< 1 Rois 8 >
1 Alors s’assemblèrent tous les anciens d’Israël avec les princes des tribus, et les chefs des familles des enfants d’Israël, auprès du roi Salomon dans Jérusalem, pour transporter l’arche de l’alliance du Seigneur de la cité de David, c’est-à-dire, de Sion.
Sai Sarki Solomon ya tattara dattawan Urushalima a gabansa, da dukan shugabannin kabilu, da shugabannin iyalan Isra’ilawa, domin su kawo akwatin alkawarin Ubangiji daga Sihiyona, Birnin Dawuda.
2 Et tout Israël vint ensemble auprès du roi Salomon, dans le mois d’Ethanim, au jour solennel: c’est le septième mois.
Dukan mutanen Isra’ila suka tattaru a gaban Sarki Solomon a lokacin biki, a watan Etanim, wato, wata na bakwai.
3 Tous les anciens d’Israël vinrent donc, et les prêtres emportèrent l’arche,
Sa’ad da dukan dattawan Isra’ila suka iso, sai firistoci suka ɗauki akwatin alkawarin,
4 Et ils emportèrent l’arche du Seigneur, et le tabernacle d’alliance, et tous les vases du sanctuaire qui étaient dans le tabernacle; et les prêtres et les lévites les portaient.
suka haura da akwatin alkawarin Ubangiji da kuma Tentin Sujada, da dukan kayayyaki masu tsarkin da suke cikinsa. Firistoci da Lawiyawa suka ɗauko su,
5 Or le roi Salomon, et toute la multitude d’Israël, qui était venue auprès de lui, marchait avec lui devant l’arche, et ils immolaient des brebis et des bœufs, sans prix et sans nombre.
sai Sarki Solomon da dukan taron Isra’ila da suka tattaru kewaye da shi a gaban akwatin alkawari, suka yi ta miƙa hadayar tumaki da bijimai masu yawa da ba a iya lissaftawa, ko ƙirgawa.
6 Et les prêtres portèrent l’arche de l’alliance du Seigneur en son lieu, dans l’oracle du temple, dans le Saint des saints, sous les ailes des chérubins.
Sa’an nan firistoci suka kawo akwatin alkawarin Ubangiji inda aka shirya masa, can ciki cikin haikali, a Wuri Mafi Tsarki, aka kuma sa shi a ƙarƙashin fikafikan kerubobin.
7 Car les chérubins étendaient leurs ailes au-dessus du lieu de l’arche, et ils couvraient l’arche, et les leviers par en haut.
Kerubobin sun buɗe fikafikansu a bisa wurin da akwatin alkawarin yake, suka inuwartar da akwatin alkawarin da sandunan ɗaukansa.
8 Et comme les leviers passaient en dehors, et que leurs extrémités paraissaient hors du sanctuaire devant l’oracle, ils ne paraissaient plus extérieurement, et ils sont demeurés là jusqu’au présent jour.
Waɗannan sandunan sun yi tsawo har ana iya ganin bakinsu daga Wuri Mai Tsarki a gaban wuri mai tsarki na can ciki, amma ba a iya ganinsu daga waje na Wuri Mai Tsarki ba. Suna nan kuwa a can har wa yau.
9 Or, il n’y avait rien autre chose dans l’arche que les deux tables de pierre que Moïse y avait mises à Horeb, quand le Seigneur fit alliance avec les enfants d’Israël, lorsqu’ils sortirent de la terre d’Egypte.
Ba kome a cikin akwatin alkawarin, sai dai alluna na dutse guda biyu waɗanda Musa ya ajiye a ciki tun a Horeb, inda Ubangiji ya yi alkawari da Isra’ilawa bayan sun fito Masar.
10 Mais il arriva que, quand les prêtres furent sortis du sanctuaire, la nuée remplit la maison du Seigneur;
Sa’ad da firistoci suka janye daga Wuri Mai Tsarki, sai girgije ya cika haikalin Ubangiji.
