< 2 Chroniques 15 >
1 Or Azarias, fils d’Oded, l’esprit de Dieu étant venu en lui,
Sai Ruhun Allah ya sauko a kan Azariya ɗan Oded.
2 Sortit à la rencontre d’Asa, et lui dit: Ecoutez-moi, Asa, et vous, Juda et Benjamin. Le Seigneur a été avec vous, parce que vous avez été avec lui. Si vous le cherchez, vous le trouverez, mais si vous l’abandonnez, il vous abandonnera.
Ya fita ya je ya sadu da Asa ya kuma faɗa masa, “Ka saurare ni, Asa da kuma dukan Yahuda da Benyamin. Ubangiji yana tare da ku sa’ad da kuke tare da shi. In kuka neme shi, za ku same shi, amma in kuka yashe shi, zai yashe ku.
3 Il se passera un grand nombre de jours en Israël, sans vrai Dieu, sans prêtre enseignant et sans loi.
Tun da daɗewa Isra’ila ba su da Allah na gaskiya, babu firist da zai koyar, kuma babu doka.
4 Et lorsque dans leur angoisse ils reviendront au Seigneur Dieu d’Israël, et qu’ils le chercheront, ils le trouveront.
Amma cikin wahalarsu suka juya ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, suka kuma neme shi, suka kuwa same shi.
5 En ce temps-là, il n’y aura point de paix pour l’entrant et le sortant, mais des terreurs de toutes parts sur tous les habitants de la terre;
A waɗancan kwanaki akwai hatsari a yin tafiye-tafiye, gama dukan mazaunan ƙasashe suna cikin babbar damuwa.
6 Car une nation combattra contre une nation, et une ville contre une ville, parce que le Seigneur les troublera de toutes sortes d’angoisses.
Wata ƙasa takan murƙushe wata, wani birni kuma yakan murƙushe wani, domin Allah ya wahalshe su da kowace irin damuwa.
7 Vous donc, fortifiez-vous, et que vos mains ne s’affaiblissent point; car il y aura une récompense pour votre œuvre.
Amma game da ku, ku ƙarfafa kada ku fid da zuciya, gama za a ba ku ladan aikinku.”
8 Lorsqu’Asa eut entendu cela, c’est-à-dire les paroles et la prophétie d’Azarias, fils d’Oded, le prophète, il se fortifia, et enleva les idoles de toute la terre de Juda et de Benjamin, et des villes qu’il avait prises, du mont Ephraïm, et il dédia l’autel du Seigneur qui était devant le portique du Seigneur.
Sa’ad da Asa ya ji waɗannan kalmomin da annabcin Azariya ɗan Oded annabi ya faɗa, sai ya sami ƙarfi hali. Ya kawar da gumaka masu banƙyama daga dukan ƙasar Yahuda da Benyamin da kuma daga garuruwan da ya ci da yaƙi a ƙasar tudu ta Efraim. Ya gyaggyara bagaden Ubangiji da yake a gaban shirayin haikalin Ubangiji.
9 Et il assembla tout Juda et Benjamin, et avec eux les étrangers venus d’Ephraïm, de Manassé, et de Siméon; car plusieurs s’étaient réfugiés d’Israël vers lui, voyant que le Seigneur son Dieu était avec lui.
Sa’an nan ya tattara dukan Yahuda da Benyamin da kuma mutane daga Efraim, Manasse da Simeyon waɗanda suke zaune a cikinsu, gama jama’a mai girma ta zo wurinsa daga Isra’ila sa’ad da suka ga cewa Ubangiji Allahnsa yana tare da shi.
10 Et lorsqu’ils furent venus à Jérusalem le troisième mois, l’an quinzième du règne d’Asa,
Suka taru a Urushalima a wata na uku na shekara ta goma sha biyar ta mulkin Asa.
11 Ils immolèrent au Seigneur en ce jour-là, parmi les dépouilles et le butin qu’ils avaient emmené, sept cents bœufs et sept mille béliers.
A lokacin suka miƙa hadaya bijimai ɗari bakwai da tumaki da kuma awaki dubu bakwai ga Ubangiji daga ganimar da suka dawo da ita.
12 Et le roi entra selon la coutume pour confirmer l’alliance, afin qu’ils cherchassent le Seigneur Dieu de leurs pères de tout leur cœur et de toute leur âme.
Suka yi alkawari don su nemi Ubangiji Allah na kakanninsu, da dukan zuciyarsu da kuma dukan ransu.
13 Or, si quelqu’un, dit-il, ne cherche pas le Seigneur Dieu d’Israël, qu’il meure, depuis le plus petit jusqu’au plus grand, depuis l’homme jusqu’à la femme.
Aka kashe dukan waɗanda ba su nemi Ubangiji, Allah na Isra’ila ba, ko ƙarami ko babba, namiji ko ta mace.
14 Et ils le jurèrent au Seigneur avec une voix forte au milieu des cris de joie, au bruit de la trompette et au son des clairons,
Suka yi rantsuwa ga Ubangiji da babbar murya, da ihu da garayu da ƙahoni.
15 Tous ceux qui étaient dans la Judée, avec exécration; car c’est en tout leur cœur qu’ils jurèrent, et avec leur entière volonté qu’ils cherchèrent le Seigneur; et ils le trouvèrent, et le Seigneur leur donna le repos à l’entour.
Dukan Yahuda suka yi farin ciki game da rantsuwar domin sun yi rantsuwar gabagadi. Suka nemi Allah da gaske, suka kuma same shi. Saboda haka Ubangiji ya ba su hutu a kowane gefe.
16 Asa déposa Maacha, mère du roi, de l’autorité souveraine, parce qu’elle avait élevé dans un bois sacré un simulacre de Priape, qu’il brisa entièrement; et l’ayant mis en pièces, il le brûla dans le torrent de Cédron.
Sarki Asa ya tuɓe mahaifiyar mahaifiyarsa daga matsayinta na mahaifiyar sarauniya, domin ta gina ginshiƙin banƙyama na Ashera. Asa ya rurrushe shi, ya farfasa shi ya kuma ƙone shi a Kwarin Kidron.
17 Mais les hauts lieux restèrent en Israël; cependant le cœur d’Asa fut parfait durant tous ses jours.
Ko da yake bai kawar da masujadan kan tudu daga Isra’ila ba, zuciyar Asa ta cika da bin Ubangiji dukan kwanakinsa.
18 Et les choses que son père avait vouées ainsi que lui-même, il les porta dans la maison du Seigneur: de l’argent, de l’or et différentes espèces de vases.
Ya kawo azurfa da zinariya da kayayyaki a haikalin Allah waɗanda shi da mahaifinsa suka keɓe.
19 Or il n’y eut point de guerre jusqu’à la trente-cinquième année du règne d’Asa.
Ba a ƙara yin yaƙi ba sai a shekara ta talatin da biyar ta mulkin Asa.