< 1 Rois 3 >

1 La royauté fut donc affermie dans la main de Salomon; il s’unit par alliance à Pharaon, roi d’Egypte; car il prit sa fille, et il l’amena dans la cité de David, jusqu’à ce qu’il eût achevé de bâtir sa maison, et la maison du Seigneur, et le mur de Jérusalem tout autour.
Solomon ya haɗa kai da Fir’auna sarkin Masar, ya kuwa auri’yarsa. Ya kawo ta cikin Birnin Dawuda kafin yă gama ginin fadarsa, da haikalin Ubangiji, da kuma katanga kewaye da Urushalima.
2 Cependant le peuple immolait sur les hauts lieux; car il n’avait pas été bâti de temple au nom du Seigneur jusqu’à ce jour.
A lokacin dai mutane suna miƙa hadaya a wurare a bisa tuddai, domin ba a riga an gina haikali saboda Sunan Ubangiji ba.
3 Or, Salomon aima le Seigneur, marchant selon les préceptes de David son père, excepté qu’il sacrifiait sur les hauts lieux, et qu’il brûlait de l’encens.
Solomon ya ƙaunaci Ubangiji ta wurin yin tafiya bisa ga farillan mahaifinsa Dawuda, sai dai ya miƙa hadayu, ya kuma ƙone turare a wuraren nan na bisa tuddai.
4 C’est pourquoi il s’en alla à Gabaon pour y sacrifier; car c’était le haut lieu le plus grand; Salomon offrit mille hosties en holocauste sur cet autel à Gabaon.
Sai sarki Solomon ya tafi Gibeyon don yă miƙa hadayu, gama a can ne wuri mafi muhimmanci na sujada. Solomon kuwa ya miƙa hadayun ƙonawa guda dubu a kan wannan bagade.
5 Or le Seigneur apparut à Salomon en songe pendant la nuit, disant: Demande-moi ce que tu veux que je te donne.
A Gibeyon, Ubangiji ya bayyana ga Solomon da dare a mafarki, Allah ya ce, “Ka roƙi abin da kake so in ba ka.”
6 Et Salomon répondit: Vous avez fait à David mon père, votre serviteur, une grande miséricorde, selon qu’il a marché en votre présence dans la vérité, dans la justice et dans la droiture de cœur envers vous; vous lui avez conservé cette grande miséricorde; et vous lui avez donné un fils qui devait être assis sur son trône, comme il l’est aujourd’hui.
Solomon ya amsa ya ce, “Ka nuna alheri mai girma ga bawanka, mahaifina Dawuda domin ya yi aminci gare ka da adalci, ya kuma kasance da zuciya mai gaskiya. Ka ci gaba da wannan alheri mai girma gare shi, ka ba shi ɗa don yă zauna a kujerar sarautarsa a wannan rana.
7 Et maintenant, Seigneur Dieu, vous avez fait régner votre serviteur en la place de David, mon père: mais moi, je suis un petit enfant, ignorant mon entrée et ma sortie.
“Yanzu, ya Ubangiji Allahna, ka sa bawanka a wurin mahaifina Dawuda. Amma ni ɗan yaro ne kawai, ban kuma san yadda zan yi ayyukana ba.
8 Et votre serviteur est au milieu du peuple que vous avez choisi; d’un peuple infini, qui ne peut être nombre ni supputé à cause de sa multitude.
Bawanka yana nan a cikin mutanen da ka zaɓa, mutane masu girma, waɗanda suka wuce ƙirge, ko a lissafta.
9 Vous donnerez donc à votre serviteur un cœur docile, afin qu’il puisse juger votre peuple et discerner entre le bien et le mal; car qui pourra juger ce peuple-ci, ce peuple vôtre, si nombreux?
Saboda haka ka ba bawanka zuciyar ganewa, don yă shugabanci mutanenka, yă kuma iya rarrabe tsakanin abin da yake daidai da abin da ba daidai ba. Gama wa zai iya shugabance wannan mutanenka masu girma haka?”
10 Elle plut donc aux yeux du Seigneur la parole par laquelle Salomon avait demandé une telle chose.
Sai Ubangiji ya ji daɗi cewa Solomon ya roƙa wannan.
11 Et le Seigneur dit à Salomon: Parce que tu as demandé cette chose, et que tu n’as point désiré pour toi des jours nombreux, ni des richesses, ou les âmes de tes ennemis, mais que tu as demandé pour loi la sagesse, afin de discerner ce qui est juste,
Saboda haka Allah ya ce masa, “Da yake ka nemi wannan ne, ba ka kuwa nemi tsawon rai ko arziki wa kanka ba, ba ka kuma nemi mutuwar abokan gābanka ba, amma ka nemi ganewa a aikata gaskiya,
12 Voilà que j’ai fait envers toi selon tes paroles, et je t’ai donné un cœur sage et intelligent, tellement que nul avant toi n’a été semblable à toi, et qu’après toi il ne s’en élèvera point.
zan yi abin da ka roƙa. Zan ba ka zuciya mai hikima da ta ganewa, har yă zama ba a taɓa samun wani kamar ka ba, ba kuwa za a taɓa samunsa ba.
13 Mais même ce que tu n’as point demandé, je te l’ai donné, les richesses et la gloire, en sorte que personne n’aura été semblable à toi parmi les rois dans tous les jours passés.
Ban da haka ma, zan ba ka abin da ba ka nema ba; arziki da girma, don a rayuwarka ba za ka kasance da wani kamar ka ba a cikin sarakuna.
14 Or, si tu marches dans mes voies, et que tu gardes mes préceptes et mes commandements, comme a marché ton père, je prolongerai tes jours.