11 Et les prêtres ne pouvaient pas s’y tenir, ni remplir leur ministère à cause de la nuée; car la gloire du Seigneur avait rempli la maison du Seigneur.
Firistocin kuwa ba su iya yin hidimarsu ba saboda girgijen, gama ɗaukakar Ubangiji ta cika haikalinsa.
12 Alors Salomon dit: Le Seigneur a dit qu’il habiterait dans la nuée.
Sai Solomon ya ce, “Ubangiji ya ce zai zauna a gizagizai masu duhu;
13 Ô Dieu, j’ai bâti cette maison pour votre demeure, et pour votre trône très affermi à jamais.
ga shi na gina haikali mai daraja dominka, inda za ka zauna har abada.”
14 Et le roi tourna sa face, et bénit toute l’assemblée d’Israël: car toute l’assemblée d’Israël était présente.
Yayinda dukan taron Isra’ila suke tsattsaye a can, sai sarki ya juya ya albarkace su.
15 Et Salomon dit: Béni le Seigneur Dieu d’Israël! lui qui a parlé de sa bouche à David mon père, et par ses mains a accompli sa parole, disant:
Sa’an nan ya ce, “Ku yabi Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda da hannunsa ya cika abin da ya yi alkawari da bakinsa ga mahaifina Dawuda. Gama ya ce,
16 Depuis le jour que j’ai retiré de l’Egypte mon peuple Israël, je n’ai point choisi de ville d’entre toutes les tribus d’Israël, afin qu’on me bâtît une maison et que mon nom y fût; mais j’ai choisi David, afin qu’il fût chef de mon peuple Israël.
‘Tun ran da na fitar da mutanena Isra’ila daga Masar, ban zaɓi wani birni a cikin wata kabilar Isra’ila a gina haikali domin Sunana yă kasance a can ba, amma na zaɓi Dawuda yă yi mulkin mutanena Isra’ila.’
17 Et David mon père voulut bâtir une maison au nom du Seigneur Dieu d’Israël;
“Mahaifina Dawuda ya yi niyya a cikin zuciyarsa yă gina haikali saboda Sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila.
18 Mais le Seigneur dit à David mon père: Quand tu as pensé en ton cœur à bâtir une maison à mon nom, tu as bien fait, en t’occupant de cela en ton esprit.
Amma Ubangiji ya ce wa mahaifina Dawuda, ‘Saboda yana a zuciyarka ka gina haikali domin Sunana, ka yi daidai da ka yi niyyar wannan a zuciyarka.
19 Cependant ce ne sera pas toi qui me bâtiras une maison; mais ton fils, qui sortira de tes flancs, sera celui qui bâtira une maison à mon nom.
Duk da haka, ba kai ba ne za ka gina haikali, amma ɗanka, wanda yake namanka da jininka, shi ne wanda zai gina haikali domin Sunana.’
20 Le Seigneur a continué la parole qu’il a dite: j’ai succédé à David mon père, je me suis assis sur le trône d’Israël, comme l’a dit le Seigneur, et j’ai bâti une maison au nom du Seigneur Dieu d’Israël.
“Ubangiji ya kiyaye alkawarin da ya yi. Na gāje Dawuda mahaifina, yanzu kuma ga shi na zauna a kujerar sarautar Isra’ila, kamar dai yadda Ubangiji ya yi alkawari, na kuma gina haikali domin Sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila.
21 Et j’ai établi là le lieu de l’arche, dans laquelle est l’alliance du Seigneur, qu’il fit avec nos pères, quand ils sortirent de la terre d’Egypte.
Na tanada wuri saboda akwatin alkawari, akwatin da ya ƙunshi alkawarin da Ubangiji ya yi da kakanninmu sa’ad da ya fitar da su daga Masar.”
