< 1 Corinthiens 14 >
1 Recherchez avec ardeur la charité; désirez les dons spirituels, et surtout de prophétiser.
Ku dafkaci kauna kuma ku himmatu domin baye bayen ruhaniya, musamman domin kuyi anabci.
2 Car celui qui parle en une langue ne parle pas aux hommes, mais à Dieu, puisque personne ne l’entend; mais par l’Esprit il dit des choses mystérieuses.
Domin wanda yake magana da harshe bada mutane yake magana ba amma da Allah. domin babu mai fahimtarsa saboda yana zancen boyayyun abubuwa ciki Ruhu.
3 Mais celui qui prophétise parle aux hommes pour l’édification, l’exhortation et la consolation.
Amma wanda yake anabci da mutane yake magana domin ya gina su, ya karfafa su, kuma ya ta'azantar dasu.
4 Celui qui parle une langue s’édifie lui-même, tandis que celui qui prophétise édifie l’Eglise de Dieu.
Wanda yake magana da wani harshe, kansa yake ginawa, amma mai yin annabci kuwa, ikilisiya yake ginawa.
5 Je voudrais que vous pussiez tous parler les langues, mais encore plus prophétiser. Car celui qui prophétise est au-dessus de celui qui parle les langues; à moins qu’il n’interprète, afin que l’Eglise en reçoive de l’édification.
To, fatana ace dukan ku kuna magana da harsuna. Amma fiye da hakama, fatana ace kuyi anabci. Wanda yake anabci yafi wanda yake magana da harsuna ( sai dai idan wani ya fassara domin ikilisiya ta ginu).
6 Aussi, mes frères, si je viens à vous parlant les langues, à quoi vous serai-je utile, si je ne joins à mes paroles ou la révélation, ou la science, ou la prophétie, ou la doctrine?
Amma yanzu, 'yan'uwa, in na zo wurin ku ina magana da harsuna, ta yaya zaku karu dani? ba zaya yiwu ba, sai idan nayi maku magana da wahayi, ko sani, ko anabci, ko koyarwa.
7 Les choses qui sont inanimées quoique rendant des sons, comme la flûte et la harpe, si elles ne forment des tons différents, comment saura-t-on ce qu’on joue sur la flûte ou sur la harpe?
Idan kayan kida marasa rai suna fitar da sauti - kamar su sarewa da algaita - kuma basu fitar da amo daban daban, ta yaya wani zaya san irin amon da sarewar da algaitar suke kadawa?
8 Et si la trompette rend un son incertain, qui se préparera au combat?
Domin idan aka busa kaho da sauti marar ma'ana, ta yaya wani zaya san lokacin da ya dace ya shirya zuwa yaki?
9 De même vous, si vous exprimez par la langue des mots qui ne sont pas clairs, comment saura-t-on ce que vous dites? Vous parlerez en l’air.
Haka yake game da ku. Idan kuka furta zance marar ma'ana, ta yaya wani zaya fahimci abinda kukace? zaku yita magana, kuma babu wanda zaya fahimce ku.
10 Il y a, en effet, tant de sortes de langues dans ce monde; et il n’en est aucune qui n’ait des sons intelligibles.
Babu shakka akwai harsuna daban daban a duniya, kuma babu wanda baya da ma'ana.
11 Si donc j’ignore la valeur des mots, je serai barbare pour celui à qui je parle, et celui qui parle, barbare pour moi.
Amma idan ban san ma'anar wani harshe ba, zan zama bare ga mai maganar, kuma mai maganar zaya zama bare a gareni.
12 Ainsi, vous-mêmes puisque vous désirez si ardemment les dons spirituels, faites que pour l’édification de l’Eglise vous en abondiez.
haka yake gare ku. Tun da kuna da dokin bayyanuwar Ruhu, ku himmatu da habaka cikin gina ikilisiya.
