< 1 Rois 1 >

1 Or, le roi David était devenu vieux, et il comptait un grand nombre de jours de vie; et quoiqu’il fût couvert de vêtements, il ne se réchauffait pas.
Sa’ad da Sarki Dawuda ya tsufa ya kuma ƙara shekaru, ba ya iya jin ɗumi ko an rufe shi da abin rufuwa.
2 Ses serviteurs lui dirent donc: Cherchons pour notre seigneur le roi une jeune fille vierge, afin qu’elle se tienne devant le roi, qu’elle le soigne, dorme sur son sein, et réchauffe notre seigneur le roi.
Saboda haka bayinsa suka ce masa, “Bari mu nemi wata budurwa wadda za tă yi wa ranka yă daɗe, sarki hidima, tă kuma kula da shi. Za tă dinga kwanta kusa da ranka yă daɗe, yă ji ɗumi.”
3 Ils cherchèrent donc une jeune fille, belle, dans tous les confins d’Israël; et ils trouvèrent Abisag, la Sunamite, et ils l’amenèrent au roi.
Suka nemi kyakkyawar yarinya cikin fāɗin Isra’ila, sai suka sami Abishag, mutuniyar Shunam, suka kawo ta wa sarki.
4 Or, c’était une fille très belle, et elle dormait avec le roi, et elle le servait; mais le roi ne la connut pas.
Yarinyar kuwa kyakkyawa ce ƙwarai; ta kuwa lura da sarki, ta kuma yi masa hidima, amma sarki bai yi jima’i da ita ba.
5 Cependant Adonias, fils d’Haggith, s’élevait, disant: C’est moi qui régnerai. Et il se procura des chars et des cavaliers, et cinquante hommes pour courir devant lui.
Adoniya, wanda mahaifiyarsa ce Haggit, ya fito ya ce, “Zan zama sarki.” Saboda haka ya nemi kekunan yaƙi, ya kuma shirya dawakai, tare da mutane hamsin da za su sha gabansa.
6 Jamais son père ne le reprit, disant: Pourquoi as-tu fait cela? Or, Adonias était aussi très beau, et le second après Absalom.
(A duk rayuwarsa mahaifinsa bai taɓa tsawata masa yă ce, “Me ya sa kake yin haka ba?” Shi kuwa mai kyan gani ne ƙwarai, shi ne aka haifa bayan Absalom.)
7 Et il avait des entretiens avec Joab, fils de Sarvia, et avec Abiathar, le prêtre, qui soutenaient le parti d’Adonias.
Adoniya ya haɗa baƙi da Yowab ɗan Zeruhiya da kuma Abiyatar firist, suka kuma ba shi goyon baya.
8 Mais Sadoc, le prêtre, Banaïas, fils de Joïada, Nathan, le prophète. Séméi, Réi, et la force de l’armée de David, n’étaient pas avec Adonias.
Amma Zadok firist, Benahiya ɗan Yehohiyada, annabi Natan, Shimeyi, Reyi da kuma matsara na musamman na Dawuda ba su bi Adoniya ba.
9 Adonias, ayant donc immolé des béliers, des veaux et toutes les victimes grasses, près de la pierre de Zohéleth, qui était voisine de la fontaine de Rogel, appela tous ses frères, fils du roi, et tous les hommes de Juda, serviteurs du roi.
Wata rana Adoniya ya tafi Dutsen Zohelet kusa da En Rogel, inda ya yi hadayar tumaki, da shanun noma, da shanun da ake kiwo a gida. Ya kuma gayyaci’yan’uwansa, wato, sauran’ya’yan Sarki Dawuda, tare da dukan dattawan sarki da suka fito daga Yahuda,
10 Mais Nathan, le prophète, Banaïas, tous les hommes vigoureux, et Salomon, son frère, il ne les appela point.
amma bai gayyaci annabi Natan, ko Benahiya, ko wani daga matsara na musamman, ko kuwa ɗan’uwansa Solomon ba.
