< 2 Chroniques 19 >

1 Mais Josaphat, roi de Juda, retourna paisiblement en sa maison à Jérusalem.
Sa’ad da Yehoshafat sarkin Yahuda ya dawo zuwa fadansa a Urushalima lafiya,
2 Jéhu, le Voyant, fils d’Hanani, vint à sa rencontre, et lui dit: Vous donnez du secours à l’impie, et vous vous liez d’amitié avec ceux qui haïssent le Seigneur; et c’est pour cela certainement que vous méritiez la colère de Dieu.
Yehu mai duba, ɗan Hanani, ya fita don yă tarye shi, ya kuma ce wa sarki, “Ya yi kyau ke nan da ka taimaki mugu ka kuma ƙaunaci waɗanda suke ƙin Ubangiji? Da yake ka yi haka fushin Ubangiji yana a kanka
3 Mais de bonnes œuvres ont été trouvées en vous, parce que vous avez enlevé les bois sacrés de la terre de Juda, et que vous avez préparé votre cœur pour chercher le Seigneur Dieu de vos pères.
Duk da haka an sami wani abin kirki a wurinka, gama ka kawar da ginshiƙan Ashera a ƙasar, ka kuma sa zuciyarka a kan neman Allah.”
4 Josaphat habita donc à Jérusalem, et il sortit de nouveau vers le peuple, depuis Bersabée jusqu’à la montagne d’Ephraïm, et il les rappela au culte du Seigneur, le Dieu de leurs pères.
Yehoshafat ya zauna a Urushalima, ya kuma fita yana shiga cikin mutane daga Beyersheba zuwa ƙasar tudun Efraim ya kuma juyar da su ga Ubangiji Allah na kakanninsu.
5 Et il établit des juges pour le pays dans toutes les villes de Juda fortifiées, pour chaque lieu en particulier.
Ya naɗa alƙalai a kowanne daga cikin biranen katanga na Yahuda a ƙasar.
6 Et il ordonna aux juges: Prenez garde, dit-il, à tout ce que vous ferez; car ce n’est pas la justice d’un homme que vous exercez, mais celle du Seigneur, et tout ce que vous aurez jugé retombera sur vous.
Ya faɗa musu, “Ku lura da abin da kuke yi, gama shari’ar da kuke yi ba ta mutum ba ce, amma ta Ubangiji ce, yana tare da ku sa’ad da kuke yanke shari’a.
7 Que la crainte du Seigneur soit avec vous, et faites tout avec soin; car il n’y a dans le Seigneur notre Dieu, ni iniquité, ni acception de personnes, ni désir de présents.
Yanzu fa ku ji tsoron Ubangiji. Ku yi hankali a kan abin da kuke yi, gama Ubangiji Allahnmu ba ya sonkai ko nuna wariya ko cin hanci.”
8 Josaphat établit aussi dans Jérusalem des Lévites, des prêtres, et des princes des familles d’Israël, afin de juger le jugement et la cause du Seigneur pour ses habitants.
A Urushalima kuma, Yehoshafat ya naɗa waɗansu Lawiyawa, firistoci da kawunan iyalan Isra’ilawa don su tabbatar da an bi dokar Ubangiji, su kuma sasanta tsakanin mutane. A Urushalima za su zauna.
9 Et il leur ordonna, disant: C’est ainsi que vous agirez dans la crainte du Seigneur, fidèlement et avec un cœur parfait.
Ya ba su waɗannan umarnai, “Ku yi aikinku da aminci da tsoron Ubangiji da dukan zuciyarku.
10 Quant à toute cause (qui vous viendra) de vos frères qui habitent dans leurs villes, entre parenté et parenté, partout où il sera question de loi, de commandement, de cérémonies, d’ordonnances, faites-la leur connaître, afin qu’ils ne pèchent point contre le Seigneur, et que sa colère ne vienne point sur vous et sur vos frères; agissant donc ainsi, vous ne pécherez point.
Cikin kowane batun da ya zo gabanku daga’yan’uwanku waɗanda suke zama a birane, ko batun na kisa ne ko kuwa waɗansu batuttuwan da suka shafi doka, umarnai, ƙa’idodi ko farillai, dole ku ja musu kunne kada su yi wa Ubangiji zunubi; in ba haka ba fushinsa zai sauko a kanku da’yan’uwanku. Ku yi wannan, ta haka ba za ku kuwa yi zunubi ba.
11 Or Amarias, le prêtre, votre pontife, présidera dans les choses qui regardent Dieu, et Zabadias, fils d’Ismael, chef dans la maison de Juda, sera préposé sur les ouvrages qui appartiennent au service du roi. Vous avez aussi pour maîtres les Lévites devant vous; fortifiez-vous et agissez avec soin, et le Seigneur sera avec vous, vous comblant de biens.
“Amariya, babban firist, shi ne zai shugabance ku a kan dukan al’amuran da suke na wajen Ubangiji, Zebadiya ɗan Ishmayel kuwa, shugabanku a kan dukan al’amuran da suka shafi sarki, Lawiyawa kuma za su zama a matsayin manya a gabanku. Ku yi abubuwa da ƙarfin hali, bari kuma Ubangiji yă kasance tare da masu yin gaskiya.”

< 2 Chroniques 19 >