< 2 Rois 9 >

1 Or le prophète Élisée appela un des enfants des prophètes, et lui dit: Ceins tes reins, prends ce petit vase d’huile en ta main et va à Ramoth-Galaad.
Sai Elisha ya kira wani daga cikin ƙungiyar annabawa, ya ce masa, “Ka sha ɗamara, ka ɗauki wannan kwalabar mai ka je Ramot Gileyad.
2 Et lorsque tu seras arrivé là, tu verras Jéhu, fils de Josaphat, fils de Namsi; et, étant entré, tu le feras sortir du milieu de ses frères, et tu l’introduiras dans une chambre secrète.
Da ka isa can, ka nemi Yehu ɗan Yehoshafat, ɗan Nimshi. Ka je wurinsa, ka ja shi gefe daga abokansa, ka shiga da shi ɗaki na ciki.
3 Et tenant le petit vase d’huile, tu la répandras sur sa tête, et tu diras: Voici ce que dit le Seigneur: Je t’ai oint roi sur Israël. Et tu ouvriras la porte, et tu t’enfuiras, et tu ne resteras pas là.
Sa’an nan ka ɗauki kwalabar man ka zuba a kansa, ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji ya faɗa, na naɗa ka sarkin Isra’ila.’ Sa’an nan ka buɗe ƙofa ka ruga a guje; kada ka ɓata lokaci!”
4 Le jeune homme, serviteur du prophète, s’en alla donc à Ramoth-Galaad,
Sai saurayin nan, annabi, ya tafi Ramot Gileyad.
5 Et il y entra: or, voilà que les princes de l’armée étaient assis; et il dit à Jéhu: J’ai un mot pour vous, ô prince. Et Jéhu demanda: Pour qui d’entre nous tous? Et celui-ci répondit: Pour vous, ô prince.
Da ya isa can, sai ya tarar da hafsoshin soji zaune a wuri guda. Sai ya ce, “Ina da saƙo dominka komanda.” Sai Yehu ya ce, “Wanne a cikinmu?” Sai ce, “Dominka, komanda.”
6 Alors il se leva, et il entra dans sa chambre, et le jeune homme répandit l’huile sur sa tête, et dit: Voici ce que dit le Seigneur, Dieu d’Israël: Je t’ai oint roi sur le peuple du Seigneur, Israël,
Sai Yehu ya tashi ya shiga cikin gida. Sa’an nan annabin ya zuba wa Yehu mai a kā, ya ce, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, ‘Na naɗa ka sarki a bisa jama’ar Ubangiji, wato, Isra’ila.
7 Et tu frapperas la maison d’Achab, ton seigneur, et je vengerai le sang de mes serviteurs, les prophètes, et le sang de tous les serviteurs du Seigneur, de la main de Jézabel.
Za aka hallaka gidan Ahab maigidanka, zan kuma ɗauki fansar jinin bayina annabawa da kuma jinin dukan bayin Ubangiji da Yezebel ta zub da.
8 Et je perdrai toute la maison d’Achab, et je tuerai d’Achab, celui qui urine contre une muraille, celui qui est renfermé, et celui qui est le dernier dans Israël.
Dukan gidan Ahab zai hallaka. Zan kashe dukan’ya’yan Ahab maza a Isra’ila, bayi ko’yantattu.
9 Et je rendrai la maison d’Achab comme la maison de Jéroboam, fils de Nabath, et comme la maison de Baasa, fils d’Ahia.
Zan mai da gidan Ahab kamar gidan Yerobowam ɗan Nebat da kuma kamar gidan Ba’asha ɗan Ahiya.
10 Et Jézabel elle-même, les chiens la mangeront dans la campagne de Jezrahel, et il n’y aura personne qui l’ensevelisse. Et il ouvrit la porte et s’enfuit.
Game da Yezebel kuwa, karnuka za su cinye ta a fili a Yezireyel, ba kuwa wanda zai binne ta.’” Sa’an nan ya buɗe ƙofa ya ruga a guje.
11 Mais Jéhu sortit vers les serviteurs de son maître, qui lui demandèrent: Tout va-t-il bien? Pourquoi cet insensé est-il venu vers vous? Jéhu leur dit: Vous connaissez cet homme et ce qu’il a pu dire.