11 C’est pourquoi Nathan dit à Bethsabée, mère de Salomon: Avez-vous ouï dire qu’Adonias, fils d’Haggith, a été fait roi, et notre seigneur David l’ignore?
Sai Natan ya ce wa Batsheba, mahaifiyar Solomon, “Ki san cewa Adoniya, ɗan Haggit, ya zama sarki ba tare da sanin ranka yă daɗe, sarkinmu Dawuda ba?
12 Maintenant donc venez, et recevez un conseil de moi: sauvez votre vie et celle de votre fils Salomon.
Yanzu bari in ba ki shawara yadda za ki cece ranki da kuma ran ɗanki Solomon.
13 Allez, et entrez chez le roi David, et dites-lui: N’est-ce pas vous, mon seigneur le roi, qui avez juré, à moi votre servante, disant: Salomon ton fils régnera après moi, et c’est lui qui sera assis sur mon trône? Pourquoi donc Adonias règne-t-il?
Ki shiga wurin Sarki Dawuda ki ce masa, ‘Ranka yă daɗe sarki, ba ka rantse mini ni baiwarka cewa, “Tabbatacce Solomon ɗanka ne zai zama sarki bayana, yă kuma zauna a kujerar sarautar ba”? To, me ya sa Adoniya ya zama sarki?’
14 Et tandis que vous parlerez encore au roi, moi je viendrai après vous, et je compléterai vos discours.
Yayinda kike can kina magana da sarki, zan shiga in kuma tabbatar da abin da kika faɗa.”
15 C’est pourquoi Bethsabée entra chez le roi, dans sa chambre: or, le roi était fort vieux, et Abisag, la Sunamite, le servait.
Saboda haka Batsheba ta je don tă ga sarki. A yanzu dai sarki ya tsufa, yana nan kuma a cikin ɗakinsa, inda Abishag mutuniya Shunam take masa hidima.
16 Bethsabée s’inclina et se prosterna devant le roi. Le roi lui dit: Que veux-tu?
Batsheba ta rusuna ta kuma durƙusa a gaban sarki. Sai sarki ya tambaye ta ya ce, “Me kike so?”
17 Bethsabée répondant, dit: Mon seigneur, c’est vous qui avez juré par le Seigneur votre Dieu à votre servante: Salomon ton fils régnera après moi, et c’est lui qui sera assis sur mon trône.
Ta ce masa, “Ranka yă daɗe, kai kanka ka rantse mini ni baiwarka da sunan Ubangiji Allahnka cewa, ‘Solomon ɗanka zai zama sarki bayana, zai kuma zauna a kujerar sarautata.’
18 Et voilà qu’Adonias règne, vous, mon seigneur le roi, l’ignorant.
Amma yanzu Adoniya ya zama sarki, kai kuwa ranka yă daɗe sarki, ba ka san wani abu game da shi ba.
19 Il a immolé des bœufs, toutes les victimes grasses, et un grand nombre de béliers; et il a appelé tous les enfants du roi, même Abiathar, le prêtre, et Joab, prince de la milice; mais Salomon votre serviteur, il ne l’a pas appelé.
Ya miƙa hadayun shanu, da shanun da ake kiwo a gida, da tumaki masu yawa, ya kuma gayyaci dukan’ya’yan sarki maza, da Abiyatar firist, da Yowab shugaban mayaƙa, amma bai gayyaci Solomon bawanka ba.
20 Cependant, mon seigneur le roi, c’est sur vous que sont fixés les yeux de tout Israël, afin que vous leur déclariez, mon seigneur le roi, qui doit être assis sur votre trône après vous.
Ranka yă daɗe sarki, idanun dukan Isra’ila suna a kanka, domin su san wa zai zauna a kujerar ranka yă daɗe sarkina, a bayanka.
21 Car il arrivera que, lorsque mon seigneur le roi se sera endormi avec ses pères, nous serons, moi et mon fils Salomon, des criminels.
In ba haka, bayan an binne ranka yă daɗe sarki, tare da kakanninsa, za a wulaƙance ni da Solomon ɗana, kamar masu laifi.”
