< 1 Rois 14 >
1 En ce temps-là, Abia, fils de Jéroboam, fut malade,
A lokacin Abiya, ɗan Yerobowam ya kamu da ciwo,
2 Et Jéroboam dit à sa femme: Lève-toi, change de vêtement, pour qu’on ne sache point que tu es femme de Jéroboam, et va à Silo, où est Ahias le prophète, qui m’a dit que je devais régner sur ce peuple.
sai Yerobowam ya ce wa matarsa, “Ki tafi, ki ɓad da kama, don kada a gane ke a matsayin matar Yerobowam. Ki je Shilo. Annabi Ahiya yana a can, wannan wanda ya ce mini zan zama sarki a bisa wannan mutane.
3 Prends aussi en ta main dix pains, une galette et un vase de miel, et va vers lui; car lui-même t’indiquera ce qui doit arriver à cet enfant.
Ki ɗauki dunƙulen burodi goma tare da ke, da waina, da tulun zuma, ki tafi wurinsa. Zai faɗa miki abin da zai faru da yaron.”
4 La femme de Jéroboam fit comme il avait dit; et, se levant, elle alla à Silo, et vint dans la maison d’Ahias; mais celui-ci ne pouvait voir, parce que ses yeux s’étaient obscurcis à cause de sa vieillesse.
Saboda haka matar Yerobowam ta yi abin da ya faɗa, ta kuma tafi gidan Ahiya a Shilo. Yanzu dai Ahiya ba ya gani; idanunsa sun tafi saboda tsufa.
5 Or le Seigneur dit à Ahias: Voilà que la femme de Jéroboam vient te consulter sur son fils qui est malade: tu lui diras ceci et cela. Comme donc elle entrait, et dissimulait qui elle était,
Amma Ubangiji ya ce wa Ahiya, “Matar Yerobowam tana zuwa tă tambaye ka game da ɗanta, gama yana ciwo, za ka kuwa ba ta amsa kaza da kaza. Sa’ad da ta iso za tă yi kamar wata ce dabam.”
6 Ahias entendit le bruit de ses pieds lorsqu’elle entrait à la porte, et il dit: Entrez, femme de Jéroboam: pourquoi feignez-vous d’être une autre? Pour moi, je vous suis envoyé comme un messager funeste.
Saboda haka sa’ad da Ahiya ya ji motsin sawunta a ƙofa, sai ya ce, “Ki shigo, matar Yerobowam. Me ya sa kike yi kamar wata ce dabam? An aiko ni wurinki da labari marar daɗi.
7 Allez, et dites à Jéroboam: Voici ce que dit le Seigneur Dieu d’Israël: Je t’ai élevé du milieu du peuple, et je t’ai établi chef sur mon peuple Israël;
Je ki faɗa wa Yerobowam cewa ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, ‘Na tā da kai daga cikin mutane, na mai da kai shugaba a bisa mutanena Isra’ila.
8 Et j’ai divisé le royaume de la maison de David et te l’ai donné; et tu n’as point été comme mon serviteur David, qui a gardé mes commandements, et qui m’a suivi en tout son cœur, faisant tout ce qui était agréable en ma présence;
Na yage mulki daga gidan Dawuda na ba da shi gare ka, amma ba ka zama kamar bawana Dawuda wanda ya kiyaye umarnaina ya kuma bi ni da dukan zuciyarsa, yana yin abin da yake daidai kaɗai a idanuna ba.
9 Mais tu as fait plus de maux que tous ceux qui ont été avant toi, et tu t’es fait des dieux étrangers et jetés en fonte, pour me provoquer au courroux, et tu m’as rejeté derrière toi.
Ka aikata mugunta fiye da dukan waɗanda suka rayu kafin kai. Ka yi wa kanka waɗansu alloli, gumakan da aka yi da ƙarfe; ka tsokane ni na yi fushi, ka kuma juye mini baya.
10 C’est pourquoi voilà que j’amènerai des maux sur la maison de Jéroboam, et je frapperai de Jéroboam celui qui urine contre une muraille, celui qui est renfermé, et celui qui est le dernier dans Israël; et je nettoyerai les restes de la maison de Jéroboam, comme on a coutume de nettoyer le fumier, jusqu’à ce que tout soit net.
