< 1 Rois 11 >

1 Or le roi Salomon aima beaucoup de femmes étrangères, la fille de Pharaon aussi, et des Moabites, des Ammonites, des Iduméennes, des Sidoniennes et des Héthéennes,
Sarki Solomon ya ƙaunaci baƙin mata. Ban da’yar Fir’auna, ya auri Mowabawa, Ammonawa, mutanen Edom, Sidoniyawa da Hittiyawa.
2 De nations dont le Seigneur avait dit aux enfants d’Israël: Vous ne vous approcherez point d’elles, et les hommes d’entre elles ne s’approcheront point de vos filles; car très certainement elles pervertiront vos cœurs, pour que vous suiviez leurs dieux. C’est pourquoi Salomon s’attacha à ces femmes par un très ardent amour.
Sun fito daga al’ummai da Ubangiji ya ce wa Isra’ilawa, “Kada ku yi aurayya da su, domin tabbatacce za su juye zukatanku zuwa ga waɗansu alloli.” Duk da haka Solomon ya manne musu, ya nace, yana ƙaunarsu.
3 Et il eut sept cents femmes qui étaient comme reines, et trois cents du second rang; et ses femmes pervertirent son cœur.
Ya auri mata ɗari bakwai, haifaffun gidan sarauta, da kuma ƙwarƙwarai ɗari uku. Matan nan nasa suka karkatar da shi.
4 Et lorsqu’il était déjà vieux, son cœur fut dépravé par les femmes, en sorte qu’il suivait des dieux étrangers; et son cœur ne fut point parfait devant le Seigneur son Dieu, comme le cœur de David son père.
Yayinda Solomon yake tsufa, matansa suka juye zuciyarsa ga bin waɗansu alloli, zuciyarsa kuwa ba tă bi Ubangiji Allahnsa ɗungum kamar yadda zuciyar Dawuda mahaifinsa ta kasance ba.
5 Mais Salomon servait Astarthé, déesse des Sidoniens, et Moloch, idole des Ammonites.
Ya bi Ashtarot, alliyar Sidoniyawa, da Molek, allahn da aka hana na Ammonawa.
6 Ainsi Salomon fit ce qui ne plaisait pas au Seigneur, et il n’acheva pas de suivre le Seigneur, comme David son père.
Saboda haka Solomon ya yi abin da yake mugu a gaban Ubangiji. Bai bi Ubangiji gaba ɗaya kamar yadda Dawuda mahaifinsa ya yi ba.
7 C’est alors que Salomon bâtit un temple à Chamos, idole des Moabites, sur la montagne qui est contre Jérusalem, et à Moloch, idole des enfants d’Ammon.
A kan tudu, gabas da Urushalima, Solomon ya gina masujada a can domin Kemosh, allahn da aka hana na Mowab, da Molek, allahn da aka hana na Ammonawa.
8 Et c’est de cette manière qu’il fit pour toutes ses femmes étrangères, qui brûlaient de l’encens et sacrifiaient à leurs dieux.
Ya yi haka domin dukan baƙin matansa, waɗanda suka ƙone turare suka kuma miƙa hadayu ga allolinsu.
9 Aussi le Seigneur fut-il irrité contre Salomon, de ce que son esprit s’était détourné du Seigneur Dieu d’Israël, qui lui avait apparu une seconde fois,
Ubangiji ya yi fushi da Solomon domin zuciyarsa ya juye daga Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda ya bayyana masa sau biyu.
10 Et qui lui avait ordonné à ce sujet de ne point suivre des dieux étrangers: et il ne garda pas ce que lui commanda le Seigneur.
Ko da yake ya hana Solomon bin waɗansu alloli, Solomon bai kiyaye umarnin Ubangiji ba.
11 C’est pourquoi le Seigneur dit à Salomon; Puisque tu as ce péché en toi, et que tu n’as point gardé mon alliance et mes préceptes que je t’ai prescrits, je déchirerai et diviserai ton royaume, et je le donnerai à ton serviteur.
Saboda haka Ubangiji ya ce wa Solomon, “Da yake halinka ke nan, ba ka kuma kiyaye alkawarina, da ƙa’idodina da na umarce ka ba, tabbatacce zan yage masarautar daga gare ka, in ba da ita ga ɗaya daga cikin bayinka.