Da Yehu ya koma wurin sauran hafsoshin sai ɗaya daga cikinsu ya tambaye shi, “Lafiya? Me ya kawo wannan mahaukaci a wurinka?” Sai Yehu ya ce, “Ka san mahaukacin nan da irin maganganunsa.”
12 Mais ceux-ci répondirent: C’est quelque chose de faux, mais au moins racontez-le nous. Jéhu leur dit: Il m’a dit ceci et cela, et il a ajouté: Voici ce que dit le Seigneur: Je t’ai oint roi sur Israël.
Suka ce masa, “Ba gaskiya ba ne, ka dai faɗa mana.” Yehu ya ce, “Ga abin da ya ce mini, ‘Ga abin da Ubangiji ya ce, na naɗa ka sarki a bisa Isra’ila.’”
13 C’est pourquoi ils se hâtèrent, et chacun prenant son manteau, ils le mirent sous les pieds de Jéhu, pour représenter un tribunal; puis ils sonnèrent de la trompette, et dirent: Jéhu est roi.
Sai suka yi sauri suka ɗauki rigunansu suka shimfiɗa a ƙasa, suka busa kakaki, suka yi ihu, suka ce, “Yehu ne sarki.”
14 Jéhu, fils de Josaphat, fils de Namsi, conspira donc contre Joram: or Joram avait assiégé Ramoth-Galaad, lui et tout Israël, contre Hazaël, roi de Syrie;
Saboda haka, Yehu ɗan Yehoshafat, ɗan Nimshi, ya ƙulla wa Yoram maƙarƙashiya (To, Yoram da dukan Isra’ila suna kāre Ramot Gileyad daga Hazayel sarkin Aram,
15 Et il était revenu pour se guérir à Jezrahel d’une blessure, parce que les Syriens l’avaient blessé, lorsqu’il combattait contre Hazaël, roi de Syrie; et Jéhu dit: S’il vous plaît, que personne ne sorte, fuyant de la ville, afin qu’il n’aille et ne l’annonce à Jezrahel.
amma Sarki Yoram ya koma Yezireyel don yă farfaɗo daga raunukan da Arameyawa suka ji masa a wata gabzawar da ya yi da Hazayel sarkin Aram.) Yehu ya ce, “In haka kuke ji, kada ku bar wani yă sulluɓe daga birnin yă kai labarin Yezireyel.”
16 Et il monta et partit pour Jezrahel; car Joram était là malade; et Ochozias, roi de Juda, était descendu pour visiter Joram.
Sai ya tashi ya ɗauki keken yaƙinsa ya tafi Yezireyel gama Yoram yana hutawa a can. Ga kuma Ahaziya sarkin Yahuda ya je don yă gan shi.
17 La sentinelle donc qui était sur la tour de Jezrahel, vit la troupe de Jéhu qui venait, et dit: J’aperçois une troupe, et Joram dit: Prends un chariot et envoie à leur rencontre, et que celui qui ira dise: Tout va-t-il bien?
Mai tsaro kuwa yana tsaye a kan hasumiya a Yezireyel, sai ya hangi rundunar Yehu sa’ad da yake zuwa. Ya ce, “Na ga wata runduna.” Sai Yoram ya umarta, “Nemi mahayin doki a aike shi yă tarye su, yă kuma tambaye su, ‘Lafiya?’”
18 Celui donc qui était monté sur le char, alla à la rencontre de Jéhu, et dit: Voici ce que dit le roi: Tout est-il en paix? Et Jéhu répondit: Qu’importe à toi et à la paix? passe, et suis-moi. La sentinelle l’annonça aussi, disant: Le messager est allé vers eux, et il ne revient point.
Sai mahayin dokin ya hau, ya ruga, ya taryi Yehu, ya ce, “Ga abin da sarki ya ce, ‘Lafiya?’” Sai Yehu ya ce masa, “Ina ruwanka da zancen lafiya? Ka shiga layi.” Sai mai tsaron ya ce wa sarki, “Ɗan saƙon ya kai wurinsu, amma ba ya dawowa.”