“‘Saboda wannan, zan kawo masifa a gidan Yerobowam. Zan yanke kowane ɗa na ƙarshe a Isra’ila, bawa ko’yantacce. Zan ƙone gidan Yerobowam kamar yadda mutum yakan ƙone juji, sai duk ya ƙone ƙurmus.
11 Ceux de Jéroboam qui mourront dans la ville, les chiens les mangeront, et ceux qui mourront dans la campagne, les oiseaux du ciel les dévoreront, parce que c’est le Seigneur qui a parlé.
Karnuka za su ci waɗanda suka mutu na Yerobowam a cikin birni, kuma tsuntsayen sararin sama za su cinye waɗanda suka mutu a jeji. Ni Ubangiji na faɗa!’
12 Vous donc, levez-vous, et allez en votre maison; et, à l’entrée même de vos pieds dans la ville, l’enfant mourra,
“Ke kuma, ki koma gida. Sa’ad da kika taka ƙafa a birninki, yaron zai mutu.
13 Et tout Israël le pleurera et l’ensevelira; car c’est le seul de Jéroboam qui sera porté dans un sépulcre, parce qu’il a été trouvé en lui quelque chose de bon par le Seigneur Dieu d’Israël dans la maison de Jéroboam.
Dukan Isra’ila kuwa za su yi makoki dominsa. Shi ne kaɗai na Yerobowam wanda za a binne, domin shi ne kaɗai a gidan Yerobowam wanda Ubangiji, Allah na Isra’ila ya sami wani ɗan abu mai kyau a kansa.
14 Mais le Seigneur s’est établi un roi sur Israël, qui frappera la maison de Jéroboam en ce jour et en ce temps;
“Ubangiji zai tā da wani sarki wa kansa a bisa Isra’ila wanda zai hallaka iyalin Yerobowam. Ko yanzu ma, wannan zai fara faruwa.
15 Et le Seigneur Dieu frappera Israël comme le roseau a coutume d’être agité dans l’eau, et il arrachera Israël de la bonne terre qu’il a donnée à leurs pères, et il les dispersera au-delà du fleuve, parce qu’ils se sont fait des bois sacrés pour irriter le Seigneur.
Ubangiji kuma zai bugi Isra’ila, har tă zama kamar kyauro mai girgiza a bakin rafi. Zai tumɓuke Isra’ila daga wannan ƙasa mai kyau da ya ba wa kakanninsu, yă watsar da su gaba da Kogin Yuferites domin sun tsokane Ubangiji har ya yi fushi, ta wurin yin ginshiƙan Ashera.
16 Et le Seigneur livrera Israël à cause des péchés de Jéroboam, qui a péché et qui a fait pécher Israël.
Zai kuma ba da Isra’ila saboda zunuban da Yerobowam ya yi, da ya kuma sa Isra’ila suka yi.”
17 C’est pourquoi la femme de Jéroboam se leva, s’en alla, et vint à Thersa; et lorsqu’elle entrait sur le seuil de la porte de sa maison, l’enfant mourut,
Sai matar Yerobowam ta tashi ta tafi, ta kuwa tafi Tirza. Nan da nan da ta taka madogarar ƙofar gidan, sai yaron ya mutu.
18 Et on l’ensevelit. Et tout Israël le pleura, selon la parole du Seigneur qu’il avait dite par l’entremise de son serviteur Ahias, le prophète.
Suka binne shi, dukan Isra’ila kuwa suka yi makoki dominsa, yadda Ubangiji ya faɗa ta wurin bawansa annabi Ahiya.
19 Mais le reste des actions de Jéroboam, comment il combattit, et comment il régna, voilà que c’est écrit dans le Livre des actions des jours des rois d’Israël.
Sauran ayyukan sarautar Yerobowam, da yaƙe-yaƙensa, da yadda ya yi mulki, ba a rubuce suke a littafin tarihi na sarakunan Isra’ila ba?
20 Or les jours durant lesquels Jéroboam régna furent de vingt-deux ans, et il dormit avec ses pères, et Nadab, son fils, régna en sa place.
