< 2 Samuel 7 >
1 Or il arriva que lorsque le roi se fut établi en sa maison, et que le Seigneur lui eut donné le repos de toutes parts du côté de tous ses ennemis,
Bayan sarki ya kama zama a fadansa Ubangiji kuma ya hutashe shi daga dukan abokan gābansa da suke kewaye da shi,
2 Il dit à Nathan le prophète: Vois-tu que j’habite dans une maison de cèdre, et que l’arche de Dieu est placée au milieu des peaux?
sai ya ce wa annabi Natan, “Ga ni, ina zama a fadar katakon al’ul, amma akwatin alkawarin Allah yana zaune a tenti.”
3 Et Nathan répondit au roi: Tout ce qui est en votre cœur, allez, faites-le, parce que le Seigneur est avec vous.
Natan ya amsa wa sarki ya ce, “Duk abin da yake a zuciyarka, sai ka yi, gama Ubangiji yana tare da kai.”
4 Or il arriva pendant cette nuit-là, que voilà que la parole du Seigneur vint à Nathan, disant:
A daren nan maganar Ubangiji ta zo wa Natan cewa,
5 Va, et dis à mon serviteur David: Voici ce que dit le Seigneur: Est-ce que tu ne me bâtiras point une maison pour l’habiter?
“Je ka faɗa wa bawana Dawuda, ‘Ga abin da Ubangiji ya ce, kai ne za ka gina mini gida in zauna?
6 Car je n’ai pas habité dans une maison, depuis le jour que j’ai retiré les enfants d’Israël de la terre d’Egypte, jusqu’à ce jour-ci; mais je marchais dans un tabernacle, dans une tente.
Ban taɓa zama a gida ba tun daga ranar da na fito da Isra’ilawa daga Masar har yă zuwa yau. Ina dai kai da kawowa a tenti, a matsayin mazaunina.
7 Dans tous les lieux par où j’ai passé avec tous les enfants d’Israël, est-ce que j’ai jamais dit à une des tribus d’Israël, à laquelle j’ai ordonné de conduire mon peuple Israël, disant: Pourquoi ne m’avez-vous pas bâti une maison de cèdre?
A cikin kaiwa da kawowar da nake yi cikin dukan Isra’ilawa, na taɓa ce wa wani shugabanninsu wanda na umarta su lura da mutanena Isra’ila, “Don me ba ku gina mini mazauni da katakon al’ul ba?”’
8 Et maintenant tu diras ceci à mon serviteur David: Voici ce que dit le Seigneur des armées: C’est moi qui t’ai tiré des pâturages, lorsque tu suivais les troupeaux, afin que tu fusses chef sur mon peuple Israël;
“Yanzu, ka gaya wa bawana Dawuda ‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, na ɗauko ka daga makiyaya, daga kuma garken tumaki ka zama sarki bisan mutane Isra’ila.
9 Et j’ai été avec toi dans tous les lieux où tu as marché, et j’ai tué tous tes ennemis devant toi, et j’ai rendu ton nom grand, comme le nom des grands qui sont sur la terre.
Na kasance tare da kai duk inda ka tafi, na kuma kawar da dukan abokan gābanka a gabanka. Yanzu zan sa sunanka yă shahara kamar sunayen shahararrun mutanen duniya.
10 Et je fixerai un lieu à mon peuple Israël, et je le planterai, et il y habitera, et il ne sera plus troublé; et des fils d’iniquité ne recommenceront pas à l’affliger, comme auparavant,
Zan kuma tanada wa mutanena Isra’ila wuri, in kuma dasa su yadda za su kasance da gida kansu ba tare da an ƙara damunsu ba. Mugayen mutane ba za su ƙara wahalshe su kamar dā ba,
11 Depuis le jour que j’ai établi des juges sur mon peuple Israël; et je te donnerai le repos du côté de tous tes ennemis; et le Seigneur t’annonce qu’il te fera une maison.
yadda suka yi tun lokacin da na naɗa shugabanni bisan mutanena Isra’ila, zan kuma hutashe ka daga hannun abokan gābanka. “‘Ubangiji ya furta maka cewa Ubangiji kansa zai kafa maka gida.
12 Et lorsque tes jours seront accomplis, et que tu dormiras avec tes pères, je te susciterai un fils après toi, lequel sortira de tes entrailles, et j’affermirai son règne.
Sa’ad da kwanakinka suka ƙare, za ka huta tare da kakanninka, zan tā da zuriyarka, na cikinka, zan kuma sa mulkinsa ya kahu.
13 C’est lui qui bâtira une maison à mon nom, et j’établirai fermement le trône de son royaume pour toujours.
Shi zai gina gida domin Sunana, zan kuwa kafa gadon sarautarsa har abada.
14 Moi je serai son père, et lui sera mon fils; et s’il fait quelque chose iniquement, je le châtierai avec une verge d’homme, et avec des plaies des enfants des hommes.
Zan zama Ubansa, shi kuma yă zama ɗana. Idan ya yi laifi, zan yi amfani da mutane in hukunta shi. Mutane ne za su zama bulalata.
15 Mais ma miséricorde, je ne la retirerai pas de lui, comme je l’ai retirée de Saül, que j’ai écarté de ma face.
Amma ba za a taɓa ɗauke ƙaunata daga gare shi yadda na ɗauke ta daga wurin Shawulu ba, shi wannan wanda na kawar daga gabanka.
