< 2 Chroniques 20 >

1 Après cela les enfants de Moab et les enfants d’Ammon, et avec eux des Ammonites, s’assemblèrent contre Josaphat pour combattre contre lui.
Bayan wannan, Mowabawa da Ammonawa tare da waɗansu Meyunawa suka zo su yaƙi Yehoshafat.
2 Et des messagers vinrent et l’annoncèrent à Josaphat, disant: Une grande multitude vient contre vous des lieux qui sont au-delà de la mer et de la Syrie, et voilà qu’ils s’arrêtent à Asasonthamar, qui est Engaddi.
Sai waɗansu mutane suka zo suka faɗa wa Yehoshafat, “Ga babban runduna tana zuwa a kanka daga Edom, daga ƙetaren Teku, daga Aram. Ta ma kai Hazazon Tamar” (wato, En Gedi).
3 Or, Josaphat, saisi de crainte, s’appliqua entièrement à prier le Seigneur, et publia un jeûne dans tout Juda.
A firgice, Yehoshafat ya yanke shawara yă nemi nufin Ubangiji, ya kuma yi shelar azumi a dukan Yahuda.
4 Et Juda s’assembla pour prier le Seigneur, et même tous sortirent de leurs villes pour l’implorer,
Mutanen Yahuda suka taru gaba ɗaya don su nemi taimako daga wurin Ubangiji, tabbatacce suka fito daga kowane garin Yahuda don su neme shi.
5 Et lorsque Josaphat se fut levé au milieu de Juda et de Jérusalem dans la maison du Seigneur, devant le parvis nouveau,
Sa’an nan Yehoshafat ya miƙe tsaye a taron Yahuda da Urushalima a haikalin Ubangiji a sabon filin
6 Il dit: Seigneur Dieu de nos pères, c’est vous qui êtes Dieu dans le ciel, et qui dominez sur tous les royaumes des nations: dans votre main sont la force et la puissance, et personne ne peut vous résister.
ya ce, “Ya Ubangiji Allah na kakanninmu, ba kai ne Allah wanda yake sama ba? Kana mulki a bisa dukan mulkokin ƙasashe. Iko da girma suna a hannunka, kuma ba wanda zai iya tsayayya da kai.
7 N’est-ce pas vous, notre Dieu, qui avez tué tous les habitants de cette terre devant votre peuple Israël, et qui l’avez donnée à la postérité d’Abraham, votre ami pour toujours?
Ya Allahnmu, ba kai ba ne ka kore mazaunan wannan ƙasa a gaban mutanenka Isra’ila ka kuma ba da ita har abada ga zuriyar Ibrahim abokinka?
8 Et ils y ont habité, et ils y ont construit un sanctuaire à votre nom, disant:
Sun yi zama a cikinta suka kuma yi gina wuri mai tsarki a cikinta domin Sunanka cewa,
9 S’il fond sur nous des maux, un glaive de jugement, une peste, et une famine, nous nous tiendrons en votre présence devant cette maison, dans laquelle a été invoqué votre nom, et nous crierons vers vous dans nos tribulations, et vous nous exaucerez, et vous nous sauverez.
‘In masifa ta zo mana, ko takobin hukunci, ko annoba ko yunwa, za mu tsaya a gabanka a gaban wannan haikalin da yake ɗauke da Sunanka, mu kuma yi kuka gare ka cikin azaba, za ka kuwa ji mu, ka cece mu.’
10 Maintenant donc, voilà que les enfants d’Ammon et de Moab, et les habitants de la montagne de Séir, au milieu desquels vous ne permîtes pas à Israël de passer lorsqu’ils sortaient d’Égypte; mais ils se détournèrent d’eux, et ils ne les tuèrent pas.
“Yanzu kuma ga mutanen Ammon, da na Mowab, da na Dutsen Seyir, waɗanda ka hana Isra’ilawa su kai musu yaƙi sa’ad da suka fito daga ƙasar Masar, su ne mutanen da Isra’ila suka ƙyale, ba su hallaka su ba.