In kuma ka yi tafiya a hanyoyina, ka kuma yi biyayya da farillaina da umarnaina kamar yadda Dawuda mahaifinka ya yi, zan ba ka tsawon rai.”
15 Ainsi s’éveilla Salomon, et il comprit que c’était un songe; et, lorsqu’il fut venu à Jérusalem, il se présenta devant l’arche de l’alliance du Seigneur, offrit des holocaustes, sacrifia des victimes pacifiques, et fit un grand festin à tous ses serviteurs.
Sai Solomon ya farka, ya gane ashe mafarki ne. Ya koma Urushalima, ya tsaya a gaban akwatin alkawarin Ubangiji ya miƙa hadayun ƙonawa da hadayun salama. Sa’an nan ya shirya wa fadawansa biki.
16 Alors vinrent deux femmes de mauvaise vie vers le roi, et se présentèrent devant lui;
To, ana nan sai waɗansu karuwai biyu suka zo wurin sarki, suka tsaya a gabansa.
17 Et l’une dit: Je vous conjure, mon seigneur: moi et cette femme, nous habitions dans une même maison, et j’ai enfanté auprès d’elle dans la chambre.
Sai ɗaya ta ce, “Ranka yă daɗe, wannan mata da ni muna zama a gida ɗaya. Na haifi jariri yayinda take can tare da ni.
18 Mais le troisième jour après que moi j’ai enfanté, elle a enfanté, elle aussi, et nous étions ensemble, nul autre n’était dans la maison, excepté nous deux.
Kwana uku bayan haihuwar jaririna, wannan mata ma ta haifi jariri. Mu dai kaɗai ne; babu wani a gidan sai mu biyu.
19 Or le fils de cette femme est mort pendant la nuit; car en dormant elle l’a étouffé.
“Da dare ɗan wannan matan ya mutu domin ta kwanta a kansa.
20 Et, se levant dans le silence d’une profonde nuit, elle a pris mon fils à mon côté, pendant que je dormais, moi, votre servante, et l’a placé sur son sein; mais son fils, qui était mort, elle l’a posé sur mon sein.
Saboda haka ta tashi da tsakar dare ta ɗauki ɗana daga gefena yayinda baiwarka take barci. Sai ta sa shi kusa da ƙirjinta, ta kuma sa mataccen ɗanta kusa da ƙirjina.
21 Et lorsque je me suis levée le matin pour donner du lait à mon fils, il a paru mort; et, le considérant plus attentivement au grand jour, j’ai reconnu que ce n’était pas le mien que j’avais enfanté.
Kashegari, da na farka don in shayar da ɗana, sai na tarar ya mutu! Amma sa’ad da na dube shi da kyau da safe, sai na ga ashe ba ɗan da na haifa ba ne.”
22 Et l’autre femme répondit: Il n’en est pas ainsi que tu dis; mais ton fils est mort, et le mien vit. Au contraire, celle-là disait: Tu mens; car c’est mon fils qui vit, et le tien est mort. Et c’est de cette manière qu’elles disputaient devant le roi.
Amma ɗaya matar ta ce, “A’a! Mai rai ɗin ne ɗana; mataccen naki ne.” Amma ta farin ta nace, “A’a! Mataccen ne naki; mai ran ne nawa.” A haka suka yi ta gardama a gaban sarki.
23 Alors le roi dit: Celle-ci dit: Mon fils vit, et le tien est mort; et celle-là répond: Non; mais c’est ton fils qui est mort, et le mien vit.
Sarki ya ce, “Wannan ta ce, ‘Ɗana ne a raye, naki ne matacce,’ yayinda ɗayan tana cewa, ‘A’a! Ɗanki ne mataccen, nawa ne a raye.’”
24 Le roi dit donc: Apportez-moi un glaive. Et lorsqu’on eut apporté le glaive devant le roi,
Sai sarki ya ce, “Kawo mini takobi.” Sai aka kawo takobi wa sarki.
25 Coupez, dit-il, l’enfant vivant en deux parties, et donnez la moitié à l’une et la moitié à l’autre.
Ya ba da umarni ya ce, “Yanka yaron nan mai rai, gida biyu, kowacce ta ɗauki rabi.”
26 Alors la femme dont le fils était vivant dit au roi (car ses entrailles furent émues pour son fils): Je vous conjure, seigneur, donnez-lui l’enfant vivant, et ne le tuez point. Au contraire, l’autre disait: Qu’il ne soit ni à moi ni à toi; mais qu’il soit partagé.
Ainihin mamar ɗan da yake a raye ta cika da tausayi saboda ɗanta, sai ta ce wa sarki, “Ina roƙonka, ranka yă daɗe, kada ka kashe yaron! Ka ba ta kawai!” Amma ɗayan matar ta ce, “Kada a ba kowa daga cikinmu ɗan da rai, a ci gaba a raba shi!”
27 Le roi répondit, et dit: Donnez à celle-ci l’enfant vivant, et qu’il ne soit point tué; car c’est elle qui est sa mère.
Sai sarki ya zartar da hukuncinsa ya ce, “A ba da jariri mai ran ga mata ta fari. Kada a kashe shi; ita ce ainihin mahaifiyarsa.”
28 C’est pourquoi tout Israël apprit le jugement qu’avait rendu le roi; et ils craignirent le roi, voyant que la sagesse de Dieu était en lui pour rendre la justice.
Sa’ad da dukan Isra’ila suka ji hukuncin da sarki ya zartar, suka girmama sarki sosai, domin sun gane cewa Allah ya ba shi hikimar yin shari’ar adalci.

< 1 Rois 3 >