< 2 Rois 14 >

1 En la seconde année de Joas, fils de Joachaz, roi d’Israël, régna Amasias, fils de Joas, roi de Juda.
A shekara ta biyu ta mulkin Yehowash ɗan Yehoyahaz sarkin Isra’ila, Amaziya ɗan Yowash sarkin Yahuda ya fara mulki.
2 Il avait vingt-cinq ans lorsqu’il commença à régner; et il régna vingt-neuf ans dans Jérusalem; le nom de sa mère était Joadan de Jérusalem.
Ya zama sarki yana da shekaru ashirin da biyar, ya kuma yi mulki a Urushalima shekaru ashirin da tara. Sunan mahaifiyarsa Yehoyaddin, mutuniyar Urushalima.
3 Et il fit ce qui était droit devant le Seigneur, cependant non pas comme David, son père. Il fit selon tout ce que Joas son père avait fait;
Ya aikata abin da yake daidai a gaban Ubangiji, sai dai ba kamar kakansa Dawuda ba. A kome dai ya bi gurbin mahaifinsa Yowash.
4 Si ce n’est seulement qu’il n’abolit point les hauts lieux, car le peuple sacrifiait encore et brûlait de l’encens sur les hauts lieux.
Ba a dai kawar da masujadan kan tudu ba; mutane suka ci gaba da yin hadaya da ƙone turare a can.
5 Et lorsqu’il eut obtenu le royaume, il frappa de mort ses serviteurs qui avaient tué le roi, son père;
Bayan masarauta ta kahu a hannunsa, sai ya kashe fadawan da suka kashe mahaifinsa sarki.
6 Mais les enfants de ceux qui avaient commis le meurtre, il ne les tua points selon ce qui est écrit au livre de la loi de Moïse, et comme a ordonné le Seigneur, disant: Des pères ne mourront pas pour des enfants, et des enfants ne mourront point pour des pères; mais chacun mourra pour son péché.
Duk da haka bai kashe’ya’yan masu kisan ba, bisa ga abin da yake a rubuce a Dokar Musa inda Ubangiji ya umarta, “Ba za a kashe iyaye saboda laifin’ya’ya ba, ko kuma’ya’ya saboda laifin iyayensu ba, kowa zai mutu don zunubansa.”
7 Ce fut lui qui battit Edom dans la vallée des Salines, tuant dix mille hommes, et il prit le rocher dans cette bataille, et il l’appela du nom de Jectéhel, jusqu’au présent jour.
Shi ne kuma wanda ya ci mutanen Edom dubu goma a yaƙi, a Kwarin Gishiri, ya kuma ci Sela da yaƙi, ya ba ta suna Yokteyel, sunan da ake kiranta har wa yau.
8 Alors Amasias envoya des messagers vers Joas, fils de Joachaz, fils de Jéhu, roi d’Israël, disant: Venez, et voyons-nous.
Sai Amaziya ya aika’yan aika wurin Yehowash ɗan Yehoyahaz, ɗan Yehu, sarkin Isra’ila, yana tsokanarsa cewa, “Zo, mu sadu fuska da fuska.”
9 Et Joas, roi d’Israël, envoya à son tour vers Amasias, roi de Juda, disant: Le chardon du Liban envoya vers le cèdre qui est au Liban, disant: Donnez votre fille à mon fils pour femme. Et les bêtes de la forêt qui sont au Liban passèrent, et foulèrent aux pieds le chardon.
Amma Yehowash sarkin Isra’ila ya mai da martani wa Amaziya sarkin Yahuda ya ce, “Wata’yar ƙaya a kurmin Lebanon ta aika da saƙo wurin itacen al’ul a Lebanon cewa, ‘Ka ba ɗana’yarka aure.’ Amma wani naman jeji ya zo ya tattake ƙayar.
10 Vous l’avez emporté sur Edom, en le battant, et votre cœur vous a élevé. Soyez content de cette gloire, et restez dans votre maison. Pourquoi provoquez-vous un malheur, pour que vous tombiez, vous et Juda avec vous?
Tabbatacce ka ci Edom da yaƙi, yanzu kuwa kana ɗaga kai. To, ka gode da darajar da ka samu, amma ka zauna a gida! Don me kake neman faɗa kana neman fāɗuwarka da kuma ta Yahuda?”
11 Mais Amasias ne l’écouta pas; et Joas, roi d’Israël, monta contre lui, et ils se virent, lui et Amasias, roi de Juda, à Bethsamès, ville de Juda.
Amma Amaziya bai saurara ba, saboda haka Yehowash sarkin Isra’ila ya kai masa hari. Shi da Amaziya sarkin Yahuda suka fuskanci juna a Bet-Shemesh.
12 Et Juda fut vaincu par Israël, et ils s’enfuirent, chacun dans leurs tabernacles.
Isra’ila suka fatattaki Yahuda, kowa kuwa ya tsere zuwa gidansa.
13 Mais Joas, roi d’Israël, prit à Bethsamès, Amasias, roi de Juda, fils de Joas, fils d’Ochozias, et l’emmena à Jérusalem; et il perça le mur de Jérusalem, depuis la porte d’Ephraïm jusqu’à la porte de l’angle, espace de quatre cents coudées.
Yehowash sarkin Isra’ila ya kama Amaziya sarkin Yahuda, ɗan Yowash, ɗan Ahaziya, a Bet-Shemesh. Sa’an nan Yehowash ya tafi Urushalima ya rushe katangar Urushalima daga Ƙofar Efraim har zuwa Ƙofar Kusurwa, ratarta ta kai wajen ƙafa ɗari shida.