11 Voilà que ces peuples agissent tout autrement, et ils s’efforcent de nous chasser de la possession que vous nous avez donnée.
Yau ga yadda suke so su biya mu. Su suke so su kore mu daga ƙasar da ka ba mu gādo.
12 Ô notre Dieu, ne les jugerez-vous pas? Certes, nous n’avons pas une assez grande force pour que nous puissions résister à cette multitude qui vient fondre sur nous. Mais, comme nous ignorons ce que nous devons faire, il ne nous reste qu’à diriger nos yeux vers vous.
Ya Allahnmu, ba za ka hukunta su ba? Gama ba mu da ƙarfin fuskantar wannan babbar rundunar da take so ta yaƙe mu. Ba mu san abin da za mu yi ba, mu dai mun zuba maka ido.”
13 Or tout Juda était debout devant le Seigneur, avec leurs petits enfants, leurs femmes et leurs autres enfants.
Dukan mazan Yahuda, tare da matansu da yaransu da ƙananansu, suka tsaya a gaban Ubangiji.
14 Là était aussi Jahaziel, fils de Zacharie, fils de Banaïas, fils de Jéhiel, fils de Mathanias, Lévite de la famille d’Asaph; et l’Esprit de Dieu descendit sur lui au milieu de la multitude;
Sa’an nan Ruhun Ubangiji ya sauko a kan Yahaziyel ɗan Zakariya, ɗan Benahiya, ɗan Yehiyel, ɗan Mattaniya, wani Balawe kuma zuriyar Asaf, yayinda yake tsaye a cikin taron.
15 Et il dit: Ecoutez, vous tous, Juda, et vous qui habitez Jérusalem, et vous aussi, roi Josaphat: Voici ce que vous dit le Seigneur: Ne craignez point, et ne redoutez point cette multitude; car ce n’est pas votre combat, mais celui de Dieu.
Ya ce, “Saurara, Sarki Yehoshafat da dukan waɗanda suke zama a Yahuda da Urushalima! Ga abin da Ubangiji ya ce muku, ‘Kada ku ji tsoro ko ku fid da zuciya saboda wannan babbar runduna. Gama yaƙin ba naku ba ne, amma na Allah.
16 Demain vous descendrez contre eux; car ils doivent monter par le coteau du nom de Sis, et vous les trouverez à l’extrémité du torrent qui est contre le désert de Jéruel.
Gobe ku fito ku gangara ku yaƙe su. Za su yi ta haurawa ta Mashigin Ziz, ku kuwa za ku same su a ƙarshen kwari a Hamadan Yeruwel.
17 Ce ne sera pas vous qui combattrez; mais seulement soyez résolus, et vous verrez le secours du Seigneur sur vous, ô Juda et Jérusalem: ne craignez point et ne vous effrayez point; demain vous marcherez contre eux, et le Seigneur sera avec vous.
Ba lalle ba ne ku yi wannan yaƙi. Ku dai, ku ja dāgā, ku tsaya kurum ku ga nasarar da Ubangiji zai ba ku, ya Yahuda da Urushalima. Kada ku ji tsoro; kada ku karai. Ku fito don ku fuskance su gobe, Ubangiji kuwa zai kasance tare ku.’”
18 Josaphat donc, et Juda, et tous les habitants de Jérusalem, tombèrent inclinés vers la terre devant le Seigneur, et l’adorèrent.
Yehoshafat ya rusuna da fuskarsa har ƙasa, dukan mutanen Yahuda da Urushalima suka fāɗi rubda ciki suka yi sujada a gaban Ubangiji.
19 Et les Lévites d’entre les enfants de Caath et d’entre les enfants de Coré louaient le Seigneur Dieu d’Israël avec une voix forte et élevée.
Sa’an nan waɗansu Lawiyawa daga Kohatawa da Korayawa suka tashi tsaye suka yabe Ubangiji, Allah na Isra’ila, da babbar murya sosai.
