< 2 Rois 10 >
1 Or Achab avait soixante-dix fils dans Samarie: Jéhu écrivit donc des lettres, et il les envoya à Samarie aux grands de la ville, aux anciens et à ceux qui élevaient les enfants d’Achab, disant:
To, akwai’ya’ya maza saba’in na gidan Ahab a Samariya. Saboda haka Yehu ya rubuta wasiƙu, ya aika su Samariya, zuwa ga shugabannin Yezireyel, da kuma ga masu lura da’ya’yan Ahab. Ya ce,
2 Aussitôt que vous aurez reçu ces lettres, vous qui avez les enfants de votre maître, les chars, les chevaux, les villes fortes et les armes,
“Da zarar wasiƙan nan ta sadu da ku, da yake’ya’yan maigidanku suna tare da ku, kuna kuma da kekunan yaƙi da dawakai, da birni mai katanga da makamai,
3 Choisissez le meilleur et celui qui vous plaira davantage, d’entre les fils de votre maître, et mettez-le sur le trône de son père, et combattez pour la maison de votre maître.
sai ku zaɓi mafi cancanta a cikin’ya’yan maigidanku ku sa shi a kan kursiyin mahaifinsa. Sa’an nan ku yi yaƙi don gidan maigidanku.”
4 Ceux-ci furent saisis d’une grande crainte, et ils dirent: Voilà que deux rois n’ont pu subsister devant lui, et comment nous, pourrons-nous résister?
Amma suka razana suka ce, “Idan sarakuna biyu ba su iya yin tsayayya da shi ba, wane mu?”
5 Les intendants de la maison du roi, les chefs de la ville, les anciens et ceux qui élevaient les princes, envoyèrent donc vers Jéhu, disant: Nous sommes vos serviteurs, tout ce que vous nous commanderez, nous le ferons; nous ne nous établirons point de roi: tout ce qu’il vous plaît, faites-le.
Saboda haka sarkin fada, da gwamnan birnin, da dattawa, da kuma masu lura da’ya’yan suka aika da saƙo ga Yehu, cewa, “Mu bayinka ne, za mu kuma yi duk abin da ka ce. Ba za mu naɗa kowa sarki ba; sai ka yi abin da ka ga ya fi kyau.”
6 Or il leur écrivit des lettres une seconde fois, disant: Si vous êtes à moi, et que vous vouliez m’obéir, coupez les têtes des fils de votre maître, et venez vers moi à cette même heure demain, à Jezrahel. Or, les fils du roi, soixante-dix individus étaient élevés chez les grands de la ville.
Sai Yehu ya sāke rubuta musu wasiƙa ta biyu, ya ce, “In a gefena kuke, to, sai ku yi biyayya da ni, ku fille kawunan’ya’yan maigidanku, ku kawo mini a Yezireyel war haka gobe.” To,’ya’yan sarki, su saba’in, suna tare da manyan birni waɗanda suke lura da su.
7 Et lorsque les lettres leur furent parvenues, ils prirent les fils du roi, et tuèrent ces soixante dix individus; ils mirent leurs têtes dans les corbeilles, et les envoyèrent à Jezrahel.
Sa’ad da wasiƙar ta iso, sai mutanen nan suka ɗauki dukan’ya’yan sarkin nan saba’in, suka kashe su, suka sa kawunansu cikin kwanduna, suka aika wa Yehu a Yezireyel.
8 Or le messager vint et l’annonça à Jéhu, disant: Ils ont apporté les têtes des enfants du roi. Jéhu répondit: Mettez-les en deux tas à l’entrée de la porte jusqu’au matin.
Da ɗan saƙon ya iso, sai aka ce wa Yehu, “Sun kawo kawunan’ya’yan sarki.” Sai Yehu ya ce, “Ku ajiye su kashi biyu a ƙofar gari har safiya.”
9 Et lorsqu’il fit jour, il sortit, et s’arrêtant, il dit à tout le peuple: Vous êtes justes; si c’est moi qui ai conspiré contre mon maître, et si je l’ai tué, qui est celui qui a frappé tous ceux-ci?