19 Joram envoya encore un second chariot avec des chevaux; et le messager alla vers eux, et dit: Voici ce que dit le roi: Est-ce la paix? Et Jéhu répondit: Qu’importe à toi et à la paix? Passe, et suis-moi.
Saboda haka sarki ya sāke aika mahayin doki na biyu. Sa’ad da ya isa wurinsu sai ya ce, “Ga abin da sarki ya ce, ‘Lafiya?’” Yehu ya ce, “Ina ruwanka da zancen lafiya? Ka shiga layi.”
20 Or la sentinelle l’annonça, disant: Il est allé jusqu’à eux, et il ne revient point; mais la démarche de quelqu’un qui vient, est comme la démarche de Jéhu, fils de Namsi; car il marche avec précipitation.
Mai tsaro ya sāke cewa, “Ya kai wurinsu, amma shi ma ba ya dawowa. Ina ganin sukuwar kamar irin ta Yehu, jikan Nimshi, gama yakan yi sukuwa kamar mahaukaci.”
21 Et Joram dit: Attelle mon char. Et l’on attela son char, et Joram, roi d’Israël, sortit, et Ochozias, roi de Juda, chacun dans son char, et ils sortirent à la rencontre de Jéhu, et le trouvèrent dans le champ de Naboth, le Jezrahélite.
Yoram ya umarta, “Haɗa mini keken yaƙi!” Da aka haɗa, sai Yoram sarkin Isra’ila, da Ahaziya sarkin Yahuda, suka hau suka tafi, kowa a keken yaƙinsa, don su taryi Yehu. Suka sadu da shi a filin da yake na Nabot mutumin Yezireyel.
22 Et lorsque Joram eut vu Jéhu, il dit: Est-ce la paix, Jéhu? Mais celui-ci répondit: Quelle est cette paix? Les fornications de Jézabel votre mère et ses enchantements nombreux subsistent encore.
Sa’ad da Yoram ya ga Yehu sai ya tambaye shi, “Lafiya kuwa ka zo, Yehu?” Yehu ya ce, “Ina kuwa lafiya, da yake dukan bautar gumaka da bokancin mahaifiyarka Yezebel sun bazu ko’ina?”
23 Or Joram tourna sa main, et, fuyant, il dit à Ochozias: C’est un piège, Ochozias.
Yoram ya juya, ya gudu, yana ce wa Ahaziya, “Cin amana, Ahaziya!”
24 Mais Jéhu tendit son arc de sa main et frappa Joram entre les épaules; et la flèche sortit par son cœur, et aussitôt il tomba sur son char.
Sai Yehu ya ja bakansa ya harbi Yoram a tsakanin kafaɗunsa. Kibiyar ta same shi a zuciyarsa sai ya fāɗi a cikin keken yaƙinsa.
25 Alors Jéhu dit à Badacer, chef de l’armée: Prends-le et jette-le dans le champ de Naboth, le Jezrahélite; car je me souviens, quand moi et toi, assis sur un char, nous suivions Achab, son père, que le Seigneur leva sur lui ce fardeau, disant:
Yehu ya ce wa Bidkar, hafsan keken yaƙinsa, “Ka ɗauke shi ka jefar a filin da yake na Nabot mutumin Yezireyel. Ka tuna yadda ni da kai muke a kekunan yaƙi a bayan Ahab mahaifinsa sa’ad da Ubangiji ya yi wannan annabci game da shi,
26 Je jure, si pour le sang de Naboth et pour le sang de ses fils, que j’ai vu hier verser, dit le Seigneur, je ne te rends point la pareille dans ce champ, dit le Seigneur. Maintenant donc, prends-le, et jette-le dans le champ, selon la parole du Seigneur.
‘Jiya na ga jinin Nabot da jinin’ya’yansa, in ji Ubangiji, kuma ba shakka zan ɗauki fansa a wannan fili, in ji Ubangiji.’ Saboda haka, ka ɗauke shi ka jefar da shi a bisa wannan fegi, bisa ga faɗin Ubangiji. Saboda haka, ka ɗauke shi ka jefar a filin, in ji Ubangiji.”
