< 1 Rois 20 >
1 Or Bénadad, roi de Syrie, assembla toute son armée, et trente-deux rois avec lui, des chevaux et des chars; puis montant, il combattait contre Samarie, et l’assiégeait.
Ben-Hadad sarkin Aram kuwa ya tattara mayaƙansa gaba ɗaya. Sarakuna talatin da biyu suka tafi tare da shi haɗe da dawakansu da kekunan yaƙinsu. Ya haura ya yi wa Samariya kwanto, ya kuma yaƙe ta.
2 Et envoyant dans la ville des messagers à Achab, roi d’Israël,
Ya aika da’yan aika zuwa cikin birnin wurin Ahab sarkin Isra’ila yana cewa, “Ga abin da Ben-Hadad ya ce,
3 Il dit: Voici ce que dit Bénadad: Votre argent et votre or est à moi; vos femmes et vos enfants les meilleurs sont à moi.
‘Azurfarka da zinariyarka nawa ne. Mafi kyau cikin matanka da’ya’yanka nawa ne.’”
4 Et le roi d’Israël lui répondit: Selon votre parole, ô roi mon seigneur, je suis à vous, moi et tout ce que j’ai.
Sarkin Isra’ila ya amsa, ya ce, “Kamar dai yadda ka faɗa, ranka yă daɗe, sarki. Ni da dukan abin da nake da shi, naka ne.”
5 Et revenant, les messagers dirent: Voici ce que dit Bénadad, qui nous a envoyés vers vous: Vous me donnerez votre argent, votre or, vos femmes et vos fils.
Sai’yan aikan suka sāke dawo suka ce, “Ga abin da Ben-Hadad ya ce, ‘Na aika ka ba da azurfarka da zinariyarka, matanka da kuma’ya’yanka.
6 Demain donc, à cette même heure, j’enverrai mes serviteurs vers vous, et ils fouilleront votre maison et la maison de vos serviteurs, et tout ce qui leur plaira, ils le prendront en leurs mains et l’emporteront.
Amma war haka gobe zan aika shugabannina su bincika fadanka da kuma gidajen shugabanninka. Za su kwashe dukan abubuwan da kake ganin darajarsu su tafi.’”
7 Mais le roi d’Israël appela tous les anciens du pays, et dit: Considérez et voyez qu’il nous tend un piège; car il m’a envoyé pour mes femmes, pour mes fils, pour mon argent et mon or, et je n’ai pas refusé.
Sarkin Isra’ila ya tattara dukan dattawan ƙasar, ya ce musu, “Ku duba fa, wannan mutum yana neman tsokana! Sa’ad da ya aika in ba shi matana da’ya’yana, azurfana da zinariyana, ban hana masa ba.”
8 Tous les anciens et tout le peuple lui répondirent: Ne l’écoûtez point, et ne lui cédez point.
Dattawa da dukan mutane suka amsa, suka ce, “Kada ka saurare shi ko ka yarda da abin da yake bukata.”
9 C’est pourquoi Achab répondit aux messagers de Bénadad: Dites à mon seigneur le roi: Tout ce que vous m’avez demandé, à moi votre serviteur, au commencement, je le ferai, mais, quant à ceci, je ne le puis faire.
Saboda haka ya ba wa’yan aikan Ben-Hadad amsa, ya ce, “Ku faɗa wa ranka yă daɗe, sarki, ‘Bawanka zai yi dukan abin da ka bukaci da farko, amma wannan na ƙarshe ba zan iya yin ba.’” Suka tafi suka kai amsar wa Ben-Hadad.
10 Et, étant revenus, les messagers firent leur rapport à Bénadad, et Bénadad les envoya de nouveau, et dit: Que les dieux me fassent ceci, et qu’ils ajoutent cela, si la poussière de Samarie suffit pour remplir le creux de la main de tout le peuple qui me suit!
Sai Ben-Hadad ya aika da wani saƙo wa Ahab, ya ce, “Bari alloli su yi da ni yadda suke so, su kuma yi haka da tsanani, in isashen ƙura ta rage a Samariya da za a iya ba wa mutanena a tafin hannu.”
11 Et répondant, le roi d’Israël dit: Dites-lui: Que celui qui a mis sa ceinture, ne se glorifie point comme celui qui l’a ôtée.
Sarki Isra’ila ya amsa, ya ce, “Ku faɗa masa, ‘Wanda ya sa kayan yaƙinsa bai kamata yă yi fariya ba sai ya tuɓe su.’”
12 Or il arriva que lorsque Bénadad reçut cette réponse, il buvait, lui et les autres rois, dans leurs pavillons, et il dit à ses serviteurs: Investissez la ville. Et ils l’investirent.