16 Et ta maison sera fidèle, et ton royaume éternellement devant ta face, et ton trône sera ferme à jamais.
Gidanka da kuma masarautarka za su dawwama har abada a gabana; gadon sarautarka kuma zai kahu har abada.’”
17 C’est selon toutes ces paroles, et suivant toute cette vision, que Nathan parla à David.
Natan ya gaya wa Dawuda dukan abin da Allah ya bayyana masa.
18 Or, le roi David entra, et il s’assit devant le Seigneur et dit: Que suis-je moi, Seigneur Dieu, et quelle est ma maison, pour que vous m’ayez conduit jusque-là?
Sa’an nan Sarki Dawuda ya je ya zauna a gaban Ubangiji ya ce, “Wane ne ni, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ko gidana, har da ka ɗaga mu zuwa wannan matsayi?
19 Mais cela même a paru peu, en votre présence, Seigneur Dieu, si vous ne parliez aussi de la maison de votre serviteur pour un long avenir; car c’est la loi d’Adam, Seigneur Dieu.
Har ya zama kamar wannan bai isa ba a gabanka, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ka kuma yi magana game da nan gaba na gidan bawanka. Haka ka saba yi da mutane, ya Ubangiji Mai Iko Duka?
20 Que pourra donc encore ajouter David, pour vous parler? car vous, Seigneur Dieu, vous connaissez votre serviteur.
“Me kuma Dawuda zai ce maka? Gama ka san bawanka, ya Ubangiji Mai Iko Duka.
21 À cause de votre parole et selon votre cœur vous avez fait toutes ces grandes œuvres, afin d’en donner connaissance à votre serviteur.
Gama saboda maganarka da kuma bisa ga nufinka, ka aikata wannan babban abu, ka kuma sanar da bawanka.
22 C’est pour cela que vous avez été exalté, Seigneur Dieu; car nul n’est semblable à vous, et il n’y a point de Dieu hors vous, selon tout ce que nous avons entendu de nos oreilles.
“Kai mai girma ne, ya Ubangiji Mai Iko Duka! Babu wani kamar ka, babu kuma wani Allah sai kai; kamar yadda muka ji da kunnuwanmu.
23 Mais quelle est la nation sur la terre comme votre peuple d’Israël, à cause de laquelle Dieu est allé pour la racheter comme son peuple, pour se faire un nom, et pour opérer au milieu d’eux des œuvres grandes et terribles sur la terre, à la face de votre peuple, que vous vous êtes racheté de l’Egypte, frappant une nation et son dieu.
Wane ne kuma yake kamar da mutanenka Isra’ila, al’umma guda a duniya wadda Allah ya fita don yă kuɓutar wa kansa, ya kuma yi suna wa kansa, ya kuma aikata manyan abubuwa da kuma al’amuran banmamaki ta wurin korin al’ummai da allolinsu daga gaban mutanenka, waɗanda ka kuɓutar daga Masar?
24 Car vous vous êtes assuré de votre peuple Israël comme d’un peuple perpétuel; et vous. Seigneur Dieu, vous êtes devenu leur Dieu.
Ka kafa mutanenka Isra’ila kamar naka na kanka har abada, kai kuma, ya Ubangiji, ka zama Allahnsu.
25 Maintenant donc. Seigneur Dieu, suscitez pour toujours la parole que vous avez dite sur votre serviteur et sur sa maison, et faites comme vous avez parlé,
“Yanzu kuwa, ya Ubangiji Allah, ka cika alkawarin da ka yi game da bawanka da gidansa. Ka yi kamar yadda ka alkawarta,
26 Afin que votre nom soit exalté à jamais, et que l’on dise: Le Seigneur Dieu des armées est Dieu sur Israël. Et la maison de votre serviteur David sera fermement établie devant le Seigneur,
domin sunanka yă kasance da girma har abada. Sa’an nan mutane za su ce, ‘Ubangiji Maɗaukaki, Allah ne a bisa Isra’ila!’ Kuma gidan bawanka Dawuda zai kahu a gabanka.
27 Parce que c’est vous, Seigneur des armées, Dieu d’Israël, qui avez ouvert l’oreille de votre serviteur, disant: Je te bâtirai une maison; à cause de cela votre serviteur a trouvé son cœur pour vous adresser cette prière.
“Ya Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, ka bayyana wa bawanka cewa, ‘Zan gina maka gida.’ Saboda haka bawanka ya sami ƙarfin hali yă miƙa maka wannan addu’a.
28 Maintenant donc, Seigneur Dieu, vous êtes Dieu, et vos paroles seront véritables; car vous avez dit à votre serviteur ces bonnes choses.
Ya Ubangiji Mai Iko Duka, kai Allah ne! Maganarka da aminci take, ka kuma yi wa bawanka waɗannan abubuwa masu kyau.
29 Commencez-donc, et bénissez la maison de votre serviteur, afin qu’elle soit à jamais devant vous, parce que c’est vous. Seigneur Dieu, qui avez parlé, et c’est de votre bénédiction que sera bénie la maison de votre serviteur à jamais.
In ya gamshe ka, bari ka albarkaci gidan bawanka don yă dawwama a gabanka har abada; gama kai, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ka riga ka yi magana, kuma saboda kai ka sa albarka ga gidan bawanka, lalle zai kasance da albarka har abada.”