Ya yi mulki shekaru ashirin da biyu, sai ya huta tare da kakanninsa. Sai Nadab ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
21 Cependant Roboam, fils de Salomon régnait sur Juda. Roboam avait quarante-un ans lorsqu’il commença à régner, et il régna dix-sept ans dans la ville de Jérusalem, que le Seigneur avait choisie d’entre toutes les tribus d’Israël pour y établir son nom. Or le nom de sa mère était Naama, l’Ammanite.
Rehobowam ɗan Solomon ya zama sarki a Yahuda. Yana da shekara arba’in da ɗaya sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki shekaru goma sha bakwai a Urushalima, birnin da Ubangiji ya zaɓa daga cikin dukan kabilan Isra’ila don yă sa Sunansa. Sunan mahaifiyarsa Na’ama, ita mutuniyar Ammon ce.
22 Et Juda fit le mal aux yeux du Seigneur, et ils l’irritèrent au-delà de tout ce qu’avaient fait leurs pères, dans les péchés dont ils s’étaient rendus coupables,
Yahuda ya aikata mugunta a gaban Ubangiji. Ta wurin zunuban da suka yi, sun tā da fushin kishinsa fiye da yadda kakanninsu suka yi.
23 Car ils se firent, eux aussi, des autels, des statues et des bois sacrés sur toute colline élevée et sous tout arbre couvert de feuillage.
Sun kuma kafa wa kansu masujadai da suke kan tuddai, da a kan keɓaɓɓun duwatsu, suka kuma gina ginshiƙan Ashera a kowane tudu, da kuma a ƙarƙashin kowane duhuwar itace.
24 Il y eut aussi des efféminés dans leur terre, et ils commirent toutes les abominations de ces nations que le Seigneur avait détruites devant la face des enfants d’Israël.
Har ma akwai maza karuwai na masujada. Mutane suka sa kansu ga yin kowane abin ƙyama na al’umman da Ubangiji ya kora kafin Isra’ilawa.
25 Or en la cinquième année du règne de Roboam, Sésac, roi d’Egypte, monta à Jérusalem,
A shekara ta biyar ta Sarki Rehobowam, Shishak sarkin Masar ya kai wa Urushalima yaƙi.
26 Et il enleva les trésors de la maison du Seigneur et les trésors du roi, et il pilla tout, même les boucliers d’or qu’avait faits Salomon,
Ya kwashe dukiyar haikalin Ubangiji da kuma dukiyar fadan sarki. Ya ɗauki kome, har da dukan garkuwoyi na zinariya da Solomon ya yi.
27 En la place desquels le roi Roboam fit des boucliers d’airain, et il les mit entre les mains des chefs des scutaires, et de ceux qui veillaient devant la porte de la maison du roi.
Saboda haka sarki Rehobowam ya yi garkuwoyin tagulla ya mayar da su. Ya kuma naɗa waɗannan shugabannin matsara ya sa su aiki a ƙofar zuwa fadan sarki.
28 Et lorsque le roi entrait dans la maison du Seigneur, ceux dont l’office était de marcher devant lui portaient ces boucliers, et ensuite ils les reportaient dans l’arsenal des scutaires.
Duk sa’ad da sarki ya tafi wurin haikalin Ubangiji, matsara sukan riƙe garkuwoyinsu, daga baya kuma sai su mai da su ɗakin tsaro.
29 Mais le reste des actions de Roboam, et tout ce qu’il a fait, voilà que c’est écrit dans le Livre des actions des jours des rois de Juda.
Game da sauran ayyukan mulkin Rehobowam kuwa, da kuma dukan abin da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
30 Et il y eut guerre entre Roboam et Jéroboam durant tous leurs jours.
Aka ci gaba da yaƙe-yaƙe tsakanin Rehobowam da Yerobowam.
31 Et Roboam dormit avec ses pères, et il fut enseveli avec eux dans la cité de David. Le nom de sa mère était Naama l’Ammanite, et Abiam son fils régna en sa place.
Sai Rehobowam ya huta da kakanninsa, aka kuma binne shi tare da su a Birnin Dawuda. Sunan mahaifiyarsa Na’ama, ita kuwa mutuniyar Ammon ce. Sai Abiyam ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.