Ben-Hadad ya ji wannan saƙo yayinda shi da sarakunan suke sha a cikin tentunansu, sai ya umarce mutanensa, ya ce, “Ku shirya don yaƙi.” Saboda haka suka shirya don su yaƙi birnin.
13 Et voilà qu’un prophète, s’approchant d’Achab, roi d’Israël, lui dit: Voici ce que dit le Seigneur: Sans doute que tu as vu toute cette multitude innombrable? voilà que moi je la livrerai en ta main aujourd’hui, afin que tu saches que c’est moi qui suis le Seigneur.
Ana cikin haka sai wani annabi ya zo wurin Ahab sarkin Isra’ila ya sanar masa cewa, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Ka ga wannan ɗumbun mayaƙa? Zan ba da su cikin hannunka a yau, sa’an nan za ka san cewa ni ne Ubangiji.’”
14 Et Achab lui demanda: Par qui? Et il lui répondit: Voici ce que dit le Seigneur: Par les serviteurs des princes des provinces. Achab ajouta: Qui commencera le combat? Et le prophète répondit: Toi.
Ahab ya ce, “Amma wa zai yi haka?” Annabin ya amsa, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Sojoji matasa na shugabannin yankuna za su yi haka.’” Ya tambaya, “Wa kuma zai fara yaƙin?” Annabin ya amsa, “Kai za ka fara.”
15 Achab fit donc la revue des serviteurs des princes des provinces, et il trouva le nombre de deux cent trente-deux; et après eux, il fit la revue du peuple de tous les enfants d’Israël, et il en trouva sept mille.
Saboda haka Ahab ya kira sojoji matasa na shugabannin yankuna, mutum 232. Sa’an nan ya tattara sauran Isra’ilawa su 7,000 gaba ɗaya.
16 Et ils sortirent à midi. Cependant Bénadad buvait, ivre, dans son pavillon, et avec lui les trente-deux rois qui étaient venus à son secours.
Suka fita da tsakar rana yayinda Ben-Hadad tare da sarakuna 32 masu goyon bayansa suke cikin tentunansu suna sha, suna buguwa.
17 Or les serviteurs des princes des provinces sortirent au premier rang. C’est pourquoi Bénadad envoya; et on lui annonça, en disant: Ce sont des hommes sortis de Samarie.
Sojojin nan matasa na shugabannin yankuna suka fara fita. Ben-Hadad kuwa ya riga ya aiki’yan leƙen asiri, waɗanda suka ce, “Mutane suna zuwa daga Samariya.”
18 Et lui répondit: Si c’est pour la paix qu’ils viennent, saisissez-les vivants; si c’est pour combattre, prenez-les vivants.
Ya ce, “In sun fito don salama, ku kamo su da rai; in sun fito yaƙi ne, ku kamo su da rai.”
19 Les serviteurs des princes des provinces sortirent donc, et le reste de l’armée suivait;
Sojojin nan matasa na shugabannin yankuna suka taka suka fita daga birnin da mayaƙa a bayansu.
20 Et chacun d’eux frappa celui qui venait contre lui; alors les Syriens s’enfuirent, et Israël les poursuivit. Bénadad, roi de Syrie, s’enfuit aussi à cheval avec ses cavaliers.
Kowannensu kuwa ya buge abokin gābansa. Ganin wannan, sai Arameyawa suka gudu, Isra’ilawa suna bi. Amma Ben-Hadad na Aram ya tsere a kan dokinsa tare da waɗansu mahayan dawakansa.
21 Et même le roi d’Israël, étant sorti, frappa les chevaux et les chariots, et frappa la Syrie d’une grande plaie.
Sarki Isra’ila ya bi, ya kuma sha ƙarfin dawakan da keken yaƙin, ya kashe Arameyawa da yawa.
22 (Alors le prophète, s’approchant du roi d’Israël, lui dit: Allez, fortifiez-vous, sachez et voyez ce que vous devez faire; car l’année suivante le roi de Syrie montera contre vous.)
Daga baya, annabin ya zo wurin sarkin Isra’ila ya ce, “Ka ƙarfafa matsayinka ka kuma ga abin da za a yi, gama a bazara mai zuwa sarkin Aram zai sāke kawo yaƙi.”
23 Mais les serviteurs du roi de Syrie lui dirent: Ce sont les dieux des montagnes, que leurs dieux, et c’est pourquoi ils nous ont vaincus; il vaut donc mieux que nous combattions contre eux dans les plaines, et nous l’emporterons sur eux.
Ana cikin haka, shugabannin sarkin Aram suka ba shi shawara, “Allolinsu, allolin tuddai ne. Shi ya sa suka fi mu ƙarfi. Amma in mun yaƙe su a fili, tabbatacce za mu fi su ƙarfi.