22 Bethsabée parlant encore avec le roi, Nathan, le prophète vint.
Yayinda take cikin magana tare da sarki, sai annabi Natan ya iso.
23 Et on l’annonça au roi, en disant: Nathan le prophète est là. Et lorsqu’il fut entré en présence du roi, et qu’il se fut prosterné devant lui, incliné vers la terre,
Sai aka faɗa wa sarki, “Ga annabi Natan.” Da Natan ya je gaban sarki, sai ya rusuna da fuskarsa har ƙasa.
24 Nathan dit. Mon seigneur le roi, est-ce vous qui avez dit: Qu’Adonias règne après moi, et que ce soit lui qui soit assis sur mon trône?
Natan ya ce, “Ranka yă daɗe, sarki, ko ka furta cewa Adoniya ne zai zama sarki a bayanka, yă kuma zauna a kujerar sarautarka?
25 Parce qu’il est descendu aujourd’hui, il a immolé des bœufs et des victimes grasses et un grand nombre de béliers, et il a appelé tous les fils du roi, les princes de l’armée, et même Abiathar, le prêtre; et ils ont mangé et bu avec lui, disant: Vive le roi Adonias!
Yau ya gangara, ya kuma miƙa hadayun shanu, da shanun da ake kiwo a gida, da tumaki masu yawa. Ya gayyaci dukan’ya’yan sarki maza, da shugaban mayaƙa, da kuma Abiyatar firist. A yanzu haka suna ci, suna sha, tare da shi, suna cewa, ‘Ran Sarki Adoniya yă daɗe!’
26 Mais moi, votre serviteur, et Sadoc, le prêtre, et Banaïas, fils de Joïada, et Salomon, votre serviteur, il ne nous a pas appelés.
Amma bai gayyace ni bawanka, da Zadok firist, da Benahiya ɗan Yehohiyada, da kuma bawanka Solomon ba.
27 Est-ce de mon seigneur le roi que cela vient, et ne m’avez-vous point déclaré, à moi, votre serviteur, qui était celui qui devait être assis sur le trône de mon seigneur le roi, après lui?
Ranka yă daɗe, sarki, ko ka tabbatar da haka, amma ba ka ko faɗa wa fadawanka, cewa ga wanda zai gāje Ranka yă daɗe, sarki ba?”
28 Et le roi David répondit, disant: Appelez auprès de moi Bethsabée. Bethsabée étant entrée devant le roi, et se tenant devant lui,
Sai Dawuda ya ce, “Kira Batsheba tă shiga.” Sai ta zo gaban sarki ta kuma tsaya a gabansa.
29 Le roi jura, et dit: Le Seigneur vit, lui qui a délivré mon âme de toute angoisse!
Sai sarki ya yi rantsuwa, “Muddin Ubangiji yana a raye, wanda ya cece ni daga kowace damuwa,
30 Comme je l’ai juré par le Seigneur Dieu d’Israël, disant: Salomon ton fils régnera après moi, et c’est lui qui sera assis sur mon trône en ma place, ainsi ferai-je aujourd’hui.
tabbatacce a yau zan aikata abin da na yi miki rantsuwa da sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila; Solomon ɗanki zai zama sarki bayana, kuma shi zai zauna a kan kujerar sarautata a maimakona.”
31 Bethsabée, le visage baissé vers la terre, se prosterna devant le roi, disant: Que mon Seigneur David vive à jamais!
Sai Batsheba ta rusuna da fuskarta har ƙasa, ta kuma durƙusa a gaban sarki ta ce, “Bari ran Sarkina Dawuda yă daɗe, har abada!”
32 Le roi David dit encore: Appelez Sadoc le prêtre, Nathan le prophète, et Banaïas, fils de Joïada. Lorsqu’ils furent entrés devant le roi,
Sarki Dawuda ya ce, “Ku kira mini Zadok firist, annabi Natan, da Benahiya ɗan Yehohiyada.” Da suka zo gaban sarki,
33 Il leur dit: Prenez avez vous les serviteurs de votre maître; faites monter Salomon mon fils sur ma mule, et conduisez-le à Gihon;
sai ya ce musu, “Ku ɗauki bayin sarki tare da ku, ku kuma sa ɗana Solomon a kan dokina, ku gangara da shi zuwa Gihon.