22 Or Salomon se tint debout devant l’autel du Seigneur, en présence de toute l’assemblée d’Israël, et il étendit ses mains vers le ciel,
Sai Solomon ya tsaya a gaban bagaden Ubangiji, a gaban dukan taron Isra’ila, ya ɗaga hannuwansa sama,
23 Et il dit: Seigneur Dieu d’Israël, il n’y a point de Dieu semblable à vous en haut, dans le ciel, et en bas, sur la terre: c’est vous qui conservez l’alliance et la miséricorde à vos serviteurs, qui marchaient devant vous en tout leur cœur;
ya ce, “Ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, babu Allah kamar ka a sama can bisa, ko a ƙasa can ƙarƙashi, kai da kake kiyaye alkawarinka na ƙauna ga bayinka waɗanda suke cin gaba a hanyarka da dukan zuciyarsu.
24 Qui avez gardé à votre serviteur, David mon père, ce que vous lui avez promis: vous l’avez dit de votre bouche et accompli par vos mains, comme ce jour le prouve.
Ka kiyaye alkawarinka da ka yi wa bawanka Dawuda mahaifina. Da bakinka ka yi alkawari, da hannunka kuma ka cika shi, yadda yake a yau.
25 Maintenant donc, Seigneur Dieu d’Israël, conservez à votre serviteur David, mon père, ce que vous lui avez promis, disant: On ne t’enlèvera pas devant moi un homme qui doit s’asseoir sur le trône d’Israël, pourvu néanmoins que tes fils gardent leur voie, afin qu’ils marchent devant moi, comme toi tu as marché en ma présence.
“Yanzu, ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, bari ka cika wa bawanka Dawuda mahaifina alkawaran da ka yi masa sa’ad da ka ce, ‘Ba za ka taɓa rasa wani da zai zauna a gabana a kan kujerar sarautar Isra’ila ba, in kawai’ya’yanka maza sun yi hankali cikin dukan abubuwan da suke yi, don su yi tafiya a gabana kamar yadda ka yi.’
26 Et maintenant, Seigneur Dieu d’Israël, qu’elles soient accomplies, les paroles que vous avez dites à votre serviteur, David mon père.
Yanzu fa, ya Allah na Isra’ila, bari maganarka da ka yi wa bawanka Dawuda mahaifina tă cika.
27 Est-il donc croyable que Dieu habite véritablement sur la terre? Car, si le ciel et les cieux des cieux ne vous peuvent contenir, combien moins cette maison que j’ai bâtie?
“Amma anya, Allah, za ka zauna a duniya? Sammai, har ma da saman sammai ba za tă iya riƙe ka ba, balle wannan haikalin da na gina!
28 Mais portez vos regards sur la prière de votre serviteur, et sur ses supplications. Seigneur mon Dieu: écoutez l’hymne et la prière que votre serviteur fait devant vous aujourd’hui,
Duk da haka ka ji addu’ar bawanka da kuma roƙonsa don jinƙai, ya Ubangiji Allahna. Ka ji kuka da addu’ar da bawanka yake yi a gabanka a wannan rana.
29 Afin que vos yeux soient ouverts sur cette maison nuit et jour; sur la maison de laquelle vous avez dit: Mon nom sera là; afin que vous exauciez la prière que vous fait en ce lieu votre serviteur;
Bari idanunka su buɗe, su fuskanci wannan haikali dare da rana, wannan wurin da ka ce, ‘Sunana zai kasance a can,’ saboda ka ji addu’ar bawanka in yana fuskantar wannan wuri.
30 Afin que vous exauciez la prière de votre serviteur, et de votre peuple Israël, quelque chose qu’ils demandent en ce lieu: et vous exaucerez dans le lieu de votre habitation, dans le ciel, et lorsque vous aurez exaucé vous serez propice.
Ka ji roƙon bawanka da kuma na mutanenka Isra’ila sa’ad da suka yi addu’a, suka fuskanci wannan wuri. Ka ji daga sama, mazauninka, kuma sa’ad da ka ji, ka gafarta.
