< 1 Samuel 13 >

1 Saül avait un an, lorsqu’il commença à régner, et il régna pendant deux ans sur Israël.
Shawulu yana da shekara talatin sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi sarautar Isra’ila shekara arba’in da biyu.
2 Et il se choisit trois mille hommes d’Israël; or, il y en avait deux mille avec Saül à Machmas, et sur la montagne de Béthel, et mille avec Jonathas à Gabaa-Benjamin; pour le reste du peuple, il renvoya chacun dans son tabernacle.
Sai ya zaɓi sojoji dubu uku daga jama’ar Isra’ila. Ya keɓe dubu biyu su kasance tare da shi a Mikmash da kuma a tuddan yankin Betel. Ya kuma bar dubu ɗaya tare da ɗansa Yonatan a Gibeya a yankin zuriyar Benyamin. Sauran sojojin kuwa Shawulu ya sallame su su koma gidajensu.
3 Et Jonathas battit la garnison des Philistins, qui était à Gabaa. Lorsque les Philistins l’eurent appris, Saül sonna de la trompette dans tout le pays, disant: Que les Hébreux entendent.
Yonatan ya kai wa Filistiyawa hari a Geba, sai Filistiyawa suka sami labarin. Sai Shawulu ya sa aka busa ƙaho ko’ina a ƙasar ya ce, “Bari Ibraniyawa su ji!”
4 Or tout Israël apprit cette nouvelle: Saül a battu la garnison des Philistins; et Israël se leva contre les Philistins. Le peuple cria donc après Saul à Galgala.
Haka kuwa dukan Isra’ila suka ji labari cewa, “Shawulu ya kai hari a ƙasar Filistiyawa, yanzu Isra’ila ta zama abin ƙi ga Filistiyawa.” Aka kira mutane su haɗu da Shawulu a Gilgal.
5 Et les Philistins s’assemblèrent pour combattre contre Israël, avec trente mille chariots, six mille cavaliers et le reste de la multitude, semblable au sable nombreux qui est sur le rivage de la mer. Et, montant, ils campèrent à Machmas, vers l’orient de Béthaven.
Sai Filistiyawa suka taru don su yi yaƙi da Isra’ilawa. Suka fito da kekunan-dawakan yaƙi dubu talatin, da masu hawan dawakai dubu shida, da sojoji masu yawa kamar yashi a bakin teku. Suka tafi Mikmash a gabashin Bet-Awen, suka kafa sansani a can.
6 Lorsque les hommes d’Israël virent qu’ils étaient ainsi resserrés (car le peuple était affligé), ils se cachèrent dans les cavernes, dans les lieux retirés, dans les rochers même, dans les antres et dans les citernes.
Sa’ad da Filistiyawa suka fāɗa wa Isra’ilawa da yaƙi mai tsanani, suka sa su cikin wani hali mai wuya, sai Isra’ilawa suka ɓuya a kogwanni, da ciyayi, da duwatsu, da ramummuka, da rijiyoyi.
7 Mais les Hébreux passèrent le Jourdain et vinrent dans la terre de Gad et de Galaad. Et comme Saül était à Galgala, tout le peuple qui le suivait, était épouvanté.
Waɗansunsu ma suka haye Urdun zuwa ƙasar Gad da Gileyad. Shawulu ya zauna Gilgal, dukan ƙungiyoyi sojojin da suke tare da shi suka yi rawan jiki don tsoro.
8 Et il attendit durant sept jours, selon l’ordre de Samuel, et Samuel ne vint point à Galgala, et le peuple se détacha de Saül.
Ya jira har kwana bakwai bisa ga lokacin da Sama’ila ya bayar. Amma Sama’ila bai zo Gilgal ba, mutanen Shawulu suka fara watsewa.
9 Saul dit: Apportez-moi l’holocauste et les hosties pacifiques. Et il offrit l’holocauste.
Sai ya ce, “Ku kawo mini hadaya ta ƙonawa da hadaya ta salama.” Sai Shawulu ya miƙa hadaya ta ƙonawa.
10 Et comme il achevait d’offrir l’holocauste, voilà que Samuel arrivait; et Saul sortit au devant de lui pour le saluer.
Daidai yana gama miƙa hadaya ke nan sai Sama’ila ya iso. Shawulu kuma ya fito domin yă yi masa maraba.
11 Et Samuel lui demanda: Qu’avez-vous fait? Saül répondit: Parce que j’ai vu que le peuple se détachait de moi, et que vous n’étiez pas venu, selon les jours marqués, mais que les Philistins s’étaient assemblés à Machmas,
Sama’ila ya ce, “Me ke nan ka yi?” Shawulu ya ce, “Sa’ad da na ga mutane suna watsewa, kai kuwa ba ka zo cikin lokaci ba, ga Filistiyawa kuma suna taruwa a Mikmash,
12 J’ai dit: Maintenant les Philistins descendront vers moi à Galgala, et je n’ai point apaisé la face du Seigneur. Poussé par la nécessité, j’ai offert l’holocauste.
sai na yi tunani cewa, ‘Yanzu Filistiyawa za su gangaro su fāɗa mini a Gilgal, ga ni kuma ban riga na nemi nufin Ubangiji ba.’ Shi ya sa ya zama mini tilas in miƙa hadaya ta ƙonawa.”