34 Et que Sadoc le prêtre, et Nathan le prophète, l’oignent, en ce lieu, roi d’Israël; et vous sonnerez de la trompette, et vous direz: Vive le roi Salomon!
A can ku sa Zadok firist, da annabi Natan su shafe shi sarki a bisa Isra’ila. Ku busa ƙaho, ku kuma yi ihu, kuna cewa, ‘Ran Sarki Solomon yă daɗe!’
35 Et vous monterez après lui; et il viendra, et il s’assiéra sur mon trône, et c’est lui qui régnera en ma place, et je lui ordonnerai d’être chef sur Israël et sur Juda.
Sa’an nan ku haura tare da shi, zai kuwa zo yă zauna a kujera sarautata, yă yi mulki a maimakona. Na naɗa shi mai mulki a bisa Isra’ila da Yahuda.”
36 Et Banaïas, fils de Joïada, répondit au roi, disant: Amen; que le Seigneur Dieu de mon seigneur le roi parle ainsi.
Benahiya ɗan Yehohiyada ya amsa wa sarki, ya ce, “Amin! Bari Ubangiji Allah na ranka yă daɗe sarkina, yă tabbatar da haka.
37 Comme le Seigneur a été avec mon seigneur le roi, ainsi soit-il avec Salomon, et qu’il élève son trône encore plus haut que le trône de mon seigneur, le roi David.
Kamar yadda Ubangiji ya kasance da ranka yă daɗe, sarki, haka ma bari yă kasance da Solomon, yă kuma mai da kujerar sarautarsa tă fi kujerar sarautar ranka yă daɗe, Sarki Dawuda, girma!”
38 Sadoc, le prêtre, descendit donc, ainsi que Nathan le prophète, Banaïas, fils de Joïada, les Céréthiens et les Phéléthiens; et ils firent monter Salomon sur la mule du roi David, et ils le conduisirent à Gihon.
Sai Zadok firist, annabi Natan, Benahiya ɗan Yehohiyada, Keretawa, da Feletiyawa suka gangara, suka sa Solomon a kan dokin Sarki Dawuda, suka raka shi zuwa Gihon.
39 Et Sadoc, le prêtre, prit la corne d’huile du tabernacle, et oignit Salomon; et ils sonnèrent de la trompette, et tout le peuple dit: Vive le roi Salomon!
Zadok firist ya ɗauki ƙahon mai daga tenti mai tsarki, ya shafe Solomon. Sa’an nan suka busa ƙaho, sai dukan mutane suka yi ihu, suna cewa “Ran Sarki Solomon yă daɗe!”
40 Et toute la multitude monta après lui, et une troupe de joueurs de flûte et de gens qui se réjouissaient d’une grande joie, et la terre retentit de leur clameur.
Dukan mutane kuwa suka haura suka bi shi, suna busan sarewa, suna farin ciki sosai, har ƙasa ta girgiza saboda sowa.
41 Or, Adonias entendit, et tous ceux qui avaient été invités par lui; mais le festin était déjà achevé; et Joab aussi, ayant ouï le son de la trompette, dit: Que veut dire cette clameur de la ville en tumulte?
Adoniya tare da dukan baƙin da suke tare da shi kuwa suka ji wannan sa’ad da suke gama bikinsu. Da jin busan ƙaho, sai Yowab ya yi tambaya, ya ce, “Me ya jawo surutu haka a birni?”
42 Joab parlant encore, Jonathas, fils d’Abiathar le prêtre, vint. Adonias lui dit: Entre, parce que tu es un homme vaillant, et nous annonçant de bonnes choses.
Tun yana cikin magana, sai Yonatan ɗan Abiyatar ya iso. Adoniya ya ce, “Shigo! Ai, mutumin kirki irinka, lalle ka kawo labari mai daɗi ne.”