12 Cependant, je ne le ferai pas durant tes jours, à cause de David, ton père; mais c’est venant de la main de ton fils que je le diviserai;
Amma saboda Dawuda mahaifinka, ba zan yi haka a zamaninka ba. Zan yage ta daga hannun ɗanka.
13 Et je n’ôterai pas tout le royaume: mais je donnerai une tribu à ton fils, à cause de David, mon serviteur, et de Jérusalem, que j’ai choisie.
Amma ba zan yage dukan masarautar daga gare shi ba, zan ba shi kabila ɗaya saboda Dawuda bawana, da kuma saboda Urushalima, wadda na zaɓa.”
14 Or le Seigneur suscita pour ennemi à Salomon, Adad, l’Iduméen de la race royale, qui était dans Edom.
Sai Ubangiji ya tayar wa Solomon wani abokin gāba, mai suna Hadad, mutumin Edom daga gidan sarautar Edom.
15 Car lorsque David était dans l’Idumée, et que Joab, prince de la milice, eut monté pour ensevelir ceux qui avaient été tués, et qu’il eut tué tout mâle dans l’Idumée
A shekarun baya Dawuda ya ci Edom da yaƙi. Yowab, shugaban sojojinsa ya tafi can domin yă binne Isra’ilawa waɗanda suka mutu a yaƙi. Sa’ad da suke a can, sojojin Isra’ila suka kashe kowane ɗa namiji a Edom.
16 (Car Joab y demeura six mois et toute l’armée d’Israël, pendant qu’il tuait tout mâle dans l’Idumée),
Yowab da dukan Isra’ilawa suka zauna a can, wata shida, sai da suka hallaka dukan mutane a Edom.
17 Adad s’enfuit, lui et des Iduméens, serviteurs de son père, avec lui, pour entrer en Egypte; or Adad était alors un petit enfant.
Amma Hadad yana ɗan yaro a lokaci, wanda ya gudu zuwa Masar tare da shugabannin mutanen Edom waɗanda suka yi wa mahaifinsa hidima.
18 Et lorsqu’ils furent sortis de Madian, ils vinrent à Pharan; puis ils prirent avec eux des hommes de Pharan, et ils entrèrent en Egypte, auprès de Pharaon, roi d’Egypte, qui donna à Adad une maison, lui assigna des vivres, et lui attribua une terre.
Suka taso daga Midiyan suka tafi Faran. Sa’an nan suka ɗauki mutane daga Faran suka tafi Masar, zuwa wurin Fir’auna wanda ya ba wa Hadad gida da ƙasa, ya kuma tanada masa da abinci.
19 Et Adad trouva tout à fait grâce devant Pharaon, tellement qu’il lui donna pour femme la sœur germaine de sa propre femme, de Taphnès, la reine.
Fir’auna ya ji daɗin Hadad har ya ba shi’yar’uwar matarsa, Sarauniya Tafenes, aure.
20 Et cette sœur de la reine lui enfanta un fils, Génubath, et Taphné le nourrit dans la maison de Pharaon; ainsi Génubath habitait auprès de Pharaon avec ses enfants.
’Yar’uwar Tafenes ta haifi masa ɗa wanda ya kira Genubat, wanda Tafenes ta yi renonsa a fadan sarki. A can, Genubat ya yi zama da’ya’yan Fir’auna.
21 Lorsqu’Adad eut appris, en Egypte, que David s’était endormi avec ses pères, et que Joab, prince de la milice, était mort, il dit à Pharaon: Laissez-moi aller, afin que je retourne en mon pays.
Yayinda yake a Masar, Hadad ya ji Dawuda ya huta tare da kakanninsa, ya kuma ji cewa Yowab shugaban mayaƙa ya mutu. Sai Hadad ya ce wa Fir’auna, “Bari in tafi, don in koma ƙasata.”
22 Et Pharaon lui dit: Mais de quoi manques-tu chez moi, pour que tu cherches à aller en ton pays? Et Adad lui répondit: De rien; mais je vous conjure de me laisser aller.
Fir’auna ya tambaye shi, ya ce, “Me ka rasa a nan da kake so ka koma garinka?” Ya ce, “Ba kome, amma ka dai bar ni in tafi!”