31 Si un homme pèche contre son prochain, s’il a quelque serment par lequel il s’est lié, et qu’il vienne à cause de ce serment devant votre autel, dans votre maison,
“Sa’ad da mutum ya yi abin da ba daidai ba ga maƙwabcinsa, an kuma bukace shi yă yi rantsuwa, sai ya zo ya rantse a gaban bagade a cikin haikalin nan,
32 Vous écouterez dans le ciel, et vous agirez et vous jugerez vos serviteurs, condamnant l’impie, ramenant sa voie sur sa tête, justifiant le juste, et lui rendant selon sa justice.
sai ka ji daga sama, ka kuma yi wani abu. Ka shari’anta tsakanin bayinka, ka hukunta mai laifi, ka mai da laifinsa a kansa, mai gaskiya kuma ka nuna shi marar laifi ne bisa ga gaskiyarsa.
33 Si votre peuple Israël fuit devant ses ennemis (parce qu’il lui arrivera de pécher contre vous), et que, faisant pénitence et rendant gloire à votre nom, ils viennent, et vous prient et vous implorent dans cette maison,
“Sa’ad da abokan gāba suka ci mutanenka Isra’ila a yaƙi saboda sun yi maka zunubi, sa’ad da kuma suka dawo gare ka don su furta sunanka, suna addu’a suna roƙo gare ka a wannan haikali,
34 Exaucez-les dans le ciel, et remettez le péché de votre peuple Israël, et ramenez-les dans la terre que vous avez donnée à leurs pères.
ka ji daga sama, ka gafarta zunubin mutanenka, ka kuma dawo da su ƙasar da ka ba wa kakanninsu.
35 Si le ciel est fermé, s’il ne pleut point à cause de leurs péchés, et que, priant en ce lieu, ils fassent pénitence pour honorer votre nom, et qu’ils se convertissent, et quittent leurs péchés à cause de leur affliction,
“Sa’ad da sammai sun kulle, babu kuma ruwan sama domin mutane sun yi maka zunubi, sa’ad da suka yi addu’a suna fuskantar wannan wuri, suka kuma furta sunanka, suka juye daga zunubinsu domin ka hore su,
36 Exaucez-les dans le ciel, et remettez les péchés de vos serviteurs et de votre peuple Israël: montrez-leur la voie droite par laquelle ils doivent marcher; et répandez de la pluie sur votre terre que vous avez donnée à votre peuple en possession.
ka ji daga sama, ka kuma gafarta zunubin bayinka, mutanenka Isra’ila. Ka koya musu hanyar da ta dace ta rayuwa, ka kuma aika da ruwan sama a ƙasar da ka ba wa mutanenka gādo.
37 Si une famine se lève sur la terre, ou une peste, ou un air corrompu, ou la rouille, ou la sauterelle ou la nielle, et que votre peuple soit affligé par son ennemi, assiégeant ses portes, par toute sorte de plaies et toute sorte d’infirmités;
“Sa’ad da yunwa ko annoba ta fāɗo a ƙasar, ko burtuntuna, ko fumfuna, ko fāri, ko tsutsa, ko kuwa abokan gāba sun yi musu kwanto, a wani daga cikin biranensu, duk wata cuta, ko ciwon da ya zo,
38 Dans tout anathème et toute imprécation qui arrivera à un homme, quel qu’il soit, de votre peuple Israël: si quelqu’un reconnaît la plaie de son cœur, et qu’il étende ses mains dans cette maison,
in suka yi addu’a ko roƙo ta wurin wani daga cikin mutanenka Isra’ila, kowa ya san wahalar zuciyarsa, ya kuma buɗe hannuwansa yana fuskantar wannan haikali,
39 Vous l’exaucerez dans le ciel, dans le lieu de votre habitation; vous lui redeviendrez propice, et vous ferez en sorte d’accorder à chacun selon toutes ses voies, comme vous verrez son cœur (parce que vous seul, vous connaissez le cœur de tous les enfants des hommes),
sai ka ji daga sama, mazauninka. Ka gafarta, ka kuma yi wani abu. Ka yi da kowane mutum bisa ga dukan abin da ya yi, tun da yake ka san zuciyarsa (gama kai kaɗai ka san zukatan dukan mutane),
40 Afin qu’ils vous craignent durant tous les jours qu’ils vivront sur la face de la terre que vous avez donnée à nos pères.
saboda su ji tsoronka a kowane lokacin da suke zaune a ƙasar da ka ba wa kakanninmu.