Da gari ya waye, sai Yehu ya fita ya tsaya a gaban dukan jama’a ya ce, “Ba ku da laifi. Ni ne na ƙulla wa maigidana maƙarƙashiya, na kuma kashe shi, amma wa ya karkashe dukan waɗannan?
10 Voyez donc maintenant qu’il n’est tombé par terre aucune des paroles du Seigneur, que le Seigneur a prononcées contre la maison d’Achab, et que le Seigneur a fait ce qu’il a dit par l’entremise de son serviteur Élie.
Ku sani fa, ba kalmar da Ubangiji ya faɗa game da gidan Ahab da ba za tă cika ba. Ubangiji ya yi abin da ya alkawarta ta bakin bawansa Iliya.”
11 Jéhu frappa donc tous ceux qui restaient de la maison d’Achab dans Jezrahel, tous les grands de sa cour, ses familiers et ses prêtres, jusqu’à ce qu’il ne demeurât pas de restes de lui.
Saboda haka Yehu ya kashe duk waɗanda suka rage na iyalin Ahab a Yezireyel, tare da dukan fadawansa da aminansa da firistocinsa, ba a bar masa kowa ba.
12 Et il se leva et il vint à Samarie; et lorsqu’il fut venu près de la Cabane des pasteurs, en son chemin,
Sa’an nan Yehu ya nufi Samariya. Da ya kai Bet-Eked na Makiyaya,
13 Il trouva les frères d’Ochozias, roi de Juda, et il leur demanda: Qui êtes-vous? Ceux-ci répondirent: Nous sommes les frères d’Ochozias, et nous sommes descendus pour saluer les fils du roi et les fils de la reine.
sai ya gamu da waɗansu daga dangin Ahaziya sarkin Yahuda, sai ya tambaye su, ya ce, “Ku, su wane ne?” Suka ce, “Mu dangin Ahaziya ne, mun kuma zo ne mu gai da iyalan sarki da kuma mahaifiyar sarauniya.”
14 Et Jéhu dit: Prenez-les vivants. Et, lorsqu’ils les eurent pris vivants, ils les égorgèrent sur une citerne près de la Cabane, au nombre de quarante-deux hommes, et il n’en resta pas un seul.
Sai ya umarta ya ce, “A kama su da rai!” Aka kuwa kama su aka yayyanka kusa da rijiyar Bet-Eked, su arba’in da biyu. Ba a bar wani da rai ba.
15 Et lorsqu’il fut parti de là, il trouva Jonadab, fils de Réchab, à sa rencontre; et il lui souhaita toute sorte de prospérités. Il lui demanda ensuite: Est-ce que ton cœur est droit, comme mon cœur avec ton cœur? Et Jonadab répondit: m’est. S’il l’est, reprit-il, donne la main. Celui-ci lui donna sa main. Alors Jéhu le fit monter auprès de lui dans son char.
Bayan ya bar wurin, sai ya gamu da Yehonadab ɗan Rekab wanda yake kan hanyarsa don yă sadu da shi. Sai Yehu ya gaishe shi, ya ce, “Ka amince da ni yadda na amince da kai?” Yehonadab ya ce, “I.” Yehu ya ce, “To, in haka ne ka ba ni hannunka.” Sai ya miƙa masa, Yehu kuwa ya ja shi cikin keken yaƙin.
16 Et il lui dit: Viens avec moi, et vois mon zèle pour le Seigneur. Et l’ayant mis dans son char,
Yehu ya ce, “Zo tare da ni ka ga himmata saboda Ubangiji.” Sa’an nan ya sa suka tafi tare cikin keken yaƙinsa.
17 Il les conduisit à Samarie. Or il tua tous ceux qui étaient restés d’Achab à Samarie, jusqu’au dernier, selon la parole que le Seigneur avait dite par Elle.