13 Et Samuel dit à Saul: Vous avez agi en insensé, et vous n’avez pas gardé les commandements du Seigneur votre Dieu, qu’il vous a prescrits. Si vous n’aviez point fait cela, le Seigneur aurait déjà maintenant établi votre règne sur Israël pour toujours;
Sama’ila ya ce, “Ka yi wauta da ba ka bi umarnin da Ubangiji Allahnka ya ba ka ba. Da ka yi haka da Ubangiji ya tabbatar maka da sarautar Isra’ila har abada.
14 Mais votre règne ne subsistera plus désormais. Le Seigneur s’est cherché un homme selon son cœur; et le Seigneur lui a ordonné d’être chef sur son peuple, parce que vous n’avez pas observé ce qu’a ordonné le Seigneur.
Amma yanzu, masarautarka ba za tă dawwama ba, Ubangiji ya riga ya sami wani wanda zuciyarsa ke ƙauna, ya naɗa shi shugaban mutanensa gama ba ka bi umarnin Ubangiji ba.”
15 Or, Samuel se leva, et monta de Galgala à Gabaa-Benjamin. Et le reste du peuple, monta après Saül au-devant du peuple des Philistins qui les attaquait, tandis qu’ils venaient de Galgala à Gabaa sur la colline de Benjamin. Et Saül fit la revue du peuple, qui se trouvait avec lui au nombre d’environ six cents hommes.
Sama’ila ya tashi daga Gilgal ya tafi Gibeya a ƙasar Benyamin. Shawulu kuma ya ƙidaya mutanen da suke tare da shi, yawansu ya kai wajen mutum ɗari shida.
16 Ainsi Saül et Jonathas, son fils, et tout le peuple qui se trouvait avec eux, étaient à Gabaa-Benjamin; mais les Philistins s’étaient postés à Machmas.
Shawulu da ɗansa Yonatan da mutanen da suke tare da shi suka zauna a Geba ta Benyamin. Sa’an nan Filistiyawa suka yi sansani a Mikmash.
17 Alors sortirent pour piller trois bataillons de Philistins. Un bataillon allait en face de la voie d’Ephra, vers la terre de Sual;
Rundunar mayaƙa uku suka fito daga sansani Filistiyawa. Ɗaya ta nufi Ofra, zuwa ƙasar Shuwal.
18 Mais l’autre s’avançait par la voie de Béthoron, et le troisième avait tourné vers le chemin du territoire qui domine la vallée de Séboïm, contre le désert.
Runduna guda kuma ta nufi Bet-Horon, ɗayan kuwa ta nufi iyakar da take fuskantar Kwarin Ziboyim wajen jeji.
19 Or, il ne se trouvait point de forgeron dans toute la terre d’Israël; car les Philistins avaient pris ces mesures, de peur que les Hébreux ne fissent des glaives ou des lances.
Ba a sami maƙeri ɗaya a dukan ƙasar Isra’ila ba domin Filistiyawa sun ce, “In ba haka ba Ibraniyawa za su ƙera wa kansu takuba ko māsu.”
20 Tout Israël descendait donc chez les Philistins, pour aiguiser chacun son soc de charrue, son boyau, sa cognée et son sarcloir.
Saboda haka dukan Isra’ila sukan gangara zuwa wajen Filistiyawa domin su gyara bakin garemaninsu, da fartanansu, da gaturansu, da kuma laujunansu.
21 C’est pourquoi les tranchants des socs de charrue, des hoyaux, des fourches et des cognées étaient émoussés jusqu’à la pointe qu’il fallait redresser.
Duk lokacin da za su gyara bakin garmansu da fartanyarsu sai sun biya tsabar azurfa biyu. Haka ma idan za su gyara gatari ko bakunan abin korar shanun noma sai sun biya tsabar azurfa ɗaya.
22 Et lorsque fut venu le jour du combat, il ne se trouva ni épée, ni lance dans la main de tout le peuple qui était avec Saül et Jonathas, excepté dans celle de Saül et de Jonathas, son fils.
A ranar da yaƙi ya tashi, ba a sami wanda yake da takobi ko māshi ba a cikin mutanen da suke tare da Shawulu da Yonatan. Sai dai Shawulu da ɗansa Yonatan kaɗai.
23 Or, la garnison des Philistins sortit, pour passer vers Machmas.
Ana nan sai sojojin Filistiyawa suka fita zuwa mashigin Mikmash.

< 1 Samuel 13 >