41 De plus, lorsque l’étranger lui-même, qui n’est point de votre peuple Israël, viendra d’une terre lointaine, à cause de votre nom (car on entendra parler de votre grand nom, de votre main puissante, et de votre bras
“Game da baƙo kuwa wanda shi ba na mutanenka Isra’ila ba, amma ya zo daga ƙasa mai nisa saboda sunanka,
42 Etendu en tous lieux): lors donc qu’il viendra, et qu’il priera en ce lieu,
gama mutane za su ji game da girman sunanka, da ƙarfin hannunka, da kuma hannunka mai iko, sa’ad da ya zo, ya yi addu’a yana fuskantar wannan haikali,
43 Vous l’exaucerez dans le ciel, dans votre demeure stable, et vous ferez toutes les choses pour lesquelles l’étranger vous invoquera, afin que tous les peuples de la terre apprennent à craindre votre nom, comme le fait votre peuple Israël, et qu’ils éprouvent que votre nom a été invoqué sur cette maison que j’ai bâtie.
ka ji daga sama, mazauninka, ka kuma yi dukan abin da baƙon ya tambaye ka, saboda dukan mutanen duniya su san sunanka, su kuma ji tsoronka, kamar yadda mutanenka Isra’ila suke yi, bari kuma su san cewa wannan gidan da na gina, ya amsa Sunanka.
44 Si votre peuple sort pour la guerre contre ses ennemis, et que, dans la voie, partout où vous les aurez envoyés, ils vous prient, tournés vers la cité que vous avez choisie, et vers la maison que j’ai bâtie à votre nom,
“Sa’ad da mutanenka suka tafi yaƙi da abokan gābansu, a duk inda ka aike su, sa’ad da kuma suka yi addu’a ga Ubangiji suna fuskantar birnin da ka zaɓa, da kuma haikalin da na gina domin Sunanka,
45 Vous exaucerez aussi dans le ciel leurs prières et leurs supplications, et vous leur ferez justice.
ka ji addu’arsu da roƙonsu daga sama, ka kuma biya musu bukatansu.
46 Que s’ils pèchent contre vous (car il n’y a point d’homme qui ne pèche), et qu’irrité, vous les livriez aux mains de leurs ennemis, qu’ils soient emmenés captifs dans la terre des ennemis, ou près ou loin;
“Sa’ad da suka yi maka zunubi, gama babu wanda ba ya zunubi, ka kuwa yi fushi da su, ka kuma ba da su ga abokin gāba, wanda ya kwashe su kamammu zuwa ƙasarsa, nesa ko kusa;
47 Qu’ils fassent pénitence en leur cœur dans le lieu de la captivité, et que, convertis, ils vous prient dans leur captivité, disant: Nous avons péché, nous avons agi iniquement, nous nous sommes conduits en impies;
in suka canja zuciyarsu a ƙasar da aka riƙe su kamammu, suka tuba, suka kuma roƙe ka a ƙasar waɗanda suka ci su da yaƙi, suka ce, ‘Mun yi zunubi, mun yi abin da ba daidai ba, mun yi mugunta’;
48 Qu’ils reviennent à vous en tout leur cœur et en toute leur âme dans la terre de leurs ennemis, dans laquelle ils ont été emmenés captifs, et qu’ils vous prient, tournés du côté de leur terre que vous avez donnée à leurs pères, de la ville que vous avez choisie, et du temple que j’ai bâti à votre nom,
in sun juye gare ka da dukan zuciyarsu, da dukan ransu a ƙasar abokan gābansu waɗanda suka kwashe kamammu, suka yi addu’a gare ka, suka fuskanci wajen ƙasar da ka ba wa kakanninsu, waje birnin da ka zaɓa, da kuma haikalin da na gina domin Sunanka;
49 Vous exaucerez dans le ciel, dans le lieu stable de votre trône, leurs prières et leurs supplications; vous leur ferez justice;
sai ka ji daga sama, mazauninka, ka ji addu’a da roƙonsu, ka kuma biya musu bukatansu.