24 Vous donc, faites cette chose-ci: éloignez tous les rois de votre armée, et mettez des officiers en leur place;
Ka yi wannan. Ka cire dukan sarakuna daga matsayinsu ka sa waɗansu shugabanni a maimakonsu.
25 Rétablissez le nombre de ceux de vos soldats qui ont succombé, et autant de chevaux que les premiers chevaux, et autant de chariots que vous avez eu de chariots auparavant; et nous combattrons contre eux dans les plaines, et vous verrez que nous l’emporterons sur eux. Il crut leur conseil, et il fit ainsi.
Dole kuma ka tā da waɗansu mayaƙa kamar waɗanda ka rasa, doki don doki, keken yaƙi kuma don keken yaƙi, saboda mu iya yaƙe Isra’ila a fili. Ta haka tabbatacce za mu fi ƙarfinsu.” Sai ya yarda da su, ya kuma yi haka.
26 Ainsi après qu’un an fut passé, Bénadad fit la revue des Syriens, et il monta à Aphec pour combattre contre Israël.
Bazara na biye Ben-Hadad ya tattara Arameyawa, ya haura zuwa Afek don yă yaƙi Isra’ila.
27 Les enfants d’Israël furent aussi passés en revue; et, des vivres pris, ils partirent de leur côté, et campèrent vis-à-vis deux, comme deux petits troupeaux de chèvres, au lieu que les Syriens couvraient toute la terre.
Sa’ad da aka tattara Isra’ilawa, aka kuma ba su guzuri, sai suka taka suka fita don su sadu da Arameyawa. Isra’ilawa suka kafa sansani ɗaura da su kamar ƙananan garkuna biyu na awaki, yayinda Arameyawa suka rufe dukan jejin.
28 (Alors s’approchant, un homme de Dieu dit au roi d’Israël: Voici ce que dit le Seigneur: Parce que les Syriens ont dit: C’est le Dieu des montagnes que le Seigneur, et il n’est pas le Dieu des vallées, je mettrai toute cette grande multitude en ta main, et vous saurez que c’est moi qui suis le Seigneur.)
Sai mutumin Allah ya zo ya ce wa sarkin Isra’ila, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Domin Arameyawa suna tsammani Ubangiji allahn tuddai ne, ba allahn kwari ba, zan ba da wannan ɗumbun mayaƙa a hannuwanka, za ka kuwa sani ni ne Ubangiji.’”
29 Or durant sept jours ceux-ci et ceux-là rangèrent les armées en bataille, l’une vis-à-vis de l’autre, mais au septième jour la bataille fut engagée, et les enfants d’Israël tuèrent, parmi les Syriens, cent mille hommes de pied en un seul jour.
Kwana bakwai suka yi sansani ɗaura da juna, a rana ta bakwai sai yaƙi ya haɗu. Isra’ilawa suka kashe sojojin kafa na Arameyawa dubu ɗari a rana ɗaya.
30 Et ceux qui étaient restés s’enfuirent dans la ville d’Aphec, et le mur tomba sur vingt-sept mille hommes qui étaient restés. Quant à Bénadad, fuyant, il entra dans la ville, et se retira dans une chambre, qui était dans sa chambre;
Sauransu suka tsere zuwa birnin Afek, inda katangar ya fāɗa a kan mutum dubu ashirin da bakwai. Sai Ben-Hadad ya gudu zuwa birni ya ɓuya a ciki cikin ɗaki.
31 Et ses serviteurs lui dirent: Voilà que nous avons ouï dire que les rois de la maison d’Israël sont cléments: mettons donc des sacs sur nos reins et des cordes à nos têtes, et sortons vers le roi d’Israël; peut-être qu’il sauvera nos âmes.
Fadawansa suka je suka ce masa, “Mun ji an ce sarakunan Isra’ila masu jinƙai ne, bari mu sa tufafin makoki, mu ɗaura igiyoyi a wuyanmu, sa’an nan mu tafi wurin sarkin Isra’ila, wataƙila zai bar ka da rai.”
32 Ils ceignirent donc de sacs leurs reins, mirent des cordes à leurs têtes, vinrent vers le roi d’Israël, et lui dirent: Votre serviteur Bénadad dit: Je vous prie, que mon âme vive. Et lui répondit: S’il vit encore, il est mon frère.
Saye da tufafin makoki kewaye a gindinsu, da kuma igiyoyi kewaye da kawunansu, suka tafi wurin sarkin Isra’ila, suka ce, “Bawanka Ben-Hadad ya ce, ‘Ina roƙonka bari in rayu.’” Sarki ya amsa, “Har yanzu yana da rai? Shi ɗan’uwana ne.”
33 Ce que les Syriens prirent pour un heureux présage; et, se hâtant, ils saisirent cette parole de sa bouche et dirent: Bénadad est votre frère. Et il leur répondit: Allez, et amenez-le-moi. Bénadad sortit donc vers Achab, qui le fit monter sur son char.