43 Et Jonathas répondit à Adonias: Nullement, car notre seigneur, le roi David, a établi roi Salomon;
Yonatan ya ce wa Adoniya, “A ina! Ranka yă daɗe, Sarkinmu Dawuda ya naɗa Solomon sarki.
44 Et il a envoyé avec lui Sadoc le prêtre, Nathan le prophète, Banaïas, fils de Joïada, les Céréthiens et les Phéléthiens, et ils l’ont fait monter sur la mule du roi.
Sarki ya aika shi tare da Zadok firist, annabi Natan, Benahiya ɗan Yehohiyada, Keretawa, da Feletiyawa, suka sa shi a kan dokin sarki,
45 Et Sadoc le prêtre, et Nathan le prophète, l’ont oint roi à Gihon; et ils sont montés de là en se réjouissant; et la ville a retenti. C’est là le bruit que vous avez entendu.
Zadok firist kuwa da annabi Natan sun shafe shi sarki a Gihon. Daga can suka haura suna kirari, birni kuwa ta ɓarke da sowa. Surutun da kake ji ke nan.
46 Et Salomon même est déjà assis sur le trône du royaume.
Ban da haka ma, Solomon ne sarki yanzu.
47 Et les serviteurs du roi, étant entrés, ont félicité notre seigneur, le roi David, disant: Que Dieu étende le nom de Salomon plus que votre nom, et qu’il élève son trône au-dessus de votre trône. Et le roi a adoré le Seigneur dans son lit,
Yanzu haka, fadawa sun zo suna wa ranka yă daɗe, Sarki Dawuda, sam barka, suna cewa, ‘Bari Allahnka yă sa sunan Solomon yă zama sananne fiye da naka, bari kuma sarautarsa tă fi taka girma!’ Sarki kuwa ya rusuna, ya yi sujada a kan gadonsa
48 Et a dit: Béni le Seigneur Dieu d’Israël, qui a fait asseoir aujourd’hui mon fils sur mon trône, mes yeux le voyant!
ya ce, ‘Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda ya bar idanuna suka ga magāji a kan kujerar sarautata a yau.’”
49 Ils furent donc effrayés, et ils se levèrent, tous ceux qui avaient été invités par Adonias et chacun s’en alla en sa voie.
A nan fa, dukan baƙin Adoniya suka taso da rawar jiki suka watse.
50 Mais Adonias, craignant Salomon, se leva et s’en alla, et saisit la corne de l’autel.
Amma Adoniya, don tsoron Solomon, ya je ya kama ƙahon bagade ya riƙe.
51 Et on l’annonça à Salomon, en disant: Voilà Adonias, qui, craignant le roi Salomon, s’est attaché à la corne de l’autel, disant: Que le roi Salomon me jure aujourd’hui qu’il ne frappera point son serviteur du glaive.
Sa’ad da aka faɗa wa Solomon cewa, “Adoniya yana tsoron Sarki Solomon, kuma ya manne wa ƙahonin bagade. Yana cewa, ‘Bari Sarki Solomon yă rantse mini a yau cewa ba zai kashe bawansa da takobi ba.’”
52 Et Salomon dit: S’il est un homme de bien, il ne tombera pas même un seul de ses cheveux sur la terre; mais s’il se trouve du mal en lui, il mourra.
Solomon ya amsa ya ce, “In ya nuna kansa mai biyayya, ba gashin kansa da zai fāɗi ƙasa; amma in aka same mugunta a cikinsa, zai mutu.”
53 Le roi Salomon envoya donc, et le fit retirer de l’autel. Et, étant entré, il se prosterna devant le roi Salomon; et Salomon lui dit: Va en ta maison.
Sai Sarki Solomon ya aiki mutane, suka kuma sauko da shi daga bagade. Adoniya kuwa ya zo, ya rusuna wa Sarki Solomon, sai Solomon ya ce, “Tafi gidanka.”

< 1 Rois 1 >