< Actes 26 >
1 Alors Agrippa dit à Paul: On te permet de parler pour te défendre. Paul aussitôt, étendant la main, commença sa justification.
Sai Agaribas ya ce wa Bulus, “Za ka iya kare kan ka.” Sai Bulus ya daga hannunsa ya fara kare kansa.
2 Roi Agrippa, je m’estime heureux d’avoir, sur toutes les choses dont les Juifs m’accusent, à me défendre aujourd’hui devant vous,
“Ina farinciki, ya sarki Agaribas, game da saran da Yahudawa ke kawowa a kaina yau;
3 Surtout, vous connaissant toutes choses, et les coutumes et les questions qui existent parmi les Juifs. C’est pourquoi je vous supplie de m’écouter avec patience.
musamman ma don kai masani ne game da al'adun Yahudawa da al'amuransu. Don haka, ina rokanka ka yi hakuri ka saurare ni.
4 Et d’abord ma vie qui, depuis le commencement, s’est passée au milieu de ma nation à Jérusalem, tous les Juifs la connaissent,
Hakika, dukan Yahudawa sun san yadda na yi rayuwa ta daga kurciyata a kasa ta, da kuma Urushalima.
5 Sachant d’avance (s’ils veulent rendre témoignage), que, dès le commencement, j’ai vécu pharisien, selon la secte la mieux fondée de notre religion.
Sun san ni tun farko, kuma yakamata su yarda cewa na yi rayuwa kamar Bafarase, darikan nan mai tsatsauran ra'ayi ta addininmu.
6 Et cependant me voici soumis à un jugement au sujet de l’espérance en la promesse qui a été faite par Dieu à nos pères,
Yanzu ina tsaye a nan dominn a shari'anta ni, saboda alkawalin da Allah ya yi wa ubanninmu.
7 Et dont nos douze tribus, servant Dieu nuit et jour, espèrent entrer en possession. Ainsi, c’est au sujet de cette espérance, ô roi, que je suis accusé par les Juifs.
Domin wannan shine alkawalin da kabilunmu goma sha biyu suka sa zuciya su karba, yayin da suke yin sujada da himma ga Allah dare da rana. Saboda wanan bege, Sarki Agaribas, Yahudawa ke tuhuma ta.
8 Juge-t-on incroyable parmi vous que Dieu ressuscite les morts?
Me ya sa wani zai yi tunani cewa abin mamaki ne Allah ya ta da mattatu?
9 Pour moi, j’avais pensé que je devais par mille moyens agir contre le nom de Jésus de Nazareth;
Da, na yi tunanin yin abubuwa gaba da sunan Yesu Banazarat.
10 Et c’est ce que j’ai fait à Jérusalem; j’ai jeté en prison un grand nombre de saints, en ayant reçu le pouvoir des princes des prêtres; et, lorsqu’on les faisait mourir, j’ai donné mon suffrage.
Na yi wadanan a Urshalima. Na kulle masu bi da yawa a kurkuku, sanadiyar iko da na samu daga wurin manyan firistoci, kuma da ake kashe su ma, ina ba da goyon baya.
11 Et parcourant souvent toutes les synagogues pour les tourmenter, je les forçais de blasphémer; et, de plus en plus furieux contre eux, je les poursuivais jusque dans les villes étrangères.
Na wahalshe su sau dayawa a cikin dukan majamiu ina kuma yin kokari in tilasta masu su yi sabo. Na yi gaba mai zafi da su kuma na tsananta masu har zuwa birane na wadansu kasashe.
12 Comme j’allais dans ces dispositions à Damas, avec pouvoir et permission des princes des prêtres,
A sa'anda nake yin wannan, na tafi Dimashku da izinin manyan firistoci;
13 Je vis, ô roi, au milieu du jour, dans le chemin, qu’une lumière du ciel, surpassant l’éclat du soleil, brillait autour de moi et de ceux qui étaient avec moi.
a cikin tafiyata kuma, da tsakar rana, ya sarki, na ga haske daga sama da ya fi rana sheki, ya haskaka kewaye da ni da kuma wadanda ke tafiya tare da ni.
14 Et, étant tous tombés par terre, j’entendis une voix qui me disait en langue hébraïque: Saul, Saul, pourquoi me persécutes-tu? Il t’est dur de regimber contre l’aiguillon.
Da dukanmu muka fadi kasa, na ji wata murya na magana da ni a harshen Ibraniyawa tana cewa, 'Shawulu, Shawulu, don me kake tsananta mani? Yana da wuya ka hauri abin da ke mai tsini.'
15 Et moi, je demandai: Qui êtes-vous, Seigneur? Et le Seigneur répondit: Je suis Jésus que tu persécutes.
Sai na ce, 'Wanene kai ya Ubangiji?' Ubangiji ya amsa, 'Ni ne Yesu wanda kake tsanantawa.