20 Et lorsqu’au matin ils se furent levés, ils sortirent par le désert de Thécué; et, lorsqu’ils étaient en marche, Josaphat, debout au milieu d’eux, dit: Ecoutez-moi, hommes de Juda, et vous tous, habitants de Jérusalem: mettez votre confiance dans le Seigneur votre Dieu, et vous serez en sûreté; croyez à ses prophètes, et toutes choses seront prospères.
Da sassafe suka tashi suka nufi Hamadan Tekowa. Yayinda suka kama hanya, Yehoshafat ya tsaya ya ce, “Ku saurare ni, Yahuda da mutanen Urushalima! Ku amince da Ubangiji Allahnku za a kuwa kafa ku; ku amince da annabawansa za ku kuwa yi nasara.”
21 Et il donna ses avis au peuple, et il établit les chantres du Seigneur pour le louer dans leurs diverses bandes, marcher devant l’armée, et d’une voix unanime dire: Rendez gloire au Seigneur, parce que sa miséricorde est éternelle.
Bayan suka yi shawara tare da shugabanni, sai ya zaɓi mutanen da za su ja gaban sojoji suna waƙa ga Ubangiji suna yabonsa saboda tsarkinsa suna cewa, “Ku yi godiya ga Ubangiji, gama ƙaunarsa dawwammamiya ce har abada.”
22 Et lorsqu’ils eurent commencé à chanter ainsi des louanges, le Seigneur tourna tous les desseins des ennemis contre eux-mêmes, c’est-à-dire des enfants d’Ammon et de Moab, et des habitants de la montagne de Séir qui étaient sortis pour combattre contre Juda; et ils furent battus.
Da suka fara waƙa, suna kuma yabo, sai Ubangiji ya kai hari a kan mutanen Ammon da Mowab da Dutsen Seyir, waɗanda suka kawo hari a Yahuda, aka kuwa ci su da yaƙi.
23 Car les fils d’Ammon et de Moab se levèrent contre les habitants de la montagne de Séir, pour les massacrer et les exterminer; et lorsqu’ils eurent achevé, s’étant aussi tournés contre eux-mêmes, ils tombèrent sous leurs coups mutuels.
Mutanen Ammon da Mowab suka tasar wa mazaunan Dutsen Seyir, suka hallaka su ƙaƙaf. Sa’ad da suka karkashe mazaunan Seyir sai suka fāɗa wa juna, suka yi ta hallaka juna.
24 Or, lorsque Juda fut venu à l’échauguette qui regarde le désert, il vit de loin tout le pays dans une grande étendue plein de cadavres, et qu’il ne restait personne qui eût pu échapper à la mort.
Sa’ad da mutanen Yahuda suka zo wurin da yake fuskantar hamada, suka duba ta wajen babban rundunar, sai suka ga gawawwaki birjik a ƙasa; babu wani wanda ya kuɓuta.
25 Josaphat vint donc, et tout le peuple avec lui, pour enlever les dépouilles des morts, et ils trouvèrent, parmi les cadavres, des meubles divers, des vêtements aussi et des vases très précieux, et ils les pillèrent; en sorte qu’ils ne purent tout emporter, ni enlever durant trois jours les dépouilles, à cause de la quantité du butin.
Sa’ad da Yehoshafat da jama’arsa suka je kwasar ganima, sai suka sami shanu masu yawan gaske, da kayayyaki, da tufafi, da abubuwa masu daraja, waɗanda suka yi ta kwasa har suka gaji. Kwana uku suka yi suna kwasar ganimar saboda yawanta.
26 Or, le quatrième jour, ils s’assemblèrent dans la vallée de la Bénédiction; car, parce qu’ils y avaient béni le Seigneur, ils appelèrent ce lieu vallée de Bénédiction, jusqu’au présent jour.
A rana ta huɗu sai suka taru a Kwarin Beraka, inda suka yabi Ubangiji. Wannan ne ya sa ake kiransa Kwarin Beraka har wa yau.
