< 2 Rois 16 >
1 En la dix-septième année de Phacée, fils de Romélie, régna Achaz, fils de Joatham, roi de Juda,
A shekara ta goma sha bakwai ta mulkin Feka ɗan Remaliya, Ahaz ɗan Yotam sarkin Yahuda ya fara mulki.
2 Achaz avait vingt ans lorsqu’il commença à régner, et il régna seize ans à Jérusalem: il ne fit point ce qui était agréable en la présence du Seigneur son Dieu, comme David son père;
Ahaz ya zama sarki yana da shekara ashirin, ya kuma yi mulki shekara goma sha shida a Urushalima ba kamar Dawuda mahaifinsa ba. Ahaz bai yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji Allahnsa ba.
3 Mais il marcha dans la voie des rois d’Israël; de plus il consacra même son fils, le faisant passer par le feu, selon le culte des idoles des nations qu’avait dissipées le Seigneur devant les enfants d’Israël.
Ya yi tafiya a hanyoyin sarakunan Isra’ila har ya miƙa ɗansa hadaya a wuta, yana bin hanyoyin banƙyama na al’ummai da Ubangiji ya kora a gaban Isra’ilawa.
4 Il immolait aussi des victimes, et offrait de l’encens sur les hauts lieux, sur les collines, et sous tout arbre couvert de feuillage.
Ya miƙa hadaya, ya kuma ƙona turare a masujadan tudu, da kan tuddai, da kuma a ƙarƙashin kowane babban itace.
5 Alors Rasin, roi de Syrie, et Phacée, fils de Romélie, roi d’Israël, montèrent à Jérusalem pour livrer bataille, et quoiqu’ils tinssent Achaz assiégé, ils ne purent pas le vaincre.
Sai Rezin sarkin Aram, da Feka ɗan Remaliya sarkin Isra’ila suka haura don su kai wa Urushalima hari, suka kuma kewaye Ahaz, amma ba su iya shan ƙarfinsa ba.
6 En ce temps-là, Rasin, roi de Syrie, rendit Aila à la Syrie, et chassa les Juifs d’Aila; et les Iduméens vinrent à Aila, et ils y ont habité jusqu’à ce jour.
A wannan lokaci, Rezin sarkin Aram ya sāke ƙwato Elat wa Aram ta wurin korar Yahuda. Sa’an nan mutanen Edom suka mamaye Elat suna kuwa zaune a can har yau.
7 Alors Achaz envoya des messagers à Théglathphalasar, roi des Assyriens, disant: Je suis votre serviteur et votre fils; montez, sauvez-moi de la main du roi de Syrie et de la main du roi d’Israël, qui se sont levés ensemble contre moi.
Ahaz ya aika a faɗa wa Tiglat-Fileser sarkin Assuriya cewa, “Ni abokin tarayyarka ne kuma mai dogara da kai. Ka haura ka cece ni daga hannun sarkin Aram da hannun sarkin Isra’ila waɗanda suke kawo mini hari.”
8 Et ayant amassé l’argent et l’or qui put être trouvé dans la maison du Seigneur et dans les trésors du roi, il envoya au roi des Assyriens des présents.
Ahaz ya ɗauki azurfa da zinariyar da suke a haikalin Ubangiji da suke kuma a ma’ajin fada ya aika wa sarkin Assuriya kyauta.
9 Celui-ci acquiesça à sa volonté: le roi des Assyriens, en effet, monta à Damas, et la ravagea; il en transféra les habitants à Cyrène, mais il tua Rasin.
Sai sarkin Assuriya ya ji roƙonsa. Ya tashi ya fāɗa wa Damaskus da hari ya kuma kame ta. Ya kwashi mazaunanta zuwa Kir, ya kuma kashe Rezin.
10 Alors le roi Achaz alla à la rencontre de Théglathphalasar, roi des Assyriens, à Damas; et lorsqu’il eut vu l’autel de Damas, le roi Achaz en envoya au prêtre Urie le modèle et la représentation d’après tout le travail de cet autel.
Sa’an nan sarki Ahaz ya tafi Damaskus don yă sadu da Tiglat-Fileser sarkin Assuriya. Da ya kai can sai ya ga wani bagade a Damaskus, sai ya aika wa Uriya firist, da siffar bagaden, da fasalinsa, da cikakken bayanin bagaden.