14 Et il emporta tout l’or et l’argent, tous les vases qui furent trouvés dans la maison du Seigneur, et dans tous les trésors du roi, et les otages, et il retourna à Samarie.
Ya kwashi ɗaukan zinariya da azurfa da duk kayan da aka samu a haikalin Ubangiji da kuma ma’ajin fadan. Ya kuma kwashi bayi sa’an nan ya koma Samariya.
15 Mais le reste des actions de Joas, et son courage avec lequel il combattit contre Amasias, roi de Juda, n’est-ce pas écrit dans le Livre des actions des jours des rois d’Israël?
Game da sauran ayyukan mulkin Yehowash, abin da ya yi da kuma nasarorinsa, haɗe da yaƙinsa da Amaziya sarkin Yahuda, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
16 Et Joas dormit avec ses pères, et fut enseveli à Samarie avec les rois d’Israël; et Jéroboam, son fils, régna en sa place.
Ya huta da kakanninsa aka kuma binne shi a Samariya tare da sarakunan Isra’ila. Yerobowam ɗansa, ya kuma gāje shi.
17 Mais Amasias, fils de Joas, roi de Juda, vécut quinze ans après que fut mort Joas, fils de Joachaz, roi d’Israël.
Amaziya ɗan Yowash sarkin Yahuda ya yi shekaru goma sha biyar bayan mutuwar Yehowash ɗan Yehoyahaz sarkin Isra’ila.
18 Mais le reste des actions d’Amasias n’est-il pas écrit dans le Livre des actions des jours des rois de Juda?
Game da sauran ayyukan mulkin Amaziya, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
19 Et il se fit une conspiration contre lui à Jérusalem; mais lui s’enfuit à Lachis. Et on envoya après lui à Lachis, et on le tua là.
Suka ƙulla masa maƙarƙashiya a Urushalima, ya gudu zuwa Lakish, amma suka aika har Lakish aka kashe shi a can.
20 On transporta son cadavre sur les chevaux, et il fut enseseveli avec ses pères dans la cité de David.
Aka ɗauko shi a kan doki aka kawo shi Urushalima, aka kuwa binne shi tare da kakanninsa, a Birnin Dawuda.
21 Tout le peuple prit ensuite Azarias, âgé de seize ans, et ils l’établirent roi en la place de son père Amasias.
Sa’an nan dukan mutanen Yahuda suka ɗauki Azariya, wanda yake ɗan shekaru goma sha shida da haihuwa, suka naɗa shi sarki a madadin mahaifinsa Amaziya.
22 Ce fut lui qui bâtit Elath, et la rendit à Juda, après que le roi se fut endormi avec ses pères.
Shi ne ya sāke gina Elat, ya kuma maido da ita a hannun Yahuda bayan Amaziya ya huta da kakanninsa.
23 En la quinzième année d’Amasias, fils de Joas, roi de Juda, Jéroboam, fils de Joas, roi d’Israël, régna à Samarie, et il régna quarante-un ans;
A shekara ta goma sha biyar ta mulkin Amaziya ɗan Yowash sarkin Yahuda, Yerobowam ɗan Yehowash sarkin Isra’ila ya zama sarki a Samariya, ya kuma yi mulki na shekaru arba’in da ɗaya.
24 Et il fit le mal devant le Seigneur. Il ne s’écarta pas de tous les péchés de Jéroboam, fils de Nabath, qui fit pécher Israël.
Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji bai kuwa kauce wa duk zunuban Yerobowam ɗan Nebat, wanda ya sa Isra’ila ta aikata ba.
25 C’est lui qui rétablit les limites d’Israël depuis l’entrée d’Emath jusqu’à la mer du désert, selon la parole que le Seigneur Dieu d’Israël avait dite par son serviteur Jonas, le prophète, fils d’Amathi, qui était de Geth, qui est en Opher.
Shi ne ya maido da iyakokin Isra’ila daga Lebo Hamat zuwa Tekun Araba, bisa ga maganar Ubangiji, Allah na Isra’ila, da ya yi ta bakin bawansa Yunana ɗan Amittai, annabi daga Gat-Hefer.
26 Car le Seigneur vit l’affliction très amère d’Israël, et qu’ils étaient consumés jusqu’à ceux qui étaient renfermés dans la prison, et jusqu’aux derniers du peuple, et qu’il n’y avait personne qui secourût Israël.
Ubangiji ya ga irin muguwar wahalar da ta shafi kowa a Isra’ila, ko bawa ko’yantacce, babu mai taimakonsu.
27 Et le Seigneur ne dit pas qu’il effacerait le nom d’Israël de dessous le ciel; mais il les sauva par la main de Jéroboam, fils de Joas.
Da yake kuma Ubangiji bai ce zai shafe sunan Isra’ila daga fuskar duniya ba, sai ya cece su ta hannun Yerobowam ɗan Yowash.
28 Mais le reste des actions de Jéroboam, tout ce qu’il a fait, son courage avec lequel il combattit, et comment il rendit Damas et Emath à Juda en Israël, n’est-ce pas écrit dans le Livre des actions des jours des rois d’Israël?
Game da sauran ayyukan mulkin Yerobowam, da dukan abin da ya yi, da yaƙe-yaƙen da ya yi, haɗe da sāke ƙwato wa Isra’ila Damaskus da Hamat waɗanda suke a hannun Yahuda, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
29 Et Jéroboam dormit avec ses pères, les rois d’Israël, et Zacharie, son fils, régna en sa place.
Yerobowam ya huta da kakanninsa, sarakunan Isra’ila. Zakariya ɗansa kuwa ya gāje shi.

< 2 Rois 14 >