27 Or Ochozias, roi de Juda, ayant vu cela, s’enfuit par le chemin de la maison du jardin, et Jéhu le poursuivit et dit: Même celui-là, frappez-le sur son char. Et ils le frappèrent à la montée de Gaver, qui est près de Jéblaam, et Ochozias s’enfuit à Mageddo et mourut là.
Sa’ad da Ahaziya sarkin Yahuda ya ga abin da ya faru, sai ya haura hanyar Bet Haggan a guje. Yehu ya bi shi yana ihu, “A kashe shi, shi ma!” Suka ji masa rauni a keken yaƙinsa a hanya zuwa Gur, kusa da Ibileyam amma ya tsere zuwa Megiddo ya mutu a can.
28 Et ses serviteurs le placèrent sur son char, et le portèrent à Jérusalem, et l’ensevelirent dans le sépulcre avec ses pères dans la cité de David.
Barorinsa suka ɗauke shi cikin keken yaƙi zuwa Urushalima suka binne shi a kabarinsa tare da kakanninsa a birnin Dawuda.
29 La onzième année de Joram, fils d’Achab, Ochozias régna sur Juda,
(A shekara ta goma sha ɗaya ta Yoram ɗan Ahab, Ahaziya ya zama sarkin Yahuda.)
30 Et Jéhu vint à Jezrahel. Or Jézabel, ayant appris son arrivée, peignit ses yeux avec du noir et orna sa tête, puis elle regarda par la fenêtre
Sa’an nan Yehu ya je Yezireyel. Sa’ad da Yezebel ta sami labari, sai ta sha kwalliya ta gyara gashin kanta, ta zauna tana kallo daga taga.
31 Jéhu qui entrait à la porte, et dit: Est-ce que la paix peut être avec Zambri qui a tué son maître?
Yayinda Yehu ya shiga ƙofa, sai ta ce, “Lafiya, kai Zimri, mai kashe maigidansa?”
32 Et Jéhu leva sa face vers la fenêtre, et demanda: Qui est celle-là? Et deux ou trois eunuques se penchèrent vers lui.
Sai ya ɗaga ido ya dubi tagan ya ce, “Wa yake gefena? Wane ne?” Sai bābānni biyu ko uku suka leƙo suka dube shi.
33 Et Jéhu leur dit: Précipitez-la en bas. Et ils la précipitèrent, et la muraille fut arrosée de son sang, et la corne des chevaux la foula.
Yehu ya ce musu, “Ku jefa ta ƙasa!” Sai suka jefar da ita, jininta ya fantsama a jikin bango da kuma a jikin dawakai yayinda suke tattaka ta.
34 Et lorsque Jéhu fut entré pour boire et pour manger, il dit: Allez, et voyez cette maudite, et ensevelissez-la, parce qu’elle est fille de roi.
Yehu ya shiga ya ci, ya kuma sha. Ya ce, “Ku san yadda za ku yi da la’ananniyan nan, ku binne ta, gama’yar sarki ce.”
35 Et lorsqu’ils furent allés pour l’ensevelir, ils ne trouvèrent que le crâne, les pieds et l’extrémité des mains.
Amma sa’ad da suka je don su binne ta, ba su sami kome ba sai ƙoƙon kanta, ƙafafunta da kuma hannuwanta.
36 Et étant revenus, ils l’annoncèrent à Jéhu. Or Jéhu dit: C’est la parole du Seigneur, qu’il a prononcée par son serviteur Élie, le Tesbite, disant: Dans la campagne de Jezrahel, les chiens mangeront la chair de Jézabel,
Suka komo suka faɗa wa Yehu, wanda ya ce, “Wannan ita ce maganar da Ubangiji ya faɗa ta bakin bawansa Iliya mutumin Tishbe. A fili, a Yezireyel, karnuka za su cinye naman Yezebel.
37 Et la chair de Jézabel sera comme un fumier sur la face de la terre, dans la campagne de Jezrahel; et tous ceux qui passeront diront: Est-ce là cette Jézabel?
Gawar Yezebel zai zama kamar juji a ƙasa, a fili, a Yezireyel, har ba wanda zai iya cewa, ‘Wannan Yezebel ce.’”

< 2 Rois 9 >