient vendu,
Babu wani a cikinsu wanda ya rasa komai, domin masu filaye da gidaje suka sayar suka kawo kudin abin da suka sayar
35 Et le déposaient aux pieds des apôtres; on le distribuait ensuite à chacun selon qu’il en avait besoin.
sai suka kawo kudin gaban manzanni. Aka rarraba wa kowanne mutum bisa ga bukatarsa.
36 Joseph donc, surnommé par les apôtres Barnabé (qu’on interprète par fils de consolation), lévite et Cypriote de naissance,
Yusufu, Balawi, mutumin tsibirin Kubrus, wanda manzannisu ka yi wa lakani da suna Barnaba. (wato, mai karfafa zuciya).
37 Comme il avait un champ, le vendit, et en apporta le prix, et le déposa aux pieds des apôtres.
Yana da fili sai ya sayar da shi ya kawo kudin gaban manzanni.

< Actes 4 >