13 C’est pourquoi, que celui qui parle une langue demande le don de l’interpréter.
To wanda yake magana da harshe yayi addu'a domin ya iya fassarawa.
14 Car si je prie en une langue, mon esprit prie, mais mon intelligence est sans fruit.
Domin idan nayi addu'a da harshe, ruhuna yayi addu'a, amma fahimtata bata karu ba.
15 Que ferai-je donc? je prierai d’esprit, mais je prierai aussi avec l’intelligence. Je chanterai d’esprit des cantiques, mais je les chanterai aussi avec l’intelligence.
To, me zan yi? Zan yi addu'a da ruhuna, in kuma yi addu'a da fahimtata. Zan yi raira waka da ruhuna, kuma in raira waka da fahimtata.
16 D’ailleurs si tu ne bénis que d’esprit, comment celui qui tient la place du simple peuple répondra-t-il Amen à ta bénédiction, puisqu’il ne sait pas ce que tu dis?
In ba haka ba, idan ka yi yabon Allah da ruhu kawai, ta yaya wanda yake waje zai ce, “Amin” a kan godiyar da kake yi in bai san abin da kake fada ba?
17 Pour toi, tu rends bien grâces, mais l’autre n’est pas édifié.
Babu shakka kayi godiya sosai, amma wanin baya ginu ba.
18 Je rends grâces à mon Dieu de ce que je parle les langues de vous tous.
Nagodewa Allah ina magana da harsuna fiye da ku duka.
19 Mais dans l’Eglise, j’aime mieux dire cinq mots que je comprends, pour en instruire les autres, que dix mille en une langue.
Duk da haka dai a taron ikilisiya na gwammace in yi magana da kalmomi biyar cikin fahimta saboda inganta wadansu fiye da dubu goma da harshe.
20 Mes frères, ne devenez pas enfants par l’intelligence; mais soyez petits enfants en malice, et hommes faits en intelligence.
'Yan'uwa, kada ku zama yara cikin tunani, sai dai a wajen aikin mugunta, ku yi halin jarirai, amma a tunaninku ku girma.
21 Il est écrit dans la loi: Je parlerai à ce peuple en d’autres langues et avec d’autres lèvres; et ainsi ils ne me prêteront même pas l’oreille, dit le Seigneur.
A rubuce yake a shari'a cewa, “zan yi magana da mutanen nan ta wurin mutane masu bakin harsuna, da kuma lebunan baki. Duk da haka kuwa ba za su saurare ni ba”, in ji Ubangiji.
22 C’est pourquoi les langues sont un signe, non pour les fidèles, mais pour les infidèles; au contraire, les prophéties sont, non pour les infidèles, mais pour les fidèles.
Amma harsuna alamu ne, ba ga masu bada gaskiya ba, sai dai ga marasa ba da gaskiya. Annabci kuwa alama ce ga masu ba da gaskiya, amma ba don marasa bangaskiya ba.
23 Si donc une Eglise étant réunie en un seul lieu, tous parlent diverses langues, et qu’il entre des ignorants ou des infidèles, ne diront-ils pas que vous êtes fous?
Saboda haka, in dukan ikilisiya ta taru, kowa kuwa yana magana da wasu harsuna, wadansu na waje da kuma marasa ba da gaskiya suka shigo, ashe, ba sai su ce kun haukace ba ba?
24 Mais si tous prophétisent, et que quelque ignorant, ou quelque infidèle entre, il est convaincu par tous et jugé par tous;
In kuwa kowa yana yin annabci, wani kuma marar ba da gaskiya ko wani daga waje ya shigo, maganar kuwa zata ratsa shi. Za a ma hukanta shi a kan maganar,
25 Les secrets de son cœur sont dévoilés, de sorte que, tombant sur sa face, il adorera Dieu, déclarant que Dieu est vraiment en vous.
asiran zuciyarsa kuma za su tonu. Sakamokon haka, sai ya fadi ya yi wa Allah sujada, zaya furta cewa lallai Allah yana tare da ku.