16 Mais lève-toi et tiens-toi sur tes pieds; car je ne t’ai apparu que pour t’établir ministre et témoin des choses que tu as vues, et de celles pour lesquelles je t’apparaîtrai encore,
Yanzu ka tashi tsaye domin saboda wannan dalili ne na bayyana gare ka in sanya ka, ka zama bawa da mashaidi na game da abubuwan da ka sani a kaina yanzu da wadanda zan bayyana maka daga bisani;
17 Te délivrant des mains du peuple et de celles des gentils vers lesquels je t’envoie maintenant,
Zan kubutar da kai daga wurin mutane da kuma al'ummai da zan aike ka wurinsu,
18 Pour ouvrir leurs yeux, afin qu’ils se convertissent des ténèbres à la lumière, et de la puissance de Satan à Dieu, et qu’ils reçoivent la rémission des péchés, et une part entre les saints, par la foi en moi.
domin ka bude idanunsu ka juyo su daga duhu zuwa haske da daga ikon Shaidan zuwa ga Allah, domin su karbi gafarar zunubai da gado da zan ba wadanda na kebe wa kaina ta wurin bangaskiya gare ni.'
19 Ainsi, roi Agrippa, je ne fus pas incrédule à la vision céleste;
Saboda haka, sarki Agaribas, ban yi rashin biyayya da wahayin da na gani daga sama ba;
20 Mais à ceux de Damas, d’abord, puis à Jérusalem, dans tout le pays de Judée, et aux gentils, j’annonçais qu’ils fissent pénitence, et qu’ils se convertissent à Dieu, faisant de dignes œuvres de pénitence.
amma, da farko ga wadanda ke a Dimashku, sa'annan a Urushalima da kasar Yahudiya gaba daya, da dukan Al'ummai, na yi wa'azi domin su tuba su kuma juyo ga Allah, su yi ayyukan da suka chanchanci tuba.
21 Voilà pourquoi les Juifs; s’étant saisis de moi lorsque j’étais dans le temple, cherchaient à me tuer.
Domin wannan dalili ne Yahudawa suka kama ni a cikin haikali kuma suke kokari su kashe ni.
22 Mais, assisté du secours de Dieu, jusqu’à ce jour je suis demeuré ferme, rendant témoignage aux petits et aux grands, ne disant rien que ce que les prophètes et Moïse ont prédit devoir arriver:
Allah ya taimake ni har wa yau, domin in iya tsayawa gaban mutane kanana da manya, in bada shaida game da iyakar abin da annabawa da Musa suka fada zai faru;
23 Que le Christ souffrirait, qu’il serait le premier dans la résurrection des morts, et qu’il devait annoncer la lumière à ce peuple et aux gentils.
wato lallai Almasihu zai sha wahala, ya kuma zama na farko da za'a rayar daga matattu ya kuma yi shelar haske zuwa ga mutanen Yahudawa da Al'ummai.”
24 Comme il parlait ainsi, exposant sa défense, Festus, d’une voix forte, dit: Tu es fou, Paul; ton grand savoir te fait perdre le sens.
Da Bulus ya gama kare kansa, Festas ya yi magana da babban murya, “Bulus, kana hauka; yawan iliminka yasa ka hauka.”
25 Et Paul: Je ne suis point fou (dit-il), ô excellent Festus; mais je dis des paroles de sagesse et de vérité.
Amma Bulus ya ce, “Ba na hauka, ya mai girma Festas; amma da karfin zuciya nake fadi kalmomin gaskiya da na natsuwa.
26 Et il sait bien ces choses, le roi devant qui je parle avec tant d’assurance; car je pense qu’il n’ignore rien de cela, aucune de ces choses ne s’étant passée dans un coin.
Saboda sarkin ya san wadannan abubuwa duka; shi ya sa nake magana gabagadi, don na hakikance cewa, ba abin da ke a boye gare shi; gama ba a yi wadannan abubuwa a boye ba.
27 Croyez-vous aux prophètes, roi Agrippa? Je sais que vous y croyez.
Ko ka gaskanta da annabawa, Sarki Agaribas? Na sani ka gaskanta.”
28 Et Agrippa à Paul: Peu s’en faut que tu ne me persuades d’être chrétien.
Agaribas ya ce wa Bulus, “A cikin karamin lokaci kana so ka rinjaye ni ka mai da ni Krista?”
29 Mais Paul: Plaise à Dieu qu’il ne s’en faille ni peu ni beaucoup; que non seulement vous, mais encore tous ceux qui m’écoutent, deveniez aujourd’hui tels que je suis moi-même, à l’exception de ces liens.
Bulus ya ce, “Ina roko ga Allah, domin ko a karamin lokaci ko a dogon lokaci, ba kai kadai ba, amma har da wadanda ke sauraro na yau su zama kamar ni, amma ban da wadannan sarkokin.”
30 Alors le roi, le gouverneur, Bérénice, et tous ceux qui étaient assis avec eux se levèrent.
Sai sarki ya tashi tsaye tare da gwamna da Barniki da dukan wadanda ke zaune tare da su;
31 Et s’étant retirés à part, ils se parlaient l’un à l’autre, disant: Cet homme n’a rien fait qui mérite la mort ou les liens.
da suka bar dakin taron, suka ci gaba da magana da juna suna cewa, “Wannan mutum bai yi wani abin da ya chanchanci mutuwa ko kuma dauri ba.”
32 Aussi Agrippa dit à Festus: Cet homme pourrait être renvoyé, s’il n’en avait appelé à César.
Agaribas ya ce wa Fastos, “Da mutumin nan bai daukaka kara zuwa ga Kaisar ba da an sake shi.”