23 Dieu suscita aussi pour ennemi à Salomon, Razon, fils d’Eliada, qui s’était enfui d’auprès d’Adarézer, roi de Soba, son seigneur,
Allah kuwa ya tayar wa Solomon wani abokin gāba, mai suna Rezon, ɗan Eliyada, wanda ya gudu daga maigidansa, Hadadezer sarkin Zoba.
24 Qui assembla des hommes contre David, et devint chef de voleurs, lorsque David les tuait; et ils allèrent à Damas, ils y habitèrent, et l’établirent roi à Damas.
Rezon ya tattara mutane kewaye da shi, ya zama kuma shugaban’yan tawaye sa’ad da Dawuda ya hallaka mayaƙan Zoba;’yan tawayen suka tafi Damaskus, inda suka zauna, suka kuma yi mulki.
25 Et il fut ennemi d’Israël durant tous les jours de Salomon. Voilà le mal que fit Adad, et sa haine contre Israël; ainsi, il régna en Syrie.
Rezon ya zama babban abokin gāban Isra’ila cikin dukan kwanakin mulkin Solomon. Ya ƙara rikici a kan rikicin Hadad. Rezon ya ƙi mulkin Isra’ila da dukan ransa. Saboda haka Rezon ya yi mulki a Aram ya kuma ƙi jinin Isra’ila.
26 Jéroboam aussi, fils de Nabath, Ephrathéen, de Saréda, serviteur de Salomon, dont la mère, femme veuve, avait pour nom Sarva, leva la main contre le roi.
Haka ma Yerobowam, ɗan Nebat, shi ma ya yi wa sarki tawaye. Shi ɗaya ne daga shugabannin Solomon, shi mutumin Efraim ne daga Zereda, mahaifiyarsa kuwa gwauruwa ce, mai suna Zeruwa.
27 Et la cause de sa révolte est que Salomon avait bâti Mello, et comblé l’abîme de la cité de David son père.
Ga yadda ya tayar wa sarki Solomon. Sarki Solomon ya gina madogaran gini, ya ciccika wurare a katangar birnin Dawuda mahaifinsa da ƙasa.
28 Or Jéroboam était un homme fort et puissant; et Salomon, voyant ce jeune homme d’un bon naturel et laborieux, l’établit intendant des tributs de toute la maison de Joseph.
To, Yerobowam mutum ne mai fasaha. Sa’ad da Solomon ya ga yadda matashin yake aiki da himma, sai ya sa shi yă lura da dukan aikin gandu na gidan Yusuf.
29 Il arriva donc en ce temps-là que Jéroboam sortit de Jérusalem, et qu’Aias, le Silonite, le prophète, couvert d’un manteau neuf, le rencontra dans le chemin; or eux deux seulement étaient dans la campagne.
Da Yerobowam ya fita Urushalima, sai annabi Ahiya, mutumin Shilo ya tarar da shi a hanya. Lokacin kuwa Ahiya yana saye da sabuwar riga, ba kowa a filin sai su biyu kaɗai.
30 Et Ahias, prenant son manteau neuf dont il était couvert, le coupa en douze parts,
Sai Ahiya ya kama sabuwar rigar da yake saye da ita ya yage ta gida goma sha biyu.
31 Et dit à Jéroboam: Prenez, pour vous ces dix lambeaux; car le Seigneur Dieu d’Israël dit ceci: Voilà que moi je diviserai le royaume venant de la main de Salomon, et que je te donnerai dix tribus.
Sa’an nan ya ce wa Yerobowam, “Ɗauki gida goma wa kanka, gama abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce ke nan, ‘Duba, zan yage masarauta daga hannun Solomon in ba ka kabilu goma.
32 Mais une tribu lui restera, à cause de mon serviteur David, et de la ville de Jérusalem, que j’ai choisie d’entre toutes les tribus d’Israël;
Amma saboda bawana Dawuda da kuma birnin Urushalima, wadda na zaɓa daga dukan kabilan Isra’ila, zai sami kabila guda.