11 Urie, le prêtre, construisit donc l’autel; selon tout ce que le roi Achaz avait ordonné de Damas, ainsi fit le prêtre Urie, jusqu’à ce que le roi Achaz vint de Damas.
Saboda haka Uriya firist ya gina bagaden bisa ga tsarin da Sarki Ahaz ya aika masa daga Damaskus, ya kuma gama shi kafin Sarki Ahaz yă dawo.
12 Et lorsque le roi fut venu de Damas, il vit cet autel, et il le révéra; puis il monta, et immola les holocaustes, et son sacrifice;
Da sarki ya dawo daga Damaskus ya ga bagaden, sai ya tafi kusa da shi ya kuma miƙa hadaya a bisansa.
13 Et il fit des libations, et répandit le sang des hosties pacifiques qu’il avait offertes sur l’autel.
Ya miƙa hadayarsa ta ƙonawa da ta hatsi, ya zuba hadayarsa ta sha, ya kuma yayyafa jinin hadayunsa ta zumunci a bisa bagaden.
14 Quant à l’autel d’airain qui était devant le Seigneur, il le transféra de devant la face du temple, de la place de l’autel et de la place du temple du Seigneur, et il le mit à côté de l’autel, vers l’aquilon.
Sai ya cire bagaden tagulla wanda aka keɓe ga Ubangiji, ya sa shi a gaban haikalin wato, tsakanin ƙofar shiga haikalin Ubangiji da sabon bagaden. Ya ajiye shi a gefen arewa na sabon bagaden.
15 Le roi Achaz ordonna aussi à Urie, le prêtre, disant: Offre sur le grand autel l’holocauste du matin et le sacrifice du soir, l’holocauste du roi et son sacrifice, l’holocauste de tout le peuple, leurs sacrifices et leurs libations; mais tout le sang des holocaustes et tout le sang des victimes, tu le répandras sur cet autel; et quant à l’autel d’airain, il sera préparé selon ma volonté.
Sarkin Ahaz ya umarci Uriya cewa, “A kan babban sabon bagade, ka miƙa hadayar ƙonawa ta safe, da hadayar hatsi ta yamma, da hadayar sarki ta ƙonawa da hadayarsa ta hatsi, da hadaya ta dukan jama’ar ƙasar, tare da hadayan hatsinsu da kuma ta sha. Ka yayyafa jinin hadayun ƙonawa a kan bagade. Amma zan yi amfani da bagaden tagulla don neman bishewa.”
16 Ainsi Urie, le prêtre, fit tout selon ce qu’avait ordonné le roi Achaz.
Uriya firist kuwa ya yi duk abin da Sarki Ahaz ya umarta.
17 Or le roi Achaz enleva les bases ciselées et le bassin qui était dessus, et il ôta la mer de dessus les bœufs d’airain, qui la soutenaient, et il la mit sur le pavé, qui était de pierre.
Sarkin Ahaz ya kawar da katakon ya kuma ɗauke tasoshin daga mazauninsu da ake iya matsarwa. Ya ɗauke ƙaton kwano mai suna Teku daga kan bijiman tagullar da ya tallafe su ya ajiye a kan mazaunin dutse.
18 Même le Musach du sabbat, qu’il avait bâti dans le temple, et l’entrée extérieure du roi, il les transporta dans le temple du Seigneur, à cause du roi des Assyriens.
Ya kawar da rumfa Asabbacin da aka gina a haikalin, ya kuma kawar da mashigin sarki na waje da haikalin Ubangiji, duk dai don yă gamshi sarkin Assuriya.
19 Mais le reste des actions d’Achaz, qu’il a faites, n’est-il pas écrit dans le Livre des actions des jours des rois de Juda?
Game da sauran ayyukan mulkin Ahaz, abubuwan da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
20 Et Achaz dormit avec ses pères, et fut enseveli avec eux dans la cité de David, et Ezéchias, son fils, régna en sa place.
Ahaz ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi da su a Birnin Dawuda. Hezekiya ɗansa kuma ya gāje shi.