Da Yehu ya isa Samariya, sai ya karkashe dukan sauran iyalin Ahab, ya hallaka su, bisa ga maganar da Ubangiji ya faɗa ta bakin Iliya.
18 Ensuite Jéhu assembla tout le peuple, et il leur dit: Achab a honoré un peu Baal; mais moi je l’honorerai davantage.
Sa’an nan Yehu ya tattara dukan jama’a ya ce musu, “Ahab ya bauta wa Ba’al kaɗan ne kawai; amma Yehu zai bauta masa sosai.
19 Maintenant donc, appelez vers moi tous les prophètes de Baal, tous ses serviteurs et tous ses prêtres; qu’il n’y en ait aucun qui ne vienne; car c’est un grand sacrifice que je veux faire à Baal: quiconque y manquera, ne vivra plus. Or, Jéhu faisait cela insidieusement pour perdre les adorateurs de Baal;
Yanzu sai ku kira dukan annabawan Ba’al, dukan masu yin masa hidima da kuma dukan firistocinsa. Ku tabbata ba a manta da wani ba, gama zan yi wa Ba’al babbar hadaya. Duk wanda bai zo ba, a bakin ransa.” Amma Yehu yana wayo ne domin yă hallaka masu yi wa Ba’al sujada.
20 Et il dit: Sanctifiez un jour solennel en l’honneur de Baal; et il y invita;
Yehu ya ce, “Ku kira jama’a don a girmama Ba’al.” Saboda haka suka yi shela.
21 Il envoya donc dans tous les confins d’Israël, et tous les serviteurs de Baal vinrent, et il ne s’en trouva pas même un seul qui ne vint. Ainsi ils entrèrent dans le temple de Baal; et la maison de Baal fut remplie depuis une extrémité jusqu’à l’autre extrémité.
Sa’an nan ya aika saƙo ko’ina a Isra’ila, dukan masu yi wa Ba’al hidima kuwa suka tattaru, ba mutumin da bai zo ba. Suka yi cincirindo a haikalin Ba’al har sai da ya cika makil.
22 Il dit ensuite à ceux qui gardaient les vêtements: Apportez des vêtements à tous les serviteurs de Baal. Et ils leur apportèrent des vêtements.
Sai Yehu ya ce wa mai ajiyar tufafi, “Ka kawo riguna domin dukan masu yi wa Ba’al hidima.” Sai ya fito musu da riguna.
23 Et Jéhu, étant entré avec Jonadab, fils de Réchab, dans le temple de Baal, dit aux adorateurs de Baal: Cherchez, et voyez que personne parmi vous ne soit des serviteurs du Seigneur; mais qu’il n’y ait que les seuls serviteurs de Baal.
Sa’an nan Yehu da Yehonadab ɗan Rekab, suka shiga haikalin Ba’al. Yehu ya ce wa masu yi wa Ba’al sujada, “Ku dudduba ku tabbatar cewa babu wani bawan Ubangiji a nan tare da ku, sai masu hidimar Ba’al kawai.”
24 Ils entrèrent donc dans le temple pour sacrifier des victimes et des holocaustes: or Jéhu s’était préparé dehors quatre-vingts hommes, et il leur avait dit: Quiconque s’échappera d’entre les hommes que je remettrai moi-même en vos mains, l’âme de celui-ci sera pour l’âme de celui-là.
Saboda haka suka shiga don su miƙa hadayu da kuma hadaya ta ƙonawa. To, Yehu ya riga ya ba wa mutane takwas wannan kashedi a waje cewa, “In waninku ya bar ɗaya daga cikin mutanen nan da nake danƙa a hannunku ya tsere, to, a bakin ransa.”