33 Parce que Salomon m’a abandonné, et qu’il a adoré Astarthé, déesse des Sidoniens, Chamos, dieu de Moab, et Moloch, dieu des enfants d’Ammon; et qu’il n’a point marché dans mes voies, pour pratiquer la justice devant moi, mes préceptes et mes ordonnances, comme David, son père.
Zan yi wannan domin sun yashe ni, suka kuma yi wa Ashtarot, alliyar Sidoniyawa, da Kemosh, allahn Mowabawa, da kuma Molek, allahn Ammonawa sujada, ba su yi tafiya a hanyoyina ba, ba su kuwa yi abin da yake daidai a idanuna ba, ba su kiyaye farillaina da dokokina kamar yadda Dawuda, mahaifin Solomon ya yi ba.
34 Je n’ôterai pas tout le royaume de sa main; mais je l’en laisserai chef durant tous les jours de sa vie, à cause de David, mon serviteur, que j’ai choisi, qui a gardé mes commandements et mes préceptes.
“‘Amma ba zan ɗauki dukan masarautar daga hannun Solomon ba; na naɗa shi sarki, dukan kwanaki ransa saboda Dawuda bawana, wanda na zaɓa, wanda kuma ya kiyaye umarnai da farillaina.
35 Mais j’ôterai le royaume de la main de son fils, et je te donnerai dix tribus;
Zan ɗauke masarautar daga hannuwan ɗansa ne, in ba ka kabilu goma.
36 Et quant à son fils, je lui donnerai une tribu, afin qu’il demeure une lampe à David, mon serviteur, tous les jours, devant moi dans la ville de Jérusalem, que j’ai choisie, afin que mon nom soit là.
Zan ba da ɗaya ga ɗansa don kullum Dawuda bawana yă kasance da fitila a gabana a Urushalima, birnin da na zaɓa in sa Sunana.
37 Mais, toi, je le prendrai, et tu régneras sur tout ce que désire ton âme, et tu seras roi sur Israël.
Amma fa, ga kai, zan ɗauke ka, za ka kuwa yi mulki bisa dukan abin da zuciyarka take so; za ka zama sarki a bisa Isra’ila.
38 Si donc tu écoutes tout ce que je t’ordonne, et si tu marches dans mes voies, et que tu fasses ce qui est droit devant moi, gardant mes commandements et mes préceptes, comme a fait David, mon serviteur, je serai avec toi, et je te bâtirai une maison fidèle, comme j’ai bâti à David une maison, et je te livrerai Israël;
In ka aikata dukan abin da na umarce ka, ka yi tafiya a hanyoyina, ka kuma yi abin da yake daidai a idanuna ta wurin kiyaye farillaina da umarnaina, kamar yadda Dawuda bawana ya yi, zan kasance tare da kai. Zan gina maka masarauta mai dawwama kamar wadda na gina wa Dawuda, zan kuma ba da Isra’ila gare ka.
39 Et j’affligerai en cela la race de David, mais non pour toujours.
Zan ƙasƙantar da zuriyar Dawuda saboda wannan, amma ba har abada ba.’”
40 Salomon voulut donc tuer Jéroboam, qui s’enfuit en Egypte vers Sésac, roi d’Egypte, et fut en Egypte jusqu’à la mort de Salomon.
Solomon ya yi ƙoƙari yă kashe Yerobowam, amma Yerobowam ya tsere zuwa Masar, zuwa wurin sarki Shishak, ya zauna a can sai bayan mutuwar Solomon.
41 Quant au reste des actions de Salomon, à tout ce qu’il a fait, et à sa sagesse, voilà que tout est écrit dans le Livre des actions des jours de Salomon.
Game da sauran ayyukan mulkin Solomon, da dukan abubuwan da ya yi, da hikimar da ya nuna, an rubuta su a littafin tarihin Solomon.
42 Or les jours durant lesquels Salomon régna dans Jérusalem sur tout Israël, furent de quarante ans.
Solomon ya yi mulki a Urushalima, a bisa dukan Isra’ila, shekaru arba’in.
43 Et Salomon dormit avec ses pères, et il fut enseveli dans la cité de David son père, et Roboam son fils régna en sa place.
Sa’an nan ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a birnin Dawuda mahaifinsa. Sai Rehobowam ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.

< 1 Rois 11 >