50 Vous deviendrez propice à votre peuple qui a péché contre vous, en pardonnant toutes leurs iniquités par lesquelles ils ont prévariqué contre vous, et vous leur ferez miséricorde devant ceux qui les auront emmenés captifs, afin qu’ils aient pitié d’eux.
Ka gafarta wa mutanenka, waɗanda suka yi maka zunubi; ka gafarta dukan laifofin da suka yi maka, ka kuma sa waɗanda suka ci su a yaƙi su ji tausayinsu.
51 Car c’est votre peuple et votre héritage, que vous avez retirés de l’Egypte, du milieu de la fournaise de fer.
Gama su mutanenka ne, abin gādonka, waɗanda ka fitar daga Masar, daga tanderu mai narken ƙarfe.
52 Que vos yeux soient ouverts aux supplications de votre serviteur et de votre peuple Israël, afin que vous les exauciez dans toutes les choses pour lesquelles ils vous invoqueront.
“Bari idanunka su buɗe ga roƙon bawanka, ga roƙon mutanenka Isra’ila, bari kuma ka saurare su sa’ad da suka yi kuka gare ka.
53 Car c’est vous qui les avez séparés de tous les peuples de la terre pour votre héritage, comme vous l’avez dit par Moïse, votre serviteur, lorsque vous avez retiré nos pères de l’Egypte, ô Seigneur Dieu.
Gama ka ware su daga dukan al’umman duniya su zama abin gādonka, kamar yadda aka furta ta wurin bawanka Musa sa’ad da kai, ya Ubangiji Mai Iko Duka ka fitar da kakanninmu daga Masar.”
54 Or, il arriva que, lorsque Salomon, priant le Seigneur, eut achevé toutes ces prières et ces supplications, il se leva de devant l’autel du Seigneur; car il avait mis les deux genoux en terre, et il avait étendu les mains vers le ciel.
Da Solomon ya gama dukan waɗannan addu’o’i da roƙe-roƙe ga Ubangiji, sai ya tashi daga gaban bagaden Ubangiji, inda ya durƙusa da hannuwansa a buɗe waje sama.
55 Il se tint donc debout, et il bénit toute l’assemblée d’Israël, à haute voix, disant:
Ya tashi ya kuma albarkaci dukan taron Isra’ila da babbar murya, yana cewa,
56 Béni le Seigneur, qui a donné du repos à son peuple Israël, selon tout ce qu’il a dit! Il n’est pas même tombé une seule parole touchant tous les biens qu’il nous a promis par Moïse son serviteur.
“Yabo ya tabbata ga Ubangiji, wanda ya ba wa mutanensa hutu kamar dai yadda ya yi alkawari. Babu magana guda da ta kāsa cika cikin dukan alkawaransa masu kyau da ya yi ta wurin bawansa Musa.
57 Que le Seigneur notre Dieu soit avec nous, comme il a été avec nos pères, ne nous abandonnant point, et ne nous rejetant point;
Bari Ubangiji Allah yă kasance tare da mu kamar yadda ya kasance da kakanninmu; kada yă taɓa rabu da mu, ko yă yashe mu.
58 Mais qu’il incline nos cœurs vers lui, afin que nous marchions dans toutes ses voies, et que nous gardions ses commandements, ses cérémonies, et toutes les ordonnances qu’il a prescrites à nos pères;
Bari yă juye zukatanmu gare shi, don mu yi tafiya a cikin dukan hanyoyinsa, mu kuma kiyaye umarnansa, ƙa’idodinsa, da kuma farillan da ya ba wa kakanninmu.