26 Que faut-il donc, mes frères? Que quand vous vous assemblez, l’un ayant le chant, un autre l’enseignement, un autre la révélation, un autre les langues, un autre l’interprétation, tout se fasse pour l’édification.
Sai me kuma 'yan'uwa? idan kuka tattaru, wani yana da zabura, koyarwa, wahayi, harshe, ko fassara. Kuyi komai domin gina ikilisiya.
27 S’il y en a qui parlent les langues, que deux seulement parlent, ou au plus trois, et tour à tour; et qu’un seul interprète.
Idan wani yayi magana da harshe, bari a sami mutum biyu ko uku a yawansu, kuma kowa yayi daya bayan daya. Sai wani ya fassara abinda aka fada.
28 S’il n’y a point d’interprète, que chacun se taise, et qu’il parle à lui-même et à Dieu.
Amma idan babu wanda zaya fassara, bari dukansu suyi shiru a ikilisiya. Bari kowa yayi wa kansa maganar a gida shi kadai da kuma Allah.
29 Quant aux prophètes, que deux ou trois parlent, et que les autres jugent.
Bari annabawa biyu ko uku suyi magana, bari sauran su saurara tare da bambance abinda ake fada.
30 Que s’il se fait une révélation à un autre de ceux qui sont assis, que le premier se taise.
Idan kuma anba wani fahimta wanda yana zaune a cikin sujadar, bari wanda yake ta magana kafin yanzu yayi shiru.
31 Car vous pouvez tous prophétiser l’un après l’autre, afin que tous apprennent et soient exhortés;
Dukanku kuna iya yin annabci daya bayan daya, domin kowannen ku yayi koyi, a kuma samu karfafawa.
32 Et les esprits des prophètes sont soumis aux prophètes.
Gama ruhohin annabawa suna karkashin annabawa,
33 Car Dieu n’est pas un Dieu de dissension, mais de paix; comme je l’enseigne dans toutes les Eglises des saints.
domin Allah ba Allahn rudu ba ne, na salama ne. Haka yake kuwa a duk ikllisiyoyin masu bangaskiya.
34 Que les femmes se taisent dans les Eglises, car il ne leur est pas permis de parler, mais elles doivent être soumises, comme la loi elle-même le dit.
Mataye suyi shiru a ikilisiyoyi. Domin ba a basu dama ba suyi magana. A maimako, su zama masu sadaukar da kansu, kamar yadda doka ta ce.
35 Si elles veulent s’instruire de quelque chose, qu’elles interrogent leurs maris dans leur maison. Car il est honteux à une femme de parler dans l’Eglise.
Idan akwai abinda suke so su koya, bari su tambayi mazajen su a gida. Domin abin kunya ne mace tayi magana a ikilisiya.
36 Est-ce de vous qu’est sortie la parole de Dieu? Est-ce à vous seuls qu’elle est parvenue?
Daga wurinku maganar Allah ta zo ne? ko kuwa a gare ku kadai ta iso?
37 Si quelqu’un croit être prophète, ou spirituel, qu’il reconnaisse que les choses que je vous écris sont des commandements du Seigneur.
In wani yana zaton shi ma annabi ne, ko kuwa mai ruhaniya, to, sai ya fahimta, abin nan da nake rubuta maku umarni ne daga wurin Ubangiji.
38 Si quelqu’un l’ignore, il sera ignoré.
In kuwa wani ya ki kula da wannan, shi ma kada a kula da shi.
39 C’est pourquoi, mes frères, employez tout votre zèle à prophétiser, et n’empêchez point de parler les langues.
Saboda haka, 'yan'uwa, ku yi marmarin yin annabci sosai, sa'an nan kada ku hana kow yin magana da harsuna.
40 Mais que tout se fasse décemment et avec ordre.
Sai dai a yi komai ta hanyar da ta dace bisa ga tsari.