Da ma abin da fadawan suke so su ji ke nan, sai suka yi sauri, suka karɓi maganar a bakinsa, suka ce, “I, ɗan’uwanka, Ben-hadad!” Sarki ya ce, “Ku je ku kawo shi.” Da Ben-Hadad ya fita, sai Ahab ya sa aka kawo shi cikin keken yaƙinsa.
34 Et Bénadad lui dit: Je vous rendrai les villes que mon père a prises à votre père; et faites-vous des places publiques dans Damas, comme s’en fit mon père dans Samarie; et moi, ainsi allié, je me retirerai d’auprès de vous. Achab fit donc alliance, et le laissa aller.
Ben-Hadad ya ce, “Zan mayar da biranen mahaifinka da na ƙwace daga mahaifinka. Za ka iya sa wurin kasuwarka a cikin Damaskus, kamar yadda mahaifinka ya yi a Samariya.” Ahab ya ce, “Bisa wannan yarjejjeniya zan sake ka.” Saboda haka ya yi yarjejjeniya da shi, sai ya bar shi ya tafi.
35 Alors un certain homme d’entre les fils des prophètes dit à son compagnon avec la parole du Seigneur: Frappe-moi. Mais comme celui-ci ne voulut pas le frapper,
Ta wurin maganar Ubangiji, ɗaya daga cikin’ya’ya maza na annabawa ya ce wa abokinsa, “Ka buge ni da makaminka,” amma mutumin ya ƙi.
36 Il lui dit: Parce que tu n’as pas voulu écouter la voix du Seigneur, tu t’éloigneras de moi, et le lion te tuera. Lorsqu’il fut un peu éloigné de lui, le lion le trouva et le tua.
Sai annabin ya ce, “Domin ba ka yi biyayya da Ubangiji ba, da zarar ka bar ni zaki zai kashe ka.” Daga baya mutumin ya tafi, zaki ya same shi, ya kuma kashe shi.
37 Mais rencontrant aussi un autre homme, il lui dit: Frappe-moi. Cet homme le frappa et le blessa.
Annabin ya sami wani mutum ya ce, “Ka buge ni, ina roƙonka.” Sai mutumin ya buge shi, ya ji masa ciwo.
38 Le prophète s’en alla donc, et vint à la rencontre du roi dans la voie, et il changea, en y répandant de la poussière, son visage et ses yeux.
Sa’an nan annabin ya tafi ya tsaya a bakin hanya yana jiran sarki. Ya ɓad da kamanni da ƙyalle a kansa. Ƙyallen ya sauka zuwa bisa idanunsa.
39 Et lorsque le roi fut passé, il cria après lui, et dit: Votre serviteur est sorti pour combattre de près, et, comme un homme s’est enfui, quelqu’un me l’a amené, et a dit: Garde cet homme; et, s’il s’échappe, ton âme sera pour son âme, ou tu pèseras un talent d’argent.
Yayinda sarki yake wucewa, sai annabin ya yi kira da ƙarfi gare shi ya ce “Ni bawanka na tafi yaƙi, sai ga wani ya kawo mini wani mutum, ya ce, ‘Ka riƙe wannan mutum, kada ka bar shi yă kuɓuta ko da ƙaƙa, idan ka bari ya kuɓuta, a bakin ranka, ko kuwa ka biya talanti ɗaya na azurfa.’
40 Mais tandis que moi, troublé, je me tournais ici et là, il a subitement disparu. Et le roi d’Israël lui dit: C’est ton jugement que toi-même tu as prononcé.
Yayinda bawanka yana fama, yana kai da kawowa, sai mutumin ya ɓace.” Sai sarkin Isra’ila ya ce, “Hukuncinka ke nan, ka furta shi da kanka.”
41 Mais lui aussitôt essuya la poussière de son visage, et le roi d’Israël reconnut qu’il était du nombre des prophètes.
Sai annabin ya cire ƙyallen da sauri daga kansa, da ya rufe idanunsa, sarkin Isra’ila kuwa ya gane shi a matsayi ɗaya daga cikin annabawa.
42 Il dit au roi: Voici ce que dit le Seigneur: Parce que tu as laissé échapper de ta main un homme digne de mort, ta vie sera pour sa vie, et ton peuple pour son peuple.
Sai ya ce wa sarki, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Ka saki mutumin da na ƙudura yă mutu. Saboda haka ranka zai zama a maimakon ransa, mutanenka a maimakon mutanensa.’”
43 Le roi d’Israël retourna donc en sa maison, dédaignant d’entendre, et, plein de fureur, il vint dans Samarie.
Cike da fushi, sarkin Isra’ila ya tafi fadarsa a Samariya.