27 Ensuite tout homme de Juda, et tous les habitants de Jérusalem, et Josaphat à leur tête, retournèrent à Jérusalem dans une grande allégresse, parce que le Seigneur leur avait donné de la joie au sujet de leurs ennemis.
Sa’an nan Yehoshafat ya jagoranci dukan mutanen Yahuda da Urushalima suka dawo da farin ciki zuwa Urushalima, gama Ubangiji ya ba su dalilin farin ciki a kan abokan gābansu.
28 Ils entrèrent donc à Jérusalem dans la maison du Seigneur avec des psaltérions, des harpes et des trompettes.
Suka shiga Urushalima suka shiga haikalin Ubangiji da kiɗin molaye da sarewa da kuma garayu.
29 Mais la terreur du Seigneur fondit sur tous les royaumes des pays voisins, lorsqu’ils eurent appris que le Seigneur avait combattu contre les ennemis d’Israël.
Tsoron Allah ya kama dukan mulkokin ƙasashe sa’ad da suka ji yadda Ubangiji ya yi yaƙi a kan abokan gāban Isra’ila.
30 Et le royaume de Josaphat se reposa, et Dieu lui donna la paix alentour.
Mulkin Yehoshafat kuwa ya zauna lafiya, gama Allahnsa ya ba shi hutu a kowane gefe.
31 Josaphat régna donc sur Juda; et il avait trente-cinq ans, lorsqu’il commença à régner: or il régna vingt-cinq ans à Jérusalem; et le nom de sa mère était Azuba, fille de Sélahi.
Ta haka Yehoshafat ya yi mulki a bisa Yahuda. Yana da shekara talatin da biyar sa’ad da ya zama sarkin Yahuda, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara ashirin da biyar. Sunan mahaifiyarsa Azuba ce,’yar Shilhi.
32 Et il marcha dans les voies de son père Asa, et il ne s’en détourna point, faisant ce qui était agréable devant le Seigneur.
Ya yi tafiya a hanyoyin mahaifinsa Asa bai kuwa kauce daga gare su ba; ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji.
33 Cependant il ne détruisit pas les hauts lieux, et le peuple n’avait pas encore dirigé son cœur vers le Seigneur Dieu de ses pères.
Duk da haka ba a kawar da masujadai kan tudu ba, domin har yanzu mutanen ba su tsayar da zukatansu ga Allahn kakanninsu ba.
34 Or le reste des actions de Josaphat, des premières et des dernières, est écrit dans l’histoire que Jéhu, fils d’Hanani, a insérée dans les Livres des rois d’Israël.
Sauran ayyukan mulkin Yehoshafat, daga farko zuwa ƙarshe, an rubuta su a tarihin Yehu ɗan Hanani, waɗanda aka rubuta a littafin sarakunan Isra’ila.
35 Après cela, Josaphat, roi de Juda, contracta amitié avec Ochozias, roi d’Israël, dont les œuvres furent très impies.
Daga baya, Yehoshafat sarkin Yahuda ya haɗa kai da Ahaziya sarkin Isra’ila, wanda yake da laifin mugunta.
36 Et il contribua à ce qu’ils fissent des vaisseaux, qui iraient à Tharsis; ils firent donc une flotte à Asiongaber.
Ya yarda da shi su gina jiragen ruwan kasuwanci. Bayan aka gina waɗannan a Eziyon Geber,
37 Mais Eliézer, fils de Dodaü de Marésa, prophétisa à Josaphat, disant: Parce que vous avez fait alliance avec Ochozias, le Seigneur Dieu a frappé vos œuvres, et vos vaisseaux ont été brisés, et ils n’ont pu aller à Tharsis.
Eliyezer ɗan Dodabahu na Maresha ya yi annabci a kan Yehoshafat cewa, “Domin ka haɗa kai da Ahaziya, Ubangiji zai hallaka abin da ka yi.” Jiragen ruwan kuwa suka farfashe, ba a kuwa iya sa su je kasuwanci ba.

< 2 Chroniques 20 >