59 Et que ces mêmes paroles, par lesquelles j’ai prié devant le Seigneur, approchent du Seigneur notre Dieu, jour et nuit, afin qu’il fasse justice à son serviteur et à son peuple Israël chaque jour;
Bari kuma waɗannan kalmomina, waɗanda na yi addu’a a gaban Ubangiji, su yi kusa da Ubangiji Allahnmu, dare da rana, don yă biya bukatan bawansa da na mutanensa Isra’ila, bisa ga bukatan kowa,
60 Afin que tous les peuples de la terre sachent que c’est le Seigneur qui est Dieu, et qu’il n’y en a point d’autre, excepté lui.
saboda dukan mutanen duniya su san cewa Ubangiji, shi ne Allah, babu kuma wani.
61 Que notre cœur aussi soit parfait avec le Seigneur notre Dieu, afin que nous marchions dans ses décrets, et que nous gardions toujours ses commandements, comme nous faisons encore aujourd’hui.
Amma dole ku miƙa zukatanku ga Ubangiji Allahnmu, don ku rayu, ta wurin bin ƙa’idodinsa, ku kuma yi biyayya da umarnansa, kamar yadda kuke yi a wannan lokaci.”
62 Ainsi le roi et tout Israël avec lui immolaient des victimes devant le Seigneur.
Sai sarki da dukan Isra’ila, suka miƙa hadayu a gaban Ubangiji.
63 Et Salomon tua les hosties pacifiques qu’il immola au Seigneur, vingt-deux mille bœufs et cent vingt mille brebis; et le roi et les enfants d’Israël dédièrent le temple du Seigneur.
Solomon ya miƙa hadaya ta salama ga Ubangiji, shanu dubu ashirin da biyu, tumaki da awaki dubu ɗari da dubu ashirin. Ta haka sarki da dukan Isra’ilawa suka keɓe haikalin Ubangiji.
64 En ce jour-là, le roi consacra le milieu du parvis qui était devant la maison du Seigneur; car il offrit là l’holocauste, le sacrifice, et la graisse des hosties pacifiques, parce que l’autel d’airain qui était devant le Seigneur était trop petit et ne pouvait contenir l’holocauste, le sacrifice et la graisse des hosties pacifiques.
A wannan rana sarki ya tsarkake sashe na tsakiyar fili a gaban haikalin Ubangiji, a can kuma ya miƙa hadaya ta ƙonawa, hadaya ta gari, da kitsen hadaya ta salama, gama bagaden tagulla a gaban Ubangiji ya yi ƙanƙanta sosai da za a miƙa hadayun ƙonawa, hadayun hatsi, da kuma kitsen hadayun salama.
65 Salomon fit donc en ce temps-là la fête célèbre, et tout Israël avec lui, une grande multitude étant accourue depuis l’entrée d’Emath jusqu’au fleuve d’Egypte, devant le Seigneur notre Dieu, durant sept jours et sept jours, c’est-à-dire durant quatorze jours.
Ta haka Solomon da dukan Isra’ila, wato, babban taro, suka yi bikin a lokacin. Mutane suka zo, tun daga Lebo Hamat har zuwa Rafin Masar. Suka yi biki a gaban Ubangiji Allahnmu, kwana bakwai. Suka kuma ƙara kwana bakwai, kwanaki goma sha huɗu gaba ɗaya.
66 Et, au huitième jour, il renvoya les peuples, qui, bénissant le roi, s’en allèrent dans leurs tabernacles avec allégresse et le cœur joyeux, pour tous les biens qu’avait faits le Seigneur à David son serviteur et à Israël son peuple.
A rana ta biye sai ya sallame mutane. Suka sa wa sarki albarka, sa’an nan suka watse zuwa gida, da farin ciki, da murna a zukatansu saboda kyawawan abubuwan da Ubangiji ya yi domin bawansa Dawuda, da kuma mutanensa Isra’ila.