25 Il arriva donc que, lorsque l’holocauste eut été achevé, Jéhu donna cet ordre à ses soldats et à ses officiers: Entrez, tuez, et qu’aucun n’échappe. Et les officiers et les soldats les frappèrent du tranchant du glaive, et les jetèrent dehors; ensuite ils allèrent dans la ville où était le temple de Baal,
Nan da nan sa’ad da Yehu ya gama yin hadayar, sai ya umarci masu gadin da hafsoshi, “Ku shiga ku karkashe su; kada ku bar wani yă tsere.” Saboda haka suka karkashe su da takobi. Masu gadin da hafsoshin suka wuwwurga gawawwakinsu waje, suka kuma shiga ciki cikin haikalin Ba’al ɗin,
26 Et ils enlevèrent la statue de Baal du temple, et ils la brûlèrent,
suka fitar da dutsen tsafi daga haikalin Ba’al, suka kuma ƙone shi.
27 Et la réduisirent en poudre. Ils détruisirent aussi le temple de Baal, et firent à sa place des latrines qui ont subsisté jusqu’à ce jour.
Suka farfasa dutsen tsafin Ba’al, suka kuma rushe haikalin, mutane suka mai da wurin salga har yă zuwa yau.
28 C’est ainsi que Jéhu extermina Baal du milieu d’Israël;
Ta haka Yehu ya hallaka butar Ba’al a Isra’ila.
29 Mais quant aux péchés de Jéroboam, fils de Nabath, qui fit pécher Israël, il ne s’en écarta pas, et il n’abandonna pas les veaux d’or qui étaient à Béthel et à Dan.
Duk da haka, bai rabu da zunuban Yerobowam ɗan Nebat, wanda ya sa Isra’ila ta aikata ba, wato, yin sujada ga siffofin maruƙa na zinariya a Betel da kuma Dan.
30 Le Seigneur dit donc à Jéhu: Parce que tu as fait avec zèle ce qui était droit et plaisait à mes yeux, et que tout ce qui était en mon cœur, tu l’as fait contre la maison d’Achab, tes enfants, jusqu’à la quatrième génération, seront assis sur le trône d’Israël.
Ubangiji ya ce wa Yehu, “Tun da yake ka aikata abin da yake mai kyau a idanuna, ka kuma yi wa gidan Ahab dukan abin da yake a zuciyata, ina yin maka alkawari cewa zuriyarka za su yi mulkin Isra’ila har tsara ta huɗu.”
31 Cependant Jéhu n’eut pas soin de marcher dans la loi du Seigneur Dieu d’Israël en tout son cœur, et il ne s’écarta par des péchés de Jéroboam, qui avait fait pécher Israël.
Duk da haka, Yehu bai mai da hankali ya kiyaye dokokin Ubangiji, Allah na Isra’ila da dukan zuciyarsa ba. Bai rabu da zunubin Yerobowam, wanda ya sa Isra’ila ta aikata ba.
32 En ces jours-là, le Seigneur commença à se lasser d’Israël, et Hazaël les battit sur toutes les frontières d’Israël,
A kwanakin sai Ubangiji ya fara rage girman Isra’ila, Hazayel ya yi nasara a bisa Isra’ila a ko’ina a yankinsu
33 Depuis le Jourdain, vers le côté oriental, ruinant toute la terre de Galaad, Gad, Ruben et Manassé, depuis Aroër, qui est sur le torrent d’Arnon, et Galaad, et Basan.
gabas da Urdun, cikin dukan ƙasar Gileyad (yankin Gad, da na Ruben, da na Manasse), daga Arower wajen Kwarin Arnon ya ratsa Gileyad zuwa Bashan.
34 Mais le reste des actions de Jéhu, tout ce qu’il a fait, et son courage, n’est-ce pas écrit dans le Livre des actions des jours des rois d’Israël?
Game da sauran ayyukan mulkin Yehu, da dukan abin da ya yi, a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
35 Et Jéhu dormit avec ses pères, et on l’ensevelit à Samarie, et Joachaz, son fils, régna en sa place.
Yehu ya huta tare da kakanninsa, aka binne shi a Samariya. Yehoyahaz kuma ya ci sarauta bayansa.
36 Or les jours durant lesquels Jéhu régna sur Israël, en Samarie, furent de vingt-huit ans.
Yehu ya yi sarautar Isra’ila a Samariya